Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

7

Sake duban Pic d'in dake jikin yagani tabbas yarinya ce, Inna"lillahi wa'inna ilaihim"raji'un,, yashiga maimaita wa... rasa wani hali yake ciki yayi dan kuwa tsakanin farinciki da bakin ciki ya rasa wanne zai yi,, sai zubawa mujallar ido da yayi,, har abokan tafiyar sa suka zo bai San a wani muhalli zai saka yanayin sa ba, haka yabisu suka tafi.

         Koda suka koma damuwa takasa barin zuciyarsa,, hakika idan zaiwa yarinya adalci to kuwa ya mai data ga iyayenta tunda har address d'insu ansaka,, yasan bazai wahala gun maida ita gida ba. Saidai shi miye makomar shi? Yatashi a mara gata kenan? Wanda bashida wani tsaya yye ko dan uwa da zai duba yaji sanyi,? haka ya dinga saka da warwara,, wattannin su2 a kauyen su baubani,, saidai zakayi mamakin yadda baby tayi baki kamar me. tunda yafara ganinta yaji a jikinsa duk inda tafito to gidan masu dashi ne,, adalci d'aya zaiwa rayuwar ta matu'kar yanason ganin farinciki ya ke waye ta to fa shine ytaimaka mata ya maida ta gida,, Allah bazai barka ba Zaid zai dubeka ko dan Kyakyawar zuciyar ka,, Kaci gaba da tawakkali dashi domin shi d'in abun dogaro ne,, wannan shine abunda zuciyarsa take fad'a mai.

             Yau laraba"kuma a yau ya yanke kan zai sanar da baubani zaije neman danginsu, saidai kuma antashi da baubani cikin. Ciwo mai tsanani wanda har baisan wanda yake kansa ba,,, wannan ne yasa ya ha'kura, aka shiga nemawa baubani magani,, saidai Sam babu sau'ki ganin haka ne yasa yanemi matar baubani kan ko Za akai shi asibiti cikin gari agani,,, dubn sa tayi tace... kayi ha'kuri zaidu amma a gaskiya bazan baka baubani zuwa asibiti ba. Saboda wannan ciwon nasa da kagani,, garin nemar wa kanwar ka magani ne yasame shi,,

         Inna"lillahi wa'inna ilaihim"raji'un"baaah bangane ba,

Labari tashiga bashi.... Baubani yashiga nemar wa kanwar ka magani tun lokacin da ya fahimci asiri ne akai mata,, to makarin asirin ba ta hanyar da baubani yabi yake ba kuma akwai tsarin qarqari a Jikinta ta yadda duk wanda yayi ko'karin nema mata lafiya,, abun zai Shafe shi, dan haka kawai muyi ha'kuri aci gaba da na gida dan ciwon sa ba na asibiti bane,, ta'karasa fad'a idonta na cikowa da kwallah.

            Sosai Zaid yashiga tashin hankalin jin abunda yafaru da dalilin ciwon baubani,, saidai babu yadda ya iya saidai ya zubawa sarautar Allah ido. yau satin baubani da kwanciya cuta asubar fari yace ga garinku nan.

Tashin hankali... Wanda ba'a sa masa rana,, sosai Zaid da matar baubani suka shiga tashin hankali mawuyaci saidai babu yadda suka iya domin basu isa hana Allah ikon sa ba, bayan sati da mutuwar baubani matarsa tasamu Zaid inda take shaida masa zata koma garinsu can gurin yankin bidda kauyensu yake,, godiya sosai Zaid yayi mata na irin taimakon da sukayi musu,, Shima had'a musu kayansu yashiga yi,, yanemi abun Hawa suka wuce garin Abuja bayan sunyi sallama da jama'a,, zuciyoyin kowa babu dad'i tsakanin Zaid da matar baubani suka rabu.

            Bayan sun shiga garin Abuja,, mai mashin ya tambaye shi inda zai sauke su,, nazari yashiga yi,, har daga 'karshe baisan lokacin da ya ambaci unguwar su baby"ba

         Cikin ikon Allah ya fad'a daidai,, mai mashin kuwa yakai su unguwar saidai baisan layin ba dan haka sai Sauka sukayi, nan yashiga tambaya har yadace da kwatwncen da akai masa, duk wannan bulayin da yakeyi baby tana hannun sa. tangamemen gate d'in da aka kwatan ta masa ya duba had'i da sake duban number dake jikin gidan. tabbas gidan ne,, shiru yayi yana nazarin yadda zai shiga,, yayinda baby ta zuba masa idanuwanta.

ganin lokaci sai tafiya yake... dan yanzun gurin karfe 4 yamma ne gashi ko azahar baiyi ba bare la'asar shi yasa ya tattaro sauran karfin zuciyar da yarage masa ya nufi gate d'in gadan gadan.

'kwan'kwsa wa yayi,, mai gadi ne ya le'ko ta yar'karamar 'kofa dan ganin mai buga gidan,, ganin mata shi a tsaye yasa ya bude kofa had'i da tambayar sa malam lafiya? ba tare da ya lura da baby dake hannunsa ba,

Saida Zaid ya had'i yi wani yawu mai daci kafun yace... Nan ne gidan Alhaji Tahir yuguda"? a d'an dage mai gadi yace nan ne, lafiya? dan Allah inason magana dashi ne idan zai yu... Kai a wa zakace xakayi magana da Alhaji,, kaga malam munsan irinku masu zuwa maula a gun Alhaji dan haka to Alhaji na ba fitowa zaiyi ba kaji in fad'a maka gwara ka tattara ka kama gabanka, dubeka......... bai karasa abunda yake son cewa ba yayi saurin yin shiru yana sake duban baby da yagani,, ai kuwa ita d'in ce cike da tsantsar mamaki yace... Baby!.... ai bai tsaya wata wata ba yaruga da gudu cikin gidan yana 'kwalawa hajiya da Alhaji Kira... Inna"lillahi shikenan yau hajiya kukanku ya kare ga baby... ga baby.... Shine abunda yake ta faman zayyana wa har yakai tsakiyar falon gidan wanda Sam basa shigarsa saidai yau tsabar rudu da murna yasa ya afka ba tareda ya lura ba ma. Alhaji dake kishin gide yana duban wani sako da aka turo masa ta waya, bai lura ba kawai yaga mutum a kansa, da sauri yatashi yana dubansa yace... Malam Musa lafiya? cikin haki yashiga nuna masa kofa yana kiran Alhaji tadawo tadawo baby..... Ai da wani mugun sauri dad yatashi yana duban, malam Musa yace ka tabbata? da sauri mai gadi yafita dan zuwa ya tabbatar masa Shima Alhaji Tahir d'in bin bayansa yayi yana addu'ar Allah yasa da gaske ne,, duk wannan budirin da ake ummi tana d'aki tana bacci saboda magun gunan da aka bata akwai na bacci a ciki, dan a cewar likita kwakwalwarta zata iya samun matsala, idan bata samun ishashen bacci.
dan haka batasan abunda ke faruwa ba Kasancewar tasha maganinta bacci yayi gaba da ita.

Har rige rugen bude kofa ake tsakanin Alhaji da malam Musa mai gadi, sauran masu aikin gidan ma da basusan maike faruwa ba tasowa sukayi dan ganin ko lafiya,

Zaid yana tsaye da baby wacce ya riketa gam,, dan baisan ya shaku da yarinyar ba Sai yau da yake shirin mikata ga a halinta, saidai yanaji a jikinsa wannan aikin alkhairee ne zai aiwatar yasani Allah zai bashi ladar sadar da ya ga iyayenta. Shi yasa ko kadan baiyi nadamar kawota ba.

Alhaji Tahir"nayin tozali da yarsa yashiga hailala, tuni ya rungumeta yana mai jin wani irin farinciki da Allah yasake hadashi da yarsa d'aya tilo a tunaninsa, dan baisan yana kaunar baby har haka ba, saida aka nemeta aka rasa. Sosai ya 'kan'kame baby a jikinsa,, Zaid" ganin yayi abunda yadace kawai sai ya juya zai wuce... babu wanda ya lura dashi har yasoma tafiya wata irin'kwalla mai d'umi tasaukar mishi... Baby ce kawai talura dashi dad na shirin shigewa da ita gida ta sakar masa wani irin cizo a ka fad'a wanda babu shiri yasauke ta.

Da saurinta cikin bingil bingil, d'inta ta isa gareshi ba tare da yasan ta biyo shi ba, sai jin yayi an rungumeshi,, ta baya wanda Koda bai juyo ba yasan wacece,, a hankali ya juyo ya Kalle ta yaga sai rabon ido take ga wani irin hawaye dake zuba akan Fuskarta. Wanda yake nuna masa alamun gar yatafi yabarta,, rusunawa yayi ya rage tsawon sa, hawayen yashiga goge mata.

Cikin muryar sa mai cike da damuwa yace... Yarinya"mai kike wa kuka? ai yanzun kuma kindaina kuka saidai farinciki ko... ya karasa fad'a da murmushin yake, yaci gaba da cewa... Kuka ba irin naki bane na Yar gata bakiga dadyn ki yadda yayi farincikin dawowar ki ba? Ke Yar gata ce,, nasan bazaki bani amsa ba... Amma Kisani zan rayu dake a zuciya ta ke d'in wata abace mai mahimmanci a zuciyar Zaid yarinya ta bazan manta ki ba kinji ko? Kema ki dinga tunawa dani kinji?

   yanzun kitafi gida nasan ummanki tana dokin ganinki,, zakiyi rayuwar ki mai yanci cikin farinciki... tashi yake ko'karin yi, ta rike masa ka fad'a,, girgiza Kai tashiga yi,, tana sake bulbulo da hawaye,, gyada kanta tayi alamun nuna shi, sannan tadawo da kanta izuwa nuni da kanta,, daga bisani ta rungume shi, tasaki wani irin kuka,, wanda tunda take duniya bata ta'ba yin kuka mai sauti ba bayan ihu da take idan ciwon ta ya tashi.

Shima runtse idonsa yayi duk yadda yaso gar yayi kuka saida yasaki kuka mai ciwo,, idan yace bai sha'ku da baby ba yayi karya saidai ya zaiyi? 'kaddararsa ce wata iri kullum bata zuwa a daidai sai dai a gicciye. Dole kuma ya karbeta a yadda tazo masa... baiyi aune ba yaji an d'an bubbuga kafadarsa,, bude rinannun idanuwansa yayi dad d'in baby yagani fuskar sa cike da tausaya wa, yace... bawan Allah dan Allah taso mu 'karasa daga ciki kaga nan waje ne kuma mutane na kallo, tashi Zaid yayi dan yakasa yiwa dattijon musu kodan  'kwarjinin sa.

Bayan sun shiga ciki ne, Abba yasa uwani takawo musu abinci, shi kuma yashiga part d'in ummi,, samu yayi har lokacin tana baccin, girgiza kai yayi cikin murmushi.. a Zahiri yace kukan ki yazo karshe lubabatu ga baby tadawo gare mu.

juyawa yayi zai fita,, yaji tana salati alamun ta farka daga baccin kenan,, juya wa yayi dan dubanta itanma shi ta duba tana mai cewa.. Alhaji kanason wani abu ne? Murmushi yayi irin wanda yadad'e baiyi ba.

Kallonsa take da mamaki dan ta dade bataga fara'a akan fuskar sa ba. cike da mamakin abunda yasaka shi wannan fara'ar tace lafiya...?

hannun ta yakama yamikar da ita tsaye had'i da gyara mata d'an kwalin dog uwar rigar dake Jikinta, ta yadda ya zauna da kyau. fita yayi da ita hannun sa yana cikin nata, Kai tsaye falon sa yanufa da ita itakam banda fad'uwa babu abunda gabanta yakeyi saidai takasa furta masa Koda Kalma d'aya da zummar tambayar sa,, da zata iya tabbas da sai taji lafiya mai yasa yake Jan hannunta zuwa falon sa,, saidai kuma babu baki Sai kunni.
Cak! ta tsaya saboda tozali da tayi da gudan jinin ta. cikin wani irin taku tamkar ana ingiza ta,, ta isa gareta wata iriyar runguma tayi mata had'i da sake wani irin kukan farinciki,
Lumm! baby tayi a jikin mahaifiyar ta sai faman sauke ajiyar zuciya take, saida ummi tayi kukan ta ma'ishi kafun ta saki yarta sujoodu shukur tayi tane sake jaddada godiyar ta ga Allah nad'aukakin sarki, saida ta nutsu kafun ta lura da Zaid"dake zaune ya zuba musu ido a ransa yanajin inama... Inama.... Saidai babu wannan damar.yanajin a ransa ko babu komai ita dai tasamu farinciki shikam yagama cire rai da wani sauran farinciki ko walwala a rayuwar sa.

Wannan fa Alhaji? Ummi ta tambayi dad da sai faman waya yake yana sanar da bayyanar baby.

Murmushi yayi yace,, sunan sa Zaid shine wanda yakawo mana baby har gida.
Allah sarki"ummi ta fad'a tana nuna tsantsar kulawarta ga Zaid d'in

Zaid"cike da ladabi y agaida ummi itama da fara'arta ta amsa masa, nan dad yasa aka Kai Zaid d'aya daga cikin dakunan gidan domin yayi wanka ya huta. haka kuwa akayi,,



* **
Kafun kace me, dangi ya d'auka Anga baby Anga baby. take kowa yashiga farinciki da murnar ganinta da akayi,, haka aka dinga zuwa barka da arziqi.

Yau"Zaid yanada kwana hud'u a gidansu baby,, kuma a yau ne dad ya aika domin a Kira masa shi suyi magana,, wanda 'kirjin Zaid har wani irin rawar duka yakeyi, tsabar fargaba.

Sowwy bbu editing ba😥

Dn Allah kuyi manage, wlh mura ta tasani a gaba gashi labarin yanada tsawo 🤧so I hope u guy's will be with me cox is a long journey. ✌️


Xinnee smart ✌️😁💕💋

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro