Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

34


Gaisuwa da fatan alkhairee 🙏Aunty jamila yakasa😘Fateema Radda💋Haleelos💕Maikokona 😍mum Munawwara 💞maman Yara 😍mum Afra💖Mamn Sulaiman 💝mum zaheen💕baby bint oriflame 💞binta Umar 😍ta sidi🙏kankanaty Mrs yusuf mamn sajjad ta Annabi ummu haidar, Summy wakeeli 🙌😘gaskiya Kuna da yawa d sauran wanda ba fad'i ba ina muku ftn alkhairee Allah y raya zuri'a ysa albarka 🙌💕💋

ASALIN ALHAJI FAROUQ... Mutumin kano ne a karamar hukumar gwarzo mahaifin sa Alhaji Zubairu dalha" d'an kasuwa ne wanda Allah yayi masa nasibi a harkar kasuwan cin sa.

Yana da mata d'aya sai d'an su kwara d'aya wanda saida suka shekara goma kafun suka samu haihuwar sa, Alhaji Zubairu yana da yan uwa na dangi saidai yar uwar sa da suka fito ciki d'aya kwaya d'aya ce ita ma uban ta daban bayan mahaifiyar sa ta haifi suwaiba" ta rabu da mahaifin ta shine ta auri mahaifin zubairu,

      Iyayen su kuma du sun rasu, saidai yana matu'kar kaunar Yar uwarsa suwaiba kodan ita kad'ai ce dashi, a lokacin tayi aure itama a cikin garin kano Shima ya Gina gida a garin kano ya tare da matar sa.

Bayan shekaru goma Allah ya bashi haihuwar farouq, sosai yake nuna wa d'an sa gata dan ko makaranta ta yayan masu kud'i yasa shi, Allah yayi Alhaji zubairu, mutum mai tausayi da taimako, wannan yasa ya kasance mutum mai yawan ziyartar gidan marayu gajiyayyu da kuma asibitoci makabarta da gidan kaso.

A duk lokacin da yakai ziyara a irin guraren yana matu'kar jin imanin sa yana sake karfafa, haka kuma duk lokacin da yaje yakan bayar da taimakon kayan abinci kudade da sauran abubuwan bukata, wani lokacin ma ko baije ba idan suna neman taimako sukan same shi da zancen baya ku tsayawa zai bayar da abunda ake nema wannan yasa Yawanci gidan marayu da kungiyoyi na ma bu'katar suka San shi sosai.

Wannan yana daga cikin sirrin habbakar kasuwan cin sa.

Tun farouq yana kankani yake zuwa dashi duk ziyarar da zai Kai a d'aya daga guraren.

Wani lokacin idan yaga abun tausayi, sai ya dinga hawaye yana Godewa ubangiji, a lokacin farouq yakan ce Abba" an Duke ka ne?  Alhaji zubairu baya bashi amsa saidai ya shafi kansa.

Farooq yana shekarar karshe a secondary school. Wata rana mahaifin sa yace ya shirya dan suje gidan marayu kamar yadda suka saba a duk ranar jumma'a.

Hakan kuwa akayi sun shirya suka tafi kafun sallar jumma'a, dan hakan sukan yi ko idan sun gama daga can su tafi masallacin ko kuma bayan sunyi sallah sai su nufa can.

Yau dai kafun sallah suka tafi.

Suna office d'in shugaban gidan marayun, inda Alhaji zubair yake jin korafin abubuwan da suke bu'kata.

Sai ga d'aya daga cikin masu hidima da gidan marayun ya kwankwasa kofa had'i da shigowa, d'auke da kwali wanda kafun a fad'a maka abunda yake ciki zaka fahimta da kanka.

Saboda kukan jinjirin dake fitowa daga kwalin.

gaisawa sukayi da alhajin had'i da maida duban sa ga shugaban gidan.

"barka dai yallabai.

Barka malam Audu,

Yallabai kamar yadda kake ji wannan jinjira ce aka samu a gunwar da nake shine na d'auko ta zuwa nan gidan.

Ya fad'a yana mai sake duban kwalin.

Ajiyar zuciya shugaban ya sauke yace, mallam Audu, baka sanar da hukuma ba kuma ba kuyi bincike ba? ko a cikin unguwar ce wata tayi aika aikar?

Yallabai" kaima kasan yana da wahala a gano wannan al'amari.

Hmmmmm shikenan miko mun shugaban ya fad'a yana Mika hannu.

Ciro ta mallam Audu yayi daga kwalin abun mamaki a shirye take tsab cikin kayan sanyin ta, tasha hula da safa.

ta gaji da kuka ta saka yatsar ta a baki Sai tsutsa take.

Ka kira mun d'aya daga cikin matan.

to yallabai.

Wasu takardu ya d'auko, daga bisani kuma ya kalla Alhaji zubair yace... Alhaji ka gani ko? Kullum cikin karbar jinjirai muke, gashi yanzun sai a hnkali bama samun wani tallafi sosai saidai daga wajen irinku wanda baku da yawa, Alhmdllh!

Numfashi Alhaji zubair" ya sauke kafun yace, Allah ya kyauta, dan sosai abun ya taba shi wai mai mutane suka koma ne? Idan cikin shege ne ga alhakin zina ga na cutar da d'an dan sai an tambaye ki akan yarda shi da kika yi. Ina kika San zai tsinci kansa?wace tarbiyya zai taso a cikin ta?

Lumshe idanuwan sa yayi kafun ya mika hannu sa ya karba babyn.

Idonsa ya zuba mata, itakam sai bacci take abunta tanayi tana sauke Ajiyar zuciya.

Farooq ma ido ya zuba mata, kafun Alhaji zubair ya tsinci muryar sa yana cewa, Abba mu tafi da ita dan Allah yana fad'ar hakan hawaye na sauko masa.

Kallon shugaban Alhaji yayi yace, zamu iya d'auka?

Mai zai hana Alhaji.. Wasu ma suka zo muka basu bare kuma Kai.

Yanzun nan ma kuwa, wani form ya bashi ya ciccika, sukayi musayan copy, aka kira mai hoto yayi ma yarinya hoto na babban copy da kuma passport.

Suka rike copy Alhaji ya rike nasa.

********

Koda suka koma gida bayani yayi wa matar sa ubaida, itama cikin tausayi ta karbi yarinya tana kallon ta cike da tausayawa, yace wani suna zamu saka mata?

tace Jamila!

take yayi mata khuduba da Jamila.

Jamila ta taso a hannun marikan ta Yar gata saboda irin soyayyar da suke nuna mata tamkar su suka haife ta.

dan ko girma batayi ba Alhaji ya sauya unguwa, haka kuma yasaki gargad'i mai zafi akan Jamila a cikin dangin sa da abokan mu"amalar sa.

kasancewar sa mai arziki yasa kowa yaja bakin sa yayi shiru saima kauna da kulawa da ake nuna wa jamilar.

Jamila tana da shekaru shida a duniya Allah yayi wa hajiya ubaida rasuwa sosai mutuwar ta girgiza Alhaji farouq da ka war sa Jamila, uwata uba mahaifin su, wanda kasa jurewa yayi ya kwanta jinya.

Yau ciwo gobe lafiya haka zubair ya kasance, a bayan mutuwar ubaida ne yayar sa suwaiba ta dawo gidan sa da zama kasancewar nata mijin ma ya rasu  ita taci gaba da kulawa da su farouq, a lokacin farouq ya gama karatun sa na jami'a yana aiki a company d'in mahaifin sa.

Wata rana suka tashi da wani irin alhini na rasuwar Alhaji zubair, sosai suka shiga damuwar rashin iyayen nasu duka biyu.

Sai daga baya suka dangana.

A lokacin hajiya suwaiba" tasoma yiwa farouq zancen aure, saidai kawai yace mata akwai lokaci, wata rana,

Wata yarinyar fulani tazo gidan neman taimako ko da na aikatau ne, akayi sa'a kuwa hajiya suwaiba ta d'auke ta.

tunda farouq ya Sanya idanun sa akan Rukayya" yar fulani yaji ta kwanta masa a rai.

Wata rana yasa ta kai masa shayi parlourn sa.

Anan ya nemi jin tarihin ta,

Bata San mai yasa ya tambaya ba saidai ta tsinci kanta da son fad'a masa.

bashi labarin ta tayi, asalin ta yar kauyen rugar mai damma ce. (idan baku manta ba dad ma daga can yake, dan haka sun fito ne daga ruga d'aya) iyayen ta Allah yayi musu rasuwa ta taso ne a hannun baffan ta, wanda ya kasance Kani a gurin mahaifin ta.

Saidai Sam bata jin dad'in zama a gun sa saboda bakin halin matar sa, ko kad'an batajin dad'in zama dasu, daga karshe matar ta zuga baffan ta kan zasu aurar da ita ga ardon garin, wannan yasa ta gudu ta biyo akori kura zuwa garin kano shine har Allah ya kawo ta gidan neman taimako.

Jinjina kansa yayi bayan yaji labarin ta.

Tun daga ranar yashiga bayyana mata sirrin dake ransa, saidai ta kan ce itakam yafi karfin ta.

Allah ya had'a jinin Rukayya" da Jamila duk da tazarar shekarun dake tsakanin su, kasancewar a lokacin Rukayya" zata Kai shekaru 18 Jamila kuwa tana da shekaru 10 a lokacin, yayin da Yar karamar Yar hajiya suwaiba waton Azumi" take da shekaru 14.

Sosai hajiya suwaiba take shirin ta na aurawa farouq azumi, wanda shi baima San tana yi ba.

Wata rana ya same ta da zancen son auren Rukayya da yake, take ranta ya baci, ta soma yi masa fad'a,

Dan rashin hankali irin naka ga yar uwar ka, inata maka tanadi kuyi auren ku na zumunci hankali na ya kwanta shine zaka jajibo wa kanka auren tsintaccinyar mage? Yarinyar da baka San asalin ta ba?

To ka kiyayeni,

Shidai tunda tasoma magana baice da ita komai ba shikam Allah yasan bazai iya auren azumi ba dan kallon kanwar sa yake mata kuma ma ai tayi masa kankan ta.

Ganin farouq bashi da niyyar yarda da abunda take so ne yasawaqa ta du'kufa gun muzguna wa Rukayya" dan har koranta tayi farouq yace wlh dole sai ta zauna a gidan dan gida gidan sa ne, babu yadda suwaiba ta iya, ta kyale shi.

Haka ta shiga bin malamai yan bori duk dan neman asirin da zata farakka farouq da Rukayya haka kuma ya amince da duk abunda tazo masa dashi, saidai komai yana faruwa ne da izinin Allah nad'aukakin sarki.

Dan haka Allah bai nufa ko d'aya daga ciki ba, wannan yasa ta koma kan Jamila" tayi nasarar juyar da hankalin ta, haka kuma suka shiga amfani da ita, rana d'aya ta tashi da matsa nan ciyar kiyayyar Rukayya" komai tayi hantarar ta takeyi.

Rukayya bata taba nuna Bacin ranta akan abunda suke mata ba,

Jamila sosai ta sawa farouq rigima akan Lallai saidai ya auri azumi, wanda daga karshe har marinta yayi wanda bai taba Koda nuna ta da yatsa ba.

da yaga abunda ake wa Rukayya" a gidan, ya tafi gwarzo gun yan uwa ya fad'a musu yasamu matar aure aka je ruggar su Rukayya" inda da kyar baffan ta ya amince ya ba farouq" auren ta, nan aka d'aura aure.

Yana dawowa gida ya tattara ta suka nufi sabon gidan sa da ya gina ya zuba komai a ciki babu abunda bai sa ba.

Wannan abun yayi wa hajiya suwaiba da yayan ta ciwo. kasancewar sun iya munafurci ne yasa suka bashi ha'kuri, aka ci gaba da mutunci wanda a bayan idon sa Sam Rukayya"bata jin dad'in su dn babu abunda take fuskanta sai tsangwama da hantara, hka kuma bata taba fad'awa farouq ba.

Tana matu'kar ha'kuri da su.

Saida ta shekara biyar babu haihuwa, wannan yasa hajiya suwaiba sake fuskantar farouq da zancen karin aure, wanda a wannan karon ma bai amince ba.

Hakan yasake jefa tsanar Rukayya a zuciyar suwaiba da alhalin ta.

Shekarar Jamila 17 a duniya, ta samu miji farouq shine wanda ya aurar da ita da komai na yayan gata.

Mijin nata yana da rufin asiri daidai gwargwado, saidai ko kama kafar farouq baiyi a arziki ba.

Wannan yasa suwaiba suka sake samun damar sake zagin farouq d'in tare da bata shi a gun Jamila, suna nuna mata ai matu'kar ta bari Rukayya" ta haihu to dukiyar iyayen su babu abunda zata tsira dashi bayan kuma suwaiba ta San cewa Jamila bata da gadon iyayen farouq.

Auren Jamila da shekara d'aya Allah yabaiwa Rukayya ciki. tunda wannan cikin ya bayyana ta sake shiga tasku da irin tsangwamar da suke nuna mata, asiri kuwa babu irin wanda ba'a nema dan zubar da cikin ba amma cikin ikon Allah babu abunda ya samu cikin.

Watan haihuwar ta yanayi, wata ranar laraba naquda ta kama ta, akayi sa'a Jamila ta zo gidan, dan haka itace ta shiga taimaka mata, dan ko asibiti kin kaita tayi a ranta tana addu'ar Allah yasa d'an ya mutu.

Jamila ce ta kira farouq ta sanar dashi halin da ake ciki kasancewar a lokacin yayi tafiya baya kasar, addu'a yayi wa matar sa had'i da cewa gobe idan Allah ya kaimu zan biyo jirgi.

bayan ta gama waya da shi suwaiba ta kira, tana d'auka tace gwaggo" na kuda Rukayya take, cikin tashin hankali suwaiba tace Kuna ina?

Muna gida gwaggo" yawwa to duk abunda ake ciki kina kirana kina sanar dani to gwaggo.

daga haka ta koma daki ta leko Rukayya wacce ke ta faman wahala da addu'o'in samun Sauka lafiya.

har karfe taran dare bata haihu ba Sai gurin sha d'aya na dare Allah ya sauke ta lafiya ta haifa kyakyawan yaron ta, Masha'Allah. Saidai ko minti biyar ba ai ba ta sake haifar wani.

ido ta zubawa yaran tana sauke numfashin wahala.

Sai lokacin Jamila ta koma shigowa jin kukan jinjirai har biyu. Wata irin fad'uwa gaban ta yayi lokacin da tayi arba da kyawawan sojojin.masu tsananin kama da juna.

Murmushin yake tayi had'i da fad'in Masha'Allah sannu matar Yaya barka.

Kai kawai Rukayya ta daga mata.

Waje Jamila ta fita tana fad'in bari su rakiya su had'o ruwan wankan.

tana fita ta labe ta kira wayar gwaggo ta sanar da ita wata irin muguwar fad'uwar gaba ce ta kama ta, su da suke jira ya mutu su ci gado shine zai haifi Yaya har biyu duka maza?

Ba zata sabuba, dole su nema mafita.

a cikin daren akayi wa Yara wanka aka shirya su cikin kayan sanyi masu kyau iri d'aya.

Anan jamila take tambayar Rukayya dama kunsan yan biyu ne kenan?
Uhmmmm! tace mata kawai, dan yau d'aya taji haushin kin kaita asibiti da jamila tayi.

*******
Misalin karfe biyu na dare barayi sukai wa gidan dirar mikiya.

Sosai Rukayya" ta shiga tashin hankali lokacin da barayin suka shiga har d'akin ta.

Jamila ma da kukan ta kamar batasan komai ba.

Haka Rukayya"tana ji tana gani suka tasa keyar yaron ta d'aya daga cikin biyun da ta Haifa.

Koda gari ya waye jini ya tsinke mata har ta Kai ga suma.

Alhaji farouq zaucewa ne kawai baiyi ba lokacin da yasamu wannan mummunar labarin.

Sunyi kuka shi da matar sa kamar me saying that dai basu isa su canja allon kaddarar su ba.

Haka suka danga na, mus"ab ya taso cikin so gata da kulawa,, wanda iyaye suka d'auka suka kwallafa masa rai.

Hajiya suwaiba basu sauke qudurin su na ganin bayan magajin farouq ba haka kuma suna kan bakan su na Kawar dashi kansa farouq d'in bayan sun halakar masa da d'an sa.

Wannan shine asalin tarihn Alhaji farouq.




Kuyi hakuri insha'Allah gobe zanyi next page🤣😂🙏

Bbu editing dai Tohm 😢


Xinnee smart 😘

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro