33
For you my anmata my kawaye and also my sister's love 😘Amishty😘Flasher😘zarah Muhammad Mahmoud💕Billy queen❤️lady of the rose😍Afra Cutie💋zeety 💞Fiddah 💓Inner Ibrahim kime😘Fateema Habeeb💕meenah Parrot😍 Masu aure a cikin ku Allah ya zaunar da ku lfy ybada zuri'a d'ayyiba saliha🙏yan matan ciki Allah yakawo miji nagari mai albarka, in kwaso shoky 🤣💃💃😂
"sosai ko wanne yake duban d'an uwan sa, Zaid" ko'karin tashi yake amma ya kasa, cikin 'karfun hali mus"ab, ya matsa gaban sa dafa shi yayi, yana mai cewa kayi a hankali garka fad'o.
Waye Kai?
Ya tsinci tambayar Zaid,
Kallon sa mus"ab yake cikin yanayin sa na da mai cike da miskilanci, yace ni yada ce nai maka wannan tambayar saboda na ganka a matsayin d'an iyaye na alhalin nine kawai d'an da suka mallaka a duniya.
Zaid shiru yayi ya kasa cewa komai, duk da shi yayi tambayar, sai yanzun ma yake jin haushin mai yasa yayi tambayar.
Murmushi mus"ab ya saki, had'i da cewa, let stop all this, we have to face reality.
Zaid" ni d'an uwanka ne wanda iyaye na suka rasa ka Wanda bansan yadda akayi hakan ba..... ni ba d'an iyayen ka bane!
Zaid ya fad'a muryar sa na wani irin rawa.
Kallon sa mus"ab yayi yace ya kamata ka yarda dan kamannin da muke kawai ya isa ya tabbatar maka we are twins, yan biyun ma edentical.
Kai dan Allah saurara, na fad'a maka ni ba d'an iyayen ka bane ko? Kama ce kawai muke, ni maraya ne wanda Allah ya hallicce ni a tsakanin mutum biyu wanda bansani ba ko ba ta halal iyayena suka samar dani bane? Wanda hakan yasa suka yarda ni bansani ba!.... ya karasa fad'a hawaye masu d'umi suna sauko masa.
Zaid"inada tabbacin iyayen mu d'aya da kai ko dan evidence d'in da nasamu.
Wani kallo Zaid yayi masa zuciyar sa na masa zafi, ta Yaya iyayen mus"ab suka zama iyayen sa?dan suna kama kawai sai su kasance iyayen sa, ina! wadannan mutane ne masu kirki mutumci da karamci uwa uba arziqi.
Naka iyayen fa? Zuciyar sa ta tambaya.
Shiru yayi ya kasa bata amsa, sai sauke numfashi yake.
dafa shi mus"ab yayi, Zaid" muna bu'katar lokaci Eh nasan hakan dole mu bukaci lokaci domin abubuwa da yawa suna faruwa damu a lokacin da bamu da masaniya saidai a matsayin mu na musulmai sai mu saka su a jerin kaddara wanda Allah (SWT) yake jarabtar bayin sa a yadda yaso haka kuma lokacin da yaso.
Shiru Zaid yayi sai ajiyar zuciyar da yake sauke wa saboda rashin iyaye wani miki ne da ya dade da binne shi a kasan ransa ba dan ya warke ba saidai dan haka shine mafita a gare shi.
Zaid" abunda nakeson fad'a maka shine, inason 'karin haske a game da Rahamu da yar ta wacce ta bata, saboda yana da mahimmanci dakatar da ita.
Wani irin kallo Zaid ya watsa masa har saida ya tsargu.
Kafun yace mai kasani game da Rahamu? garka soma yin ganganci da rayuwarka hka kuma inason kasani, nine nake da alhakin gamawa da Rahamu ba Kai ba dn hka ka barma tunanin shiga Al'amarin Rahamu,, lafiya kawai nake jira insamu nasoma yakar ta.
A a Zaid" baza mu jira ba, a halin da nasamu mutanen gidan na fahimci ta rusa musu farincikin su, uwa uba Kawar da yayan su da tayi.
Shiru Zaid"yayi yana sauraran mus"ab gaskiya ya fad'a saidai anya zai bar mus"ab ya tunkari Rahamu kuwa,? Rahamu fa mace ce mai ban tsoro saboda duk wanda bai tsoron Allah hakika abun tsoronta ne..... dafa shi da mus"ab yayi ne ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya Lula.
Dan Allah kar kace saika warke zamu soma wannan yakin, dan nikam na riga da na fara, nan ya bashi labarin duk yadda sukayi da ita.
Duk da halin damuwar da Zaid yake ciki amma saida ya d'an Dara. Sabida dramar tasu ta saka shi nishad'i.
Ya tabbata mus"ab ba karamun d'an yi bane,
bai sake cewa komai ba Sai kallon mus"ab d'in da yake.
Dan Allah na rokeka garka ce a a.
Ni yanzun had'in kanka da goyon bayan ka kawai nake nema, kuma ina neman alfarmar ka dan Allah.
kallon sa Zaid yayi da alamun neman qarin bayani.
Inason Kaci gaba da zama tare da iyaye na ba tare da ka bayyana musu gaskiyar kai ba d'an su bane na rokeka, idan yaso bayan ka warke sai mu San yadda zamu sanar dasu.
gyada masa Kai kawai Zaid yayi zuciyar sa babu dad'i.
a gurguje, mus"ab ya fito daga asibitin.
Kai tsaye ya nufa gun shiga mota, yahau motar Abuja. (sai muce Allah y kiyaye, Rahamu maza bisa kanki 😂🤣lol)
*******
Hajiya Jamila" mintina 30 da zuwan ta police station, amma duk tayi wuri2 da ita,
Yanzun ma Alhaji farouq, ne yazo tare da Cp. Anan division d'in da aka tsare yaran itama anan aka tsare ta.
Shine yasa aka fito da ita, tana ganin d'an uwan nata ta wani saka uban kuka.... Allah sarki d'an uwa, shi kuwa jiki na rawa yayi kanta yana fad'in yi ha'kuri Jamila nasan ma babu laifin ki a cikin wannan al'amarin.
Wani irin kuka ne yazo mata mai cike da nadama marar amfani. Cp ne yayi gyaran Murya, had'i da fad'in... kamar yadda na fad'a maka taki magana, saidai hakan bashi zaisa mu cire ta a case d'in ba, wannan ne ma yasa naso tayi maganar Koda kare kanta tayi saidai ta'ki tace komai, tasani mu shirun ta a gurin mu yana da ma"anoni da yawa daga ciki kuwa harda ita d'in ce tasaka su,
Numfashi Alhaji farouq" ya sauke had'i da fad'in Jamila kiyi musu bayani baki San komai akan wannan al'amarin ba ko ba komai nasan zasu gamsu dn nasan har Abada ke ba mai cuta ta bane, wani irin kuka ta fashe dashi Allah sarki yayana shi yana zaton Jamilar sa bazatai masa haka ba, baisan tun tuni na zama azzalumar mara tausayi ba, wani kukan ta koma sakawa.
ri'ke hannun ta yayi yana mai rarashin ta da tadaina kukan, shi ya yarda da ita yasan bazata taba aikata masa hakan ba.
da kyar ya lallaba ta tadaina kukan, waje yace taje ta jira shi ya bata key d'in motar sa yace ta shiga ciki ta zauna yana fitowa.
Bayan ta wuce Cp ya dube shi had'i da bashi wata takarda yace gashi kayi signing, inyaso ranar da zamu kotun zan sanar da kai sai ka taho da kanwar taka.
Ngode sosai Cp Allah bar zumunci.
No"babu komai.
Musabiha sukayi yafita Kai tsaye inda yayi parking motar sa ya nufa, yana daf da bude motar domin ya shiga yaji muryar Jamila tana waya.......wlh tallahi da kyar idan sun yarda dani dan naga shi babban d'an sandan sai wani, cewa yake ina cikin wanda ake zargi tuna yan is kan yaran suka fad'a sunana, wai baki biya su da kyau bane ko?
OK...... Shiru tayi ga dukkan alamu tana sauraren wanda suke maganar ne.
OK tom da nakoma gida kuwa Eh zanyi wanka in shirya sai inje hospital d'in, tana maganar ne tana wani leke leke, saidai dake iya side d'in da take take leke leken sai Sam bata ganshi ba shi kuwa dafe Saman motar yayi.
Inna"lillahi wa'inna ilaihim"raji'un!
Shi yake maimaita wa yana mai jin wani iri a ransa har zuciyar sa, Jamila kanwar sa uwa d'aya uba d'aya Kodai mafarki yake yi ne?
Wata irin jarumta ya d'auka ya saka wa kansa kwabkwasa motar yayi bayan ya tabbatar ta gama magana,
Goge hawaye ta shiga yi, shi kuwa baice mata komai ba yaja motar da sauri har gidan ta yakai ta, Zata Sauka yace kiyi ha'kuri Jamila insha'Allah case d'in yazo karshe!
yana fad'in haka yace sai anjima kije gida ki huta.
tana Sauka yaja motar da gudu zuciyar sa na tsananin zafi, wani guri ya nufa, yana zuwa bai jima ba ya wuce hospital d'in Kai tsaye d'akin Zaid y nufa,
Zaid na ganin sa gaban sa ya fad'i saboda bai taba ganin kamannin sa da mutumin ba Sai yau.
A sanyaye yace Abba sannu da zuwa.
Yawwa" mus"ab y karfin jikin?
Alhmdllh Abba" nasamu sau'ki.
Yawwa likita yace a fad'a maka kar ka sake cin komai daga yanzun zuwa gobe,
Bai kawo komai ba yace to Abba insha'Allah.
Yawwa yaron kirki ya fad'a yana mai shafa kansa had'i da fad'in Allah yayi maka albarka.
Amin y Allah. Ya fad'a a kasa Lance dan haka kawai yaji kalaman sun sanyaya masa jiki.
sallama Abba yayi masa ya fita.
Kai tsaye gida ya nufa yana zuwa ya samu Mami da UMAIMAH suna shirin zuwa asibiti gun Zaid.
Sannu da zuwa sukai masa ya amsa kafun ya wuce sashen sa.
Bayan sa Mami ta bi da Lemo hade da cup a d'an karamun tray.
Samun sa tayi a zaune kan gado ya dafe Kai, ajiye tray d'in tayi kan stood, zama tayi a gefen sa had'i da sauke hannun sa daga kansa a hankali.
duban ta yayi a sanyaye,
Alhaji" lafiya naga alamun Karaya a tattare dakai?
Hummmm! babu komai Rukayya" hasali ma idan da abunda yake damuna bai wuce Jinyar Mus"ab ba.
Ayyah" ai Alhaji jikin nasa ma da sau'ki insha'Allah zaiyi tafiya da kafafun sa.
to Allah yasa, amin y Allah.
Wai ba fita zakuyi bane?
Eh fita zamuyi gun mus"ab d'in zamuje yawwa Madallah maza ku hanzarta.
tom sai mun dawo,, ta fad'a had'i da sumbatar hannun sa, murmushi yayi.
Itama murmushin tayi ta fita cike da annuri hakika tana tsananin son mijin ta. Yayi mata komai a Rayuwa ya taimaka keta lokacin da take neman taimako, ya so ta lokacin da take neman a sota shi d'in abun so da kauna ne.
*********
Koda mus"ab yakoma gida yamma yayi, hankali kwance ya shige part d'in sa, dan Dad baya gari bare yace ina yaje, haka kuma Rahamu"ma bata wuni a gida ba.
Wanka yayi ya rama sallolin da ake binsa.
Yana gama wa yaci takeaway d'in da yayi kafun ya shigo gidan, shirin bacci yayi bayan ya wanke bakin sa.
System d'in sa ya d'auka, ya soma shiga inda duk yasan ya kafa secret camera's d'in sa. Komai yana nan yadda yabar shi kasancewar bata wuni a gidan ba, dan haka babu abunda ya samu.
Kashe system d'in yayi ya kwanta, had'i da yin addu"o'in kwanciya, ya Shafe wa jikin sa.
dare ne sosai misalin karfe2 ya dinga jin magana a kansa,..... Zaid"......Zaid.... Zaid.
Kayi mun.....!
Nace kayi mun!
Zan kashe ka...... Idan bakayi mun biyayya ba....
Wata irin razana yayi ya tashi daga baccin Inna"lillahi wa'inna ilaihim"raji'un. Ya shiga maimaita wa. had'i da yin addu'ar mafarki.
kallon d'akin yayi gabas da yamma kudu da Arewa baiga komai ba dan haka ya shige toilet alwala ya d'aura ya shiga gabatar da nafilfili.
Baccin da baiyi ba kenan!
******
A hospital tunda su Mami suka je suke ta faman fira, ita dai baby tana daga gefe, saidai tayi murmushi ko kuma ta Kalle su kawai.
A haka hajiya Jamila ta shigo ta same su,
Murmushi tayi ta zauna aka gaisa ta tambayi mai jiki, nan aka ci gaba da fira da ita, daman da ta shigo ta ajiye basket d'in abinci.
Kuma Mami batasan da shirin Alhaji" na cewa doctor yace kar yaci abinci ba.
Shi kuwa Zaid bai kawo komai ba.
Haka sukai ta fira cikin raha da annashuwa.
Daga bisani ma Mami da Jamila fita sukayi zuwa, farfajiyar asibitin, suka zauna kan wasu kujeru, suna ci gaba da fira.
Zaid ganin sun fita ne yasa ya zubawa Gimbiyar tasa ido,
Itama kallon sa take a sace, dukan su basu ce komai ba.
Zaid ne yayi gyara Murya.... da hanzari baby ta dube shi, a zaton ta ko wani abun yake so ta kawo Masa, sai taga kawai ya dube ta yayi murmushi alamun tsokana ce,
Murmushin itama ta saki, taci gaba da kallon wayar ta.
Muryar sa tajiyo yana fad'in.
Rana wata shaida suke... Ni naki ne!
Da za'a tsaga jinin jiki sunan ki ne!
In muttuwar huju'a tazo sanadin ki ne...!
Maza kama hannu na!
Ki taho a damana da zanrrasa ki masoyiya ranar ko zanbar duniya...!
tun da ya soma ta zuba masa kyawawan idanuwan ta.
Shiru yayi bayan yakai baitin, maida duban sa yayi gurin ta, gani yayi ta zuba masa ido,
Ware idanuwan sa yayi alamun what??
girgida Kanta tayi had'i da yi kasa kyakyawan murmushin ta, tashi tayi zata fita har takai kofa, ta juyo, ganin tayi ya zuba mata idanuwan sa masu kyau.
Murmushi ta sakar masa had'i da daga masa yan yatsun ta babban da Manu nin 👌.
Kafun ta fice daga d'akin.
Murmushin sa mai kyau yayi, had'i da shafa gashin kansa, yana wani lumshe idanuwa.
******
Karfe 9na dare yunwa ta isheshi, kasancewar shi d'aya yake kwana a asibitin dan suna da masu jinya.
Wanda yake kwana dashi ya fita, tsaki yayi shi kam bazai jira ba dole yasamu abunda yabawa cikin sa.
Basket d'in da Jamila tazo dashi ne idonsa yakai Kai.
d'auka yayi yashiga dubawa, tuwon semo ne da Miyar ganye wacce ta sha agusi da naman Kai.
Tsabar yunwar da yake ji jikin sa har rawa yake, dan haka babu wani jira yasoma aika loma saida ya 'koshi ya rufe ya ajiye, kan drower d'in.
Mai Jinyar sa ne ya shigo.
Ruwa ya ce ya bashi, d'auko masa yayi a fridge, saida ya sha ya wanke hannun sa a robar da aka ajiye masa dan wanke hannu.
Hamdala yayi, kafun ya jingina kansa da pillow.
*******
Sosai Abb" ya matsu Mami tayi bacci dan ya samu ya kalla camera d'in da yasaka a d'akin.
Sai guraren 10 Mami tayi bacci.
jiki na rawa Abba yasoma kalla daki daki tun zuwan su Mami har zuwan Jamila har wucewar ta, numfashi ya sauke hankalin sa ya d'an kwanta ganin har Zaid d'in yayi kwanciyar sa alamun bacci zaiyi.
Har zai rufe kuma ya tsaya dai dan ganin sauran, lokacin da yaga mus"ab na cin abincin da Jamila ta kawo tamkar zuciyar sa zata buga. ganin har yagama babu abunda ya same shi ne yasa ya d'an kwantar da hankalin sa, sai dai me?
Ko kyafta ido baiyi ba ya hango Zaid yana wani irin tari mai tayar da hankali da sauri yaga wanda yake Jinyar sa yana girgiza shi hankali tashe, daga bisani yaga jini na fita daga baki da hancin sa.
Wani irin mummunar fad'uwar gaba yaji lokacin da yaga Zaid d'in ya zube alamun ma babu numfashi a tare dashi.
Inna"lillahi wa'inna ilaihim"raji'un!
Jikin sa na rawa ya zari jalabbiya ya zura, key d'in mota ya d'auka, da mugun sauri ya fice daga gidan.
Yana tafiya yana ayyana wa a ransa matu'kar Jamila ta kashe masa da to babu makawa sai ya kashe ta, wannan wani irin maseefa ne d'an uwan ka yana neman ganin bayan d'an ka duk da irin halaccin da akai masa? Tabbas hakane dama d'an Adam abun tsoro kaga mutum a rana kasa shi a inuwa ko'karin tura ka a ranar ma yake.
Waye Alhaji farouq da hajiya Jamila har ma fa hajiya Rukayya azumi da mahaifiyar ta???
Mu hade a next page 😂😘
Ummmhhhumm 💋u my guy's 😘
Editing babu 😥
Xinnee smart 😍
Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro