Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

8

Haka yanufa falon cike da fargabar mai zai faru, samun dad d'in yayi a zaune kan d'aya daga cikin royals d'in da suka sake'kawata falon, gaishe shi Zaid yayi bayan ya zauna, amsawa dad yayi cike da fara'a dan sosai yake ganin nutsuwar yaron.

              Ajiye cup d'in ruwan dake hannunsa yayi, kafun yace... Zaid waton abunda yasa nakira ka. Inason sanin wani abu a game dakai ma"ana inason sanin tarihin ka..... shiru yayi dan jin mai zai ce, Zaid bai Kai ga magana ba Sai ga ummi ta shigo tana rike da hannun baby, dama dad ne yanemi da tazo dan Susan waye Zaid d'in da daga inda yafito.

                 Baby na ganin Zaid"ta kwace hannunta Kai tsaye gunshi ta nufa, cike da d'okin ganin shi. tana zuwa tazauna kan 'kqfarsa tashiga gydal gyadal da kai,, murmushin yake yayi ya sha kanta,, kafun yace sabahul khair... murmushi kawai tayi wanda har ya bayyanar da wushiryar ta.

        Zaid"gaida ummi yayi cikin girma mawa, cike da fara'a ummi ta amsa tana mai jin farinciki a ranta yadda yarta take cikin walwala.

            Zama ummi tayi kusa da dad yazamana dukan su suna fuskantar Zaid d'in. ganin shi suke saurare ne yasa... babu yadda ya'iya yashiga basu labari kamar haka...!

           Kamar yadda naji ana fad'a,, bayan tasowa ta gidan marayu dake nan cikin garin Abuja... Ance wata rana mai gadi ya bude gate da sassafe saboda shige da fice na al'uma shine yayi tozali dani a cikin kwali,,  nan ya fad'awa hukumar gidan,, shine aka d'auko ni aka shigo dani gidan marayu domin aikin su ne dama, nan take aka bude mun file. Aka baiwa d'aya daga cikin masu kula da Yara,, wanda taci gaba da rainona ba tareda nono ba Sai madara danake sha... Inda bayan na shekara uku renona yakoma hannun wata daban.

                     A haka nataso gun  Ammi ,, mace mai kirki mutunci da ha'kuri Sam ammi batada hayaniya ko tashin hankali,, gata da riko da addini wanda ta kasance d'aya daga cikin yan gudun hijirar Iran, bayan ta rasa mijinta da dangin ta shine ta gudo da karamun ciki a inda ta nema aiki da kyar tasamu aikin kula da marayu. lokacin dana koma gun ummi a lokacin tanada jinjirar yarta wacce ta sakawa suna, SEEDIFAH! tunda naga SEEDIFAH, naji ina kaunar ta. na d'auka SEEDIFAH"tamkar kaunwa ta da muka fito ciki d'aya sosai nake nuna mata qauna ta Yaya da qanwa.... Rayuwa a gidan marayu ba kamar ko wace Rayuwa bace,, akwai matu'kar banbanci. Musamman a lokacin da mutum ya girma ya mallaki hankalin kansa ya fahimci cewa Kodai iyqyensa mutuwa sukayi ko kuma bashida su.... hakan na jefamu cikin rudani da tashin hankali. Musamman Irina da ga cikakken tarihin inda aka sameni a yashe wanda yake tabbatar mun da uwata yarda ni tayi,, tun lokacin dana taso na fahimci waye ni,, damuwa ta aure ni,, kullum tunani na ta ina zansamo mana Kyakyawar Rayuwa ni da ammi daku a seedifa?

                 A lokacin dana cika shekaru 19 a duniya a lokacin ne na kammala karatuna na secondary. Inda nafito da kyakyawan sakamako,, nasu matu'ka inci gaba da karatu saidai abun haushin lokacin da gwaunati ta turo dan zakulo daliban gidan marayun dan su dorasu a karatun gaba da secondary.... Sai me"ma'aikatan gidan marayun manya suna suka dinga bada yayansu,, harkar kasata ba wani bincie ake ba, take aka dauki yayansu da wasu daga cikin mu wanda suka ga damar bayarwa a wani dalili nasu na daban.

          Naji matu'kar bakin ciki Kasancewar karatun shine kawai hope d'ina na kashe wanda zai sa nayi tunanin Rayuwa ko babu Kowwa a duniya ta, buri nane inyi karatu wanda zan taimaki musulunci da al'ummar sa harma da wanda ba musulmi ba nad'auka damarar taimakon sa. hakan yasa naje ga shugaban gidan marayun da kokon barata akan ytaimaka min insamu shiga jami'a.  Saida yagama dubana kafun yace Zaid ko? daga kaina nayi cike da fatan Allah ya amsa addu'a ta,, Zaid abunda nakeso kasani shine idan dan jami'a ne wannan ai abune mai sau'ki ne cike da farinciki akan fuskata ina murmushi na dubeshi, saidai da shara di wannan maganar tasa ce tasaka Nad'an gimtse fara'ata,, saidai shiru nayi ina jiran mai zai ce. Fahimtar hakan da yayi ne yasa yace....

Shadin kuwa wani d'an aiki ne zakayi bawai mai wahala bane dn bazai d'auke ka awa4 ba, kawai kaidai ka amince wa duk abunda nace kayi to karatu kuwa daga nan har sin idan kaso zakaje... Cikin fargaba da rashin natsuwar zuciya nace malam amma wani irin aiki ne?

Wani murmushi yayi yace garka damu zaka ga aikin ai tunda dakai za'ayi shi kawai dai yanzun amimcewar ka nake bu'kata.

Zuciya ta tagama rufewa da son karatu kodan nemawa seedifah da ammi Kyakyawar Rayuwa,, Zaid ya fad'a yana share hawayen sa, yaci gaba da cewa....

Shi yasa nakasa ba bance fari da baki na amince da aikin da nakasa samun sukuni akan sa, nidai bu'kata ta karatu ne..murmushi shugaba Alhaji amin yayi dan ganin yasamu nasara, kafun yace shikenan Zaid zaka iya tafiya idan ranar aiwatar da aikin yayi zan nemeka, amsawa nayi da to Ngode baba, dakatar dani yayi ya 'kirgo kud'i kimanin naira dubu biyar yabani girgiza Kai nayi baba ka barshi ni karatun ma da zanyi ya wadatar dani,, bata rai yayi yace.. Inace yanzun ka kirani baba.

Maza kar'bi ni na baka. Zaid"kuma inason maganar da mukayi tazama sirri a tsakaninmu idan wani yaji to karatun ka yasha ruwa, yana gama fad'in haka yamaida tabaraun sa a fuskarsa yaci gaba da duban files d'in dake gabanshi.

Babu yadda na iya haka na karba nai masa godiya.

Ina zuwa na fad'awa ammi ya amince yace zai duba, naboye mata dukkan yadda mukayi dashi wanda a karo na farko dana soma yiwa Ammi wacce nake d'auka a matsayin mahaifiya karya.

tsawon sati d'aya babu aiken shugaba,, ni har nafara cire rai... Wata ranar littini kwatsam nadawo daga rakiyar seedifah"zuwa makaranta ina hanyar dawowa gida na had'u da baba masinja, na office d'in Alhaji Aminu.

Nan yake shaida mun Alhaji yanason ganina yanzun. babu bata lokaci nace yace masa ganinan zuwa,, juyawa yayi yayinda nikuma na nufi bangaren da Ammi take nashaida mata sakon Alhaji Aminu,, farinciki tayi had'i da yimun fatan alkhairee.

Shigana office d'insa naganshi yana shirin fitowa nan nagaishe shi ya amsa cike da fara'a.

Yawa Zaid"  zamu iya tafiya amsa masa nayi had'i da fita waje,, bud'ewa motar sa yayi yashiga yazauna nima ya bude mun yace bismillah! Shiga nayi a sanyaye dan haka kawai nakejin zuciya ta takasa aminta da wannan fitar.

Wata unguwa muka nufa wacce bansan sunanta ba, saidai kallo d'aya zakayi wa unguwar kasan cewa unguwa ce ta manyan mutane, ganin irin 'kerarrun gidajen dake gurin yasa bansan lokacin da nasoma addu"ar arziqi mai albarka ba a cikin zuciya ta wanda a Zahiri kuma sai fitar da ido nake  yi, wani tangamemen gate muka nufa, muna zuwa mai gadi ya bude mana,, parkin Alhaji yayi a parking lot.

Fita yayi had'i da mun alamun infito nima, babu yadda na iya haka nafito ina mamakin ina ne nan mukazo dan naji ana cewa iyalan shugaba suna gwagwalada, makuwa San Nana d'in ba gidan sa bane,,

Saidai kuma babu damar tambaya, haka muka kutsa cikin gidan wani 'kasaitaccen palon naga mun shiga tuni na shaga da kallo dan har mantawa da wata fargaba nayi, shugaba ne yatabo ni nayi firgigit, dariya yayi had'i da fad'in zainab mana malam zaidu!

Zama nayi akan shifidadiyar center rough d'in dake palon.

Wayarsa yajanyo yayi dailing number bansan mai aka ce masa ba naji yace yana zuwa,, wata hanyar naga yabi a raina Nashiga mamakin yadda yakutsa gidan mutane idan da matar aure fa?

Ganin ba abunda ya Shafe ni bane yasa na kawar da zancen a raina, naci gaba da karewa palon kallo, ina jiran tsammani.

Shugaba ne yadawo rike d envelope,, yana washe baki zama yayi a kusa dani yace.... Zaidu"ban amsa ba Sai kallonsa danake, a tausashe yashiga cewa... anan gidan zakayi aiki.. Kanaji na? kuma inason kasani Alhaji ubale bai son raini, anan naji sunan mai gidan.

Kuma duk abunda ya umarceka da kayi kayi domin yi masa gardama daidai yake da faruwar komai a rayuwar ka!wani irin fad'uwa kirjina yayi nasake gwaro idanuwa ina duban shugaba,,gyada kansa yayi alamun tabbatar wa. Kafun yaci gaba da cewa, ina jaddada maka ka Amincewa duk abunda yazo maka dashi, idan dai kayi hakan to tabbas rayuwarka zata haska, duniyar ka zata yi kyau...... Yana gama fad'in haka ya bubbugi ka fad'a ta, had'i da fad'in na barka lafiya, wucewa yayi ya barni tamkar wanda aka dasa,  wani irin tsoro ne yashige ni, a karon farko nafara nadamar son karatu na,, kafun inyi wani tunani ko wani yunkuri wani irin gabjejen katon Alhaji yafito a kofar da shugaba yashiga d'azun, kallo na yayi da jajayen idanuwan sa yana wani lasar baki kamar tsohon maye. zama yayi akan d'aya daga cikin kujerun gurin, dubana yayi yace d'an samari babu gaisuwa? sai a lokacin na tuna da banma gaishe shi ba.

A d'an tsorace nace ina...w..u..ni. 

bazan amsa ba Sai kazo ka zauna... a cewar mutumin, a da rare nazauna akan kujera. Murmushi yayi yatashi d'akin da yafito yanufa had'i da cewa Zaid zo in nuna maka aikin ka ko?

Cike da fargaba nabishi dan ni Sam banyarda da Mutumin ba hakannan nakejin tsoron sa,, shi yasa ma na matsu ingama abunda zai sakani inkama kaina,,

Abun mamaki ina shiga nasameshi ya cire jallabiyar dake jikin shi daga shi sai gajeren wando ya kwanta akan makeken gadon shi.

duba d'aya na masa na d'auke kaina Koda d'an uwana namiji ne haka naji kunyar ganin sa haka ta kamani, zo nan Zaid"

Na tsinkayi muryar sa.... d'ago kaina nayi na dubeshi, Alhaji ina aikin? Inason ingama inkoma gida da wuri ammi na zata jirani.
Ina maganar ne cikin tsoro tsoro,, dariyar yan duniya yayi kafun yace zo ai ga aikin shi zan saka ka,, shiru nayi ban Karasa ma inda yake ba. ganin haka yasa ya tashi zuwa gareni, banyi aune ba naji mutum yana tabani,, ko ba"a fad'amun ba nasan mai yake nufi dani,, (tabbas luwad'i yakeson aika tawa dani)

Bansan lokacin dana tureshi ba ina ko'karin fita saidai babu hanya Dan yazare key d'in,, wani irin kuka na fashe mishi dashi, a cikin kukan Nashiga cewa.... Dan Allah Alhaji kayi ha'kuri kabar ni Intafi ni maraya ne mara gata rayuwata ta dade da gurbata dan Allah garka sake mata wani bakin fentin na rokeka. na 'karasa fad'a da wani irin kuka, saidai da yake shedan yariga da ya ruruta masa ni ya rufe idanuwan sa da karya, da kuma dabbanci,, Sam baiji tausayi na ba saima tausayin kansa na yadda zai wahala kafun yabiya bu'katar sa dani.

Kalaman yaudara yashiga fad'amun da mun al'kawari kala kala. Idan na amince dashi,, saidai ko kadan zuciyata bata Kwad'aita da dukkan al'kawuransa ba. Saima wani tsoron dake sake Shigana,, bayan tunawa da nayi da irin azabar da Allah yatanadar wa masu aikata irin wannan aikin,wani irin kuka nasaka mishi,.nashiga cewa...
Kayi ha'kuri kaji tsoron Allah Alhaji... Ayoyin alqur"ani da dama sun bayyana yadda fushi ubangiji yake akan wannan abun da mai aikata shi ka tsoraci ubangijin ka, domin ya hallice mu ne dan mu bauta mishi badan mu saba mishi ba,, luwad'i yana daga cikin manyan laifuka da Allah yayi hani dasu,, katuba I zuwa ga Allah..... duk wannan maganar danakeyi yi nake ina kuka, saboda tsantsar tausayin kaina da shi kansa Alhajin nakeji,,

Ganin ba Amincewa zanyi cikin ruwan sanyi bane yasa yafice had'i da kulleni,,

Anan yabarni naci kuka har na gode Allah,, gashi ko sallar azahar banyi ba, gashi daga dukkan alamu anyi har isha"i ganin yanayin dadewar da yayi a d'akin,, cike da bakin cikin rashin sallar da baiyi ba yakoma gyara Zaman sa,

*******
A ranar yadda naga rana haka naga dare. Sai da rana ta fito sosai naga an bud'e 'kofa, a hankali nadago idanuwa na da suka'kan'kance, tsabar kuka d damuwa had'i da gajiya.

A hankali Nabi wanda yashigo d'akin da kallo shugaban gidan marayu ne. da sauri na mike tsaye ina dubansa dan ganin yanayin sa, sai naga ya rungume ni had'i da fad'in zaidu"lafiya?

  Da sauri na fashe da kuka had'i da fad'in baba dn Allah ka fitar dani daga gidannan... Kaga zaidu kwantar da hankalin ka,, zo muje, Jana yayi muka fito jikina har rawa yake naga mun fito daga gidan.

Har muka isa gidanmu, babu wanda yasake magana a tsakaninmu. Office d'insa yajani muka shiga har lokacin bana cikin nutsuwa ta, zaunar dani yayi kan d'aya daga cikin kujerun office d'insa, ruwa yabani nasha, kafun yasoma magana.... Zaid"mai yafaru tsakanin ka da Alhaji? a matu'kar rude Nashiga fad'a masa ina mai tsananta kukana.

Ina gama fad'a masa ya dubeni...... yace... Zaidu yi hakuri bansan abunda Alhaji yake nemanka dashi ba kenan, ni cemun yayi aiki zai saka ka... bansan haka abun yake ba ashe Alhaji Mutumin banza ne?

To kasan mai ye? kayi ha'kuri kuma mu bazamu yarda ba a matsayin mu na iyayenku a wannan gidan, Kagane? Ka kwantar da hankalin ka, kuma abunda nakeso dakai wannan maganar yazama sirri a tsakanin mu gar wanda yaji,, kaji ko?

Gyada Kai nayi natafi, Kai tsaye sashenmu na nufa nayi wanka nayi salloli na na kwanta bacci yayi awon gaba dani, sai bayan la'asar nafarka,

Tashi nayi naje nayi sallolin da ake Bina kafun na nufi gurin Ammi.
tana ganina tahau nuna farincikin ta, seedifah, ma tana ganina ta rungume ni tashiga tambaya ta ina natafi na barta,, sai rarrashin ta nayi da kyar kafun ta tafi islamiyya,

Ammi"dubana tayi kafun tace... Zaid Yaya.. Anyi nasara kuwa?

Murmushin ya'ke nayi kafun nace to saidai jiran tsammani saboda wanda naiwa aikin ma baya 'kasar.

A karo na biyu da nayi karya a arayuwa ta.

Addu"ar samun nasara ammi tayimun, kafun muka ci gaba da firar mu, har zuwa lokacin tashin seedifah naje nad'auko ta daga islamiyyar.

(abunda Zaid bai sani ba shine gadar zare ne su Alhaji Aminu sukai masa,,, kudai biyo ni 😂✌️)

Tsawon wata d'aya kenan da faruwar wannan abun wanda Ammi tun tana tambaya ta har tagaji tayi shiru da bakinta,, nikam tuni nafawwala wa Allah komai, nasan idan da rabon inyi karatu to fa zanyi idan babu rabo to duk yadda naso yi bazai yu ba m. Shi yasa kawai nabarwa Allah zabi.

Wata ranar Alhamis wacce ta kasan ce cikin ba'ka'ken ranakun da bana mantawa dasu,

Bayan nabar gun ammi, na nufi dakinmu nida sauran sa'anni na da muke kwana anan,,  katifa ta na hau na kwanta Kasancewar ina matu'kar jin bacci, dan a lokacin 10da rabi na dare ne.

A cikin bacci na naji anyi mun wata irin sha'ka wacce tai matu'kar razanani,,  kafun in bude idanuna naci karo da wani irin Mari da ya d'auke Jina na wucin gadi......

Wani irin kuka Zaid yasaka wanda ya hanashi 'karasa maganar, kuka yakeyi sosai saboda tunowa da wani irin ba'kin'kazafi da yayi.....

Bbu editing dai tom🙄

Xinnee smart 💕✌️😂

Ina ganin comments, ina jin dad'i Kuci gaba hakan yana encouraging nawa💕✌️

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro