Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

6

Inna"lillahi wa'inna ilaihim"raji'un yashiga mamaita wa, cike da tsantsar damuwa, Lallai 'karshen Zamana a gidannan yazo saboda bazan iya barin yar mutane ta tafi ba,
domin ita d'in wata irin'kaddara ce da Allah ya had'a shi da ita Lallai yana bu'katar taimaka mata da dukkan zuciyarsa hara ma da 'kwanji. duban ta yayi yaga yadda take ta baccin ta hankali kwance, wani irin mugun tausayin ta ne yasake kama shi a karo na ba adadi. ganin bashida wata mafita data wuce ta addu'a ne yafita yaje ya d'auro alwala,, nafil'fili yashiga yi inda duk karshen karatun raka'a yake rufewa da suratul ikhlas"domin ita d'in sura ce ta iklasi da tawassuli. Saida yayi raka'a 12,kafun ya rufe da shafa"i da wutiri, sosai yayi ta zuba addu'ar neman mafita da daukin Allah (SWT) cike da tsantsar tawassuli.

Bayan ya kammallah addu'a ne ya duba agogo dan ganin 'karfe nawa 4:55 yagani sosai yayi mamakin yau ciwon ta bai tashi ba. dubanta yayi na yan seconds kafun yatashi yakawo raka'atanil fajr.

    masallaci yanufa inda ya gabatar da sallar asuba cikin jam'iyana dawowa daga masallaci Kai tsaye cikin gida yashiga d'akin umma yanufa, samun ta yayi tana lazumi da alama sallah ta idar, zama yayi daga gefe gaisheta yayi, saidai ko kallonsa batayi ba bare yasaka ran zata amsa shi, ganin hakan yasa yashiga cewa... Umma dan Allah duk abunda nai muku ku gafarce ni... hakika kun taimake ni kun tallafeni a lokacin danake bu'katar hakan.
babu abunda zance sai Allah yasaka da alkhairee. idan auwal yadawo dan Allah ami'ka sa'kon godiya ta a gareshi, Allah ya had'a fuskokin mu da alkhairee. Ya karasa fad'a a raunane.

Ficewa yayi yana ko'karin karfafa kansa.

Umma da tunda yafara magana ko ci kanka batace mishi ba saida ya fice tabi bayansa da kallo had'i da fad'in ai shikenan mun rabu da 'kaya.

Kai tsaye d'akin yakoma har yanzun tana kwance saidai kuma ba bacci take ba, saima rarraba idanuwa da takeyi tamkar mai neman wani abun.
tana ganin shi tamike da saurin ta nufeshi fad'awa tayi jikinshi tana sauke ajiyar zuciya, wanda har yana jin sautin sa,

du'kawa yayi, yari'ke hannuwanta yashiga magana.... Yarinya"kinga halin da muka tsinci kanmu duk mu biyun ko? taki kaddarar ta rabaki da iyayenki ta had'aki da ni. Yayinda tawa 'kaddarar... Iyayena suka jefar dani nataso a gidan marayu nayi Rayuwa a can kaddara ta fitar dani ta had'ani da auwal, yayinda kaddarar ta sake had'ani dake, gashi ta rabani da auwal... Kuma takeso muyi tafiya gu d'aya, wasu irin hawaye ne suka ci gaba da Sauka a idanunsa, yaci gaba da cewa.... nayi imani da dukkan ta alkhairee ko ta sharri ... Saidai ina ro'kon Allah yasa a wannan tafiyar tamu yasa kaddarar tabarmu tare garta rabamu, dan a yanzun ke ce nake gani a matsayin dangina
,

ke ce komai na, kuma nayi d'amarar zama tare dake duk abunda zanyi a Rayuwa ta kece a gefena.
Kisani duk da bakida baki zan had'a wannan alkawarin a tsakaninmu komai rintsi zamu zama dangin junan mu. hannun sa ya d'ora a kanta yayinda ita kuwa sai kallon sa take yana d'ora hannun sa, ita ma ta d'ora duk da bawai ta fahimci mai yake nufi bane a a. Kawai dai a yan kwanakin duk abunda taga yayi to tana ko'karin yi,
            
                 Shafa kanta yayi yayinda hawaye suka cigaba da gudana akan Kyakyawar fuskarsa, ci gaba da magana yayi.... yarinya inasonki irin son da Yaya yake wa kanwarsa, Fatana Allah yabani ikon rike amanar ki. kanta na bingil bingil... tashiga share masa hawaye cikin damuwa duk da batasan matsalar sa ba amma hakan sai taji itanma bata jin dad'in yanayinsa,, hakan da tayi yasa yasake jin wata irin kaunar ta, take ya rungumeta yana sakin wani irin kukan tausayin kansu... saida yayi kukan ma'ishi, ganin rana yana dad'a yi ne yasa ya had'a kayansa cikin Yr jakar Ghana most go d'insa, hannunta ya rike suka fito zuciyarsa a matu'kar cin kushe.

                        Mashin d'insa yasoma ko'karin tayar wa,, kawai yaji surutun mutane, wai gawa yayi dan ganin suwaye haka,, idonsa ne ya Sauka kan matasan garin,, aikuwa shi suka durfafa, wani irin bugawa 'kirjinsa yayi, kafun yayi wani yun'kuri yaji ankai masa sha'ka.

                babale mai shagon aski ne".....kau!yaji saukar Marin da bai shirya wa ba, wata irin Kara yasaka duk abu nan da ake hannun baby na cikin nasa.

                   Da kyar yasamu damar magana... Saminu lafiya? mai nayi muku? bai rufe baki ba babale yasake balle shi da Mari, kafun yace... Dan Ubanka ma waton tambaya kake,, Koda dai babu uban,, dama ai tsintacciyar mage, dan uwarka wannan yarinyar... 'kanwar uwarka ce?
           Ashe dama satar yayan mutane kake?

Wani irin zaro ido waje yayi yace sata? Wace irin sata kuma?

                Yar uwata ce fa...'kanwata ce... Shehulle mai rake ne yakai masa wata muguwar ham'bara a gefen wuyansa wanda ya tilasta masa du'kewa.. had'i da sakin wata razananniyar 'Kara.

                 dukansa suka hau yi kota ina,, tamkar Allah ya aiko su, shi kuwa tun yana motsi har yadaina. jama'ar dake gurin ganin baya motsi yasa suka barshi saidai sun yanke shawarar 'ko nashi zasuyi, anje akawo fetir da ashana yayinda wasu suka tsorata suka gudu wasu kuma suka tsaya daga gefe suna jiran a aiwatar da hukunci a kansa a cewarsu hakan shi yadace da Mutane irinsa. baby wani irin ihu tasaka wanda ya tilasta wa sauran jama'ar gurin razana,, take tashiga buga kanta a 'kasa bakinta naci gaba da fitar da mummunan ihu mara dad'in saurare,, babu shiri mutanen gurin suka watse, mata dake le'ke da daga katanga suka San inda dare yayi musu domin sosai yanayin ta yazama abun tsoro, masu kawo fetir da ashana sunayin arba da ita suka San inda dare ya musu..

           Zaid"kansa karar ihun baby ne yafarkar dashi daga Suman wahalar da yayi,, ganin babu kowa a gun sai shi da ita ne yasa,, a hankali yashiga tofeta da addu'a cikin 'karfun hali.  take tasoma dawowa nutsuwarta ganin idan dai aka fahimci komai ya lafa to Za a iya dawowa ne yasa ya kokarta yatashi cike da karfun hali,, yanufe ta janta yashiga yi yayinda batayi musu ba tabishi,, suka soma tafiya... Cikin'karfun hali yake takawa,, a ransa yanaji cewa dole ya rayu kodan baby,  

            Cikin ikon Allah har suka samu suka isa wani d'an karamun kauyen gwarawa,, a lokacin baby kanta kiris take jira ta zube tsabar wahala da gajiya gashi gishinta sai zugi yake mata,,

                         Suna isa kofar wani gida ya zube a gurin take itama baby ta sume a jikinsa,, baubani shine mai gidan da suka zube a kofar gidansa yadawo daga kasuwa zaiyi shiga gida yaga mutane a zube,, take hankalinta yatashi,, saidai da yake gwarawa akwai asiri bai wani razana ba saima dubawa da yayi yagane suma ne sukayi nan ya cicibi baby yashiga da ita gida,, yadawo ya taimaka wa Zaid Shima yashigar dashi gidan,, matarsa tana ganinsu tashiga tambayar inda yafito da mutane haka bayanin yadda yagansu yayi mata,,

Nan yashiga ko'karin farfad'o dasu matarsa tana tayashi da taimaka wa baby shi kuma yana kan Zaid yana fama,, cikin ikon Allah gurin asuba suka farfad'o kusan lokaci d'aya.

            Da salati Zaid"yafarka,, kansa na masa wani irin nauyi,, lalube yasoma yi, baubani ya fahimci baby yake nema nan yashiga yi masa magana da hausar sa ta gwarawa, kwantar da hankalin ka, ka nutsu ga wacce kake nema nan a kusa da kai,, Kai dubansa yayi inda yake nuna masa baby,, aikuwa ganinta yayi itama sai wuri wuri takeyi da ido,, tana ganinshi ta tashi bingil bingil,, taje kusa dashi ta lafe tamkar wani zai gudu da ita. Murmushi baubani yayi,, a ransa yana jinjina wa wanda ya asirance yarinyar,, dan gani d'aya yayimata ya fahimci akwai asiri a Jikinta, hakannan yaji yanason taimaka musu,,

          Kashe gari yake fad'awa Zaid yadda ya samesu a kofar gidansa,, nan Zaid ma ya kwashe labarin sa inda ya fad'a masa baby kanwarsa ce hatsari sukayi motar su ta'kone da iyayen su,, sun rasa inda zasu shine suka wuto wannan hanyar,, har suka sume a kofar gidansa,, sosai ya tausaya musu, yace su xauna dashi har su warke inyaso sai suje neman dangin su,, nan Zaid yayi masa godiya sosai matarsa ma ta tausaya musu sosai. Nan suka nemi jin sunayensu nan ya fad'a musu sunanshi Zaid ita kuma sunan kakarsu ce da ita suna ce mata yarinya.

                 ********
Rayuwar Zaid"da baby a kauyen milhim, Rayuwa ce ta babu yabo babu fallasa Kasancewar mutanen gurin sunsha bamban da wanda dukkan ninsu suka saba gani haka dabi'unsu Sam ba iri d'aya bane,,

     Bayan Zaid yasamu sau'ki yashiga bin baubani gona, suke noman doya, da sauran kayan amfani baubani dama daga shi sai matarsa ta rasulu,, har sun manyan ta amma basu samu, haihuwa ba. Suna Zaman lafiya da kowa a garin kasancewar su mutane ne masu kirki.

Matsalar baby kuwa"sun sanda shi, dan har baubani ya tambayi Zaid akan hakan inda ya tabbatar masa da lalurar aka haifeta, wanda Shima haka ya tsinci kansa da fad'a, nan baubani ya sanar dashi kan zasuyi bakin ko'karin su gun samun warakarta. Zaid babu yadda ya iya dan kuwa kawai amin cewa yayi amma a ransa yanajin bazai bari asamarwa baby da lafiya ta hanyar da bai dace ba domin kuwa,, su baubani suna tsafi kuma ya fahimci haka, tabbas zaiso yarinya tasamu lafiya saidai kuma bata hanyar kaucewa manzo (SAW) ba.

           ****
Yau ne suka gama Lofa buhuhunan doyar su,, inda Za a fita dasu cikin garin Abuja,, domin saidawa haka kuma baubani ya wakilta Zaid da yabi sauran wanda zasuje domin saida doyar. Saboda shi baya jin dad'i. babu Zaid ya iya domin kuwa bayason zuwa garin Abuja saidai kuma bazai iya yiwa baubani musu ba saboda tarin hallacin sa a garesu,,

          Kafun yatafi saida ya tabbatar da yarinya tayi bacci,, kafun yafice domin idonta biyu bazata bari yafita ba,, dan gona ma da yake zuwa tare suke tafiya.

Sun isa garin Abuja lafiya akayi cinikin doya Zaid ya siyar da nashi nan ya jira sauran abokan tafiyar sa domin su koma,,gurin wani mai shagon saida littafai yanufa ya zauna bayan ya sanar da abokan tafiyar tasa

          ganin shagon littafan harda jaridu suke saidawa ne yasa,, yace Abashi guda d'aya saboda kwana biyu yayi kewar karatu duk da burinsa ne karatun, amma yanzun burin nasa yana kan yarinya still dai dole yanema kud'i kodan yasama mata Kyakyawar Rayuwa, shi yasa ma Sam ba yajin wahalar da yake kwasa a gona musamman idan ya tuna dan wacce yakeyi, yakan sake samun karfin zuciyar yin aiki tukuru bisa gaskiya da Amana.

Mai shagon ne yakatse masa tunanin sa ta hanyar mi'ka mishi, mujallar... Kud'insa ya bashi bayan ya tambaye shi nawa ne,,

Har ya ajiye akan har yaje gida sai ya karanta, saidai zuciyarsa ce ke azalzalar sa akan ya karanta yadan ji mai duniya take ciki. Headline d'in yasoma bi....... Wani irin bugawa kirjin sa yayi take zuciyarsa tashiga rawa,, wani irin gumin tashin hankali ne yashiga tsatsatsafo mishi.....




Xinnee smart ✌️💞😘😂

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro