Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

32

For u, kawaye na abokan rigima ta kawayen Rahamu 🤣Mum nadeer😍Mrs Mahmoud 😘Eashert Mustapha 😍, Allah ya raya zuri'a yabar zumunci 🤗😍

Ammi"na bonu ammi anya mus"ab ba guje mun yayi ba? Kamar sauran samari na na baya.    ta fad'a hakan tana mai fashewa da kuka. kafadar ta uwar ta dafa.

SIDEEFA" ina ji a jikina mus"ab tsakani da Allah yake sonki, musamman idan kikayi duba da irin hidimar da yake da ke ga tarin kulawa, wanda ke kanki kinsan a kaff samarin da sukayi sonki babu kamar mus"ab, dan haka ni ina ganin addu'a zamuyi Allah idan da alkhairee Allah ya dawo da shi gare ki kuma Allah yasa ma dai yana lafiya.

Ammi" kina gani jarabawa zanyi amma dole saina biya mus"ab shine kawai wanda nake tunanin zai biya mun shine wanda zai d'auka nauyi na ba tare da gajiya wa ba, saidai Ammi lokaci d'aya ace na kira shi amma babu amsa hasalima wayar bata zuwa. Ammi ina tsoro idan Shima ba iyayen sa bane suka ce bazai aure ni ba banda ubangiji kamar sauran masu zuwa kwana biyu su gudu. Ammi"wlh hankali na bazai taba kwanciya ba ina matu'kar son mus"ab.

mus"ab bugun zuciya ta ne, Ammi"wlh kirjina zafi, ta karasa fad'a tana dafe saitin zuciyar ta, sai wani irin wahalallen kuka take.

Rungume ta Ammi tayi a jikin ta tana mai tsananin tausayin yar ta, mus"ab namiji ne da duk yar da tara sa shi zata iya zubar da hawayen ta a kansa.uwa uba gashi da tausayi.... wanda shine silar soyayyar sa da sideefa.

  Ci gaba tayi da rarrashin yar ta.

********
A gaskiya ina da jan aiki a gabana dan matar nan Sam naga alamar da gaske takeyi.

Mus"ab ne mai wannan tunanin, a daki sai zagaye yake, kwakwasar da ake ce tasa ya bud'e kofar mai aikin Rahamu ce, na kurmaye tai masa hajiya tana son ganin ka a sashen ta, gyda mata kai yayi.

Kafun yayi gaba, d'an jin gina Laure tayi tace ohhh ko ta Yaya zan sanar dashi kar yaci abincin da hajiya zata bashi?

Karaf!...a kinnin mus"ab.

Yace au"wani kulli tayi kenan?

Kamar Kar yaje sai kuma ya fasa kawai sai ya nufa apartment d'in kai tsaye.

A sanyaye Laure ta bi bayan sa tana ta saka yadda zata taimake shi.

Yana shiga ya zauna kan d'aya daga cikin kujerun parln.

Kamar ko yaushe cikin izza da isa ta fito, tana faman tazgar kai.

Karewa Zaid kallo tayi bayan ta zauna, zama na irin nida parlour na,

Wasu takardu ta mika masa,

Amsa yayi gaban sa na duka.

Alamu tai masa na kurame tana magana, irin wannan takardun zaka d'auko min a safe d'in Alhaji.

Gaban sa ne ya fad'i, saidai bai ce mata komai ba hka kuma bai mata alamar komai ba.

Laure... Laure " ta shiga kwalawa mai aikin ta kira, sai ga Laure da hanzarin ta.

Ga...ni hajiya.

Ki kawo abinci, to tace, jikin ta a sanyaye ta d'auko ta kawo gaban mus"ab ta a jiye.

Rahamu" da kanta ta zuzzuba masa had'i da mika masa.

Karba yayi, ya kurawa abincin ido, tana zama ya bita ya mika mata abincin kallon sa tayi had'i da murmushi, tace ka ci mana, tana yi tana kwatanta maganar ta da hannu.

      Spoon d'in ya d'auka ya debo abincin ya nufa bakin ta da shi, girgiza Kai ta shiga yi tana cewa Kai nifa bazan ci ba naka ne kai kad'ai jeka jeka ka ci, tana maganar tana ja baya, shi kuwa dariya yayi tamkar wani zararre, yashiga ko'karin dura mata abincin gadan2, ihu Rahamu" tasa

Kai nifa Bana ci billahillazi garka bani abincin nan kaji kuraman banza, Wayoooo!

Ai kuwa mus"ab bai fasa ba ci gaba da ko'karin tura spoon d'in bakin ta yake, ta sake sakin ihu, tana fad'awa kan kujera.

a lokacin ne, Laure ta sheko da gudu dan ganin mai ke faruwa hajiya take sakin ihu haka?

ganin abunda yake faruwa sosai hankalin ta ya tashi saidai wani bangaren na zuciyar ta hamdala tayi ta godewa Allah da bai ci ba.

duban ta takai kan hajiya wacce ta had'a uban gumi sai ihu takeyi. abun tausayi abun dariya..

Zaid.... Zaid.... Lafiya?

bai ce mata komai ba Sai sake nufar bakin Rahamu yake da cokalin wanda duk abincin ma ta barar dukan su basu lura ba.

   Wayoooooooooo Laure.... Kiramin su idi yaron nan ya hauka ce.... Wlh dawanau Alhaji zai Kai shi.... Wayoooo ni Rahamu na janyo wa kaina, Kai dn ubanka bazan ci ba.

Aikuwa ya kaiwa bakin ta dam'ka, tana jin haka ta Sanya ihuuuuuuuuuuu, da ka karin amai. Cokalin na soma shiga bakin ta tasaki wani uban amai da tari had'i da uwar tusa.

a daidai lokacin ne su mai gadi suka iso, rirrike Zaid sukayi, shi kuwa sai gumji yake kamar mai aljanu, da kyar suka kaishi d'akin sa.

Rahamu tana ganin an tafi da Zaid, tasaki wani mugun zawo tsiiiiiiiiiiiiiiiiiiiiii. Mai tafe da fitsari, Raba raba ta shige toilet, sosai ta zuba uban zawon ta, da amai, kafun ta hau sauke numfashin wahala,

         Wayooo ni Rahamu na debo ruwan dafa kaina, tana fad'a tana sakarwa kanta shower, saida ta gama wankan ta fita toilet d'in kan gado tayi branching,

Kaza"uba, kaga d'an is kan yaro zai kaini ya baro tsinanne ashe ba kurmance wa kawai yayi ba harda hauka cewa yayi, wlh y hauka ce, dama ance kurame yawanci basu cika hankali ba.

Wai! Allah ya bele ni da na bonu yau saidai in tsinto kaina lahira, boka fa cewa yayi idn bashi yaci ba wani yaci to saidai gawar sa, dan da jinin Zaid da sunan sa akayi aikin. Rahamu wuni tayi tana gudawa.

*******
d'aki aka saka Zaid"aka rufe, yana jin alamun wucewar su idi, ya soma babbaka dariya har yana kwallah,

Idan ya tuno yadda take zazzaro ido tana ihu sai ya sake saka dariya, kai wanda bai tsoron Allah yafi kowa tsoro.

Azzalumar mata kawai.

Saura next target d'ina.

Ya fad'a yana sakin dariya.

*********
Zakuyi bayani ko sai mun Kai ku kotun?

Shiru ko wannen su yayi fuska tayi musu sutum sutum, saboda ba qaramun duka suka ci ba.

Sargent"

"yes sir

Maida su ciki inaga basu shirya yin magana ba, idan ka maida su ka tabbatar yau sunyi rawar bori, ta hanyar kunna musu shocking hope ka gane mai nake nufi.

Yes sir"

Gud.

Wayooo Allah yallabai dan Allah kayi ha'kuri nidai zan fad'i gaskiya,

Kallon sa Cp yayi had'i da fad'in ina jinka.

a. a... ummm... Umm!.... daka tar dashi Cp yayi ta hanyar cewa..

Kaga bamu da ishashen lokaci dukan mu, zaku iya samun rangwame idan har muka gano ba laifinku bane kai tsaye bi'ma'ana dai akwai wanda kuke wa aiki, yawwa to za'ayi muku adalci daga nan har kotu, dan haka kayi maganar ka kai tsaye.

ranka ya dade kanwar Alhaji farouq ce ta saka mu!

What?

gyada kai suka shiga yi kamar kadan garu, eh yallabai, wlh itace ta biyamu.

kan Cp ne ya kulle,

Yace,
. Are sure that you guys are telling me the truth?

Wannan ba karamun case bane so duk yadda kuke tunanin sa ya wuce nan. So is better ku fad'amun gaskiya tun anan dan idan kuka mun karya to fa, zakuji jiki.

Wlh tallahi..... Suka hau rantse2

Yallabai gaskiya muke fad'a maka.

Shikenan, sergeant, take them in.

********
Yau mus"ab tun safe ya fita, bai dawo ba saida yamma yana dawowa ya wuce apartment d'in sa, wanka yayi ya bude takeaway d'in da yayi daga waje,

Bismi"llah yayi ya soma ci hankali kwance haka kuma cikin nutsu, yana jin nishadi a ransa yana d'an ratsa shi ko ba komai yasamu abunda zai iya gane kullin Rahamu hakan ka na sanyaye ransa.

Saidai kuma yana matu'kar son ganin iyayen sa, haka yana son sanar dasu d'an su da ya bata yasan inda yake, to amma ina yake? bashida Amsar basu dan haka gwara kawai ya jinkirta sanar dasu,  har zuwa lokacin da aka ga Zaid d'in saidai yana bu'katar ya tabbatar musu da yana Raye, dan yasan duk inda hankalin su yake to fa yana kan shine.

dole ne yaje gida dan hankalin iyayen sa ya kwanta.

******
A a a.... Cp badai Jamila ta ba, Sam wannan ma zancen banza ne Lallai dole inyi shari'a dasu idan angama ta d'ana....

Katse shi Cp yayi.

Saurara Alhaji farouq" ni kaina nayi mamaki da wannan zancen saidai fa muna bu'katar mu tsawaita bincike sorry to say amma yazama dole mu d'auko kanwar ka dan ta amsa wadan su tambayoyi.

ban amince ba Sam!

Wannan kuma wani abu ne na daban, please let us do our job.

Cp na gama fad'in haka ya shiga kiran wayar yaran sa, suna d'auka yabasu umarnin tahowa da Jamila.

Abba ya naji yana gani.

******
Yau tun sassafe Rahamu" ta fice daga gidan,

Mus"ab na ganin ficewar ta ya nufa boys querters, kwankwasa kofar d'akin da su Laure suke ciki yayi, cikin sa'a kuwa itace ta bud'e kofar, yafuto ta yayi da hannu alamun ta zo, komawa yayi apartment d'in sa Laure tana biye dashi cikin mamakin ko lafiya?

Sai kuma tayi tunanin kodai wani aikin za'ayi masa ne,

Shiga yayi parlourn Laure tayi tsaye tana jiran d'auko abunda Za ayi masa tunda su basa shiga d'akin mazan gidan saidai namiji ne yake masa shara da komai da ya shafe shi saidai ko  girki wannan shine kawai abunda mata yan aiki sukeyi a gidan.

mus"ab ganin bata biyo shi bane yasa, ya leka had'i da kiran ta da hannun sa dai irin na kurame,

Sukuti... Laure tayi tana tuna yadda aka sha fama tsakanin sa da Rahamu" kallon tazarar dake tsakanin ta da bakin gate tayi kafun ta had'i yi wani yawu makwatt.

Allahumma"...... Ohhhh Allah addu'ar ma to Kodai in fad'a komai ta fanjama fanjam jam, na bonu yau, ba abun ka gudu ba yanzun kuma harakar masu kud'i azo a gargada ka,

Kai... Kai..... kawai guduwa ta zanyi MI yafi ranka armashi?

Lissafe lissafen da Laure ta shiga yi kenan, mus"ab kuwa dama ya koma ciki yana duba wasu takardu yana jiran shigowar ta.

Ke Laure rufa wa kanki asiri ki d'an Kara dosana shekaru, Koda dai ansha ruwa ai mutuwar ce ba sonta ake ba, ohhh ni,

Duk Laure ce mai wannan tunanin na rashin makama, daga karshe dai tayi abunda ake kira shahadar 'kuda.

Shiga d'akin tayi jikin ta har yar karkarwa yake marar ta kuwa tuni ta cika da ruwa 'kyas take jira ta saki lafiyayyen fitsari.

Idanuwan nan sai rarraba su takeyi kamar wacce tayi wa sarki karya, zanin ta a hannu, haka ta tsaya baki bakin kofa,

d'agowa mus"ab yayi ya dube ta, kafun yace....

Ki shigo da kyau mana.

Wani irin waro Idanuwan ta tayi,

A ranta tace ni Laure yaron nan anya shi kansa ba aljanin bane, jiya ma a kurma yake yau gashi da baki, na bonu, cikin yan seconds tayi wannan tunanin, Katse mata tunanin yayi ta hanyar cewa,

Kinga ki shigo ki zauna baaba Laure magana zamuyi,

Sake hiddo Idanuwan ta tayi,

Saidai bataki Zaman ba neman guri tayi ta zauna tana sakin addu'o'in ta wanda ita kanta bata ce ga abunda take fad'a ba.

Laure" dan Allah ki nutsu ki saurare ni, abunda nake son fad'a miki shine....

tun farko ina magana kawai nayi alamun bana magana ne saboda nagano Rahamu" tana da wani kulli a ranta game dani, shi yasa nayi wannan pretending d'in.

Abunda yasa na kira ki kuwa wani taimako ne nakeson kiyi mun ina fatan insamu had'in kanki, bai bari tace komai ba yaci gaba da cewa.... wato tun jiya da naji kina fad'in da kina da yadda zakiyi da kin taimaka mun, har kike cewa da kinsan yadda zaki fad'amun da kince mun kar inci abincin nan. na fahimci tsakani da Allah kike zaune da mai gidan wannan ne ma yasa nake neman taimakon ki dan fitar da bayin Allah nan a halin da matar nan ta jefa su, wato na Gano abubuwa da yawa wanda ba Lallai ke kinsan su ba.

Inason ji zaki iya taimaka mun?

Hummmmmmmm! Laure ta sauke ajiyar zuciya,

Waton a gaskiya hajiya Rahamu" mace ce azzaluma na sha ganin ta tana zubawa Alhaji asiri a abinci haka nakanji wasu daga cikin sirri kan ta wanda ita kanta bata San naji ba, Sam bata tsoron haduwar ta da Allah.

Ni wlh a shirye nake dan ganin na taimaka maka, insha'Allah,, kuma Allah ya taimake ka akan wannan kudiri naka.

Amin amin"

Yau waye zaiyi aikin shashen ta?

Ya tambaya.

Ni ce kuma ma bata nan.

Wannan ne yasa na tambaye ki dan akwai abunda nake son yi a part d'in.

Babu matsala zaka iya zuwa zan taimaka maka.

Ngode.

Wannan shine abunda yace.
****

Saida ya fahimci hankalin masu hidimar gidan ya d'auku kafun ya nufi apartment d'in Rahamu" Dad dama baya kasar, dan haka hankalin sa a kwance yashiga gudanar da aikin sa yadda yake so, tsab komai ya tafi ba tare da kowa ya sani ba daga shi sai Laure.

Wannan kenan!

*****
Zaid" kwance a asibiti yana ta faman tunanin mafita wa kansa da UMAIMAH"

dan a yan kwanakin wani irin sonta ne yake hufa shi, dan sosai yake jin ta a jini da jijiyar sa, har mamaki yake yadda ko wani lokaci son nata yake sake huda shi, hakika yagama hakikan cewa baby ce walwalar sa dan d'an Zaman da sukai idan suna tare ji yake kamar ya janyo ta jikin sa ya rungume,

Saidai babu halin hakan ko babu ko babu aure ai ba maharramar sa bace,

lumshe kyawawan Idanuwan sa yayi wanda babu komai a cikin su tsantsar fitina nen son UMAIMAH"

dafe saitin zuciyar sa yayi, saboda yadda take bugawa, ko wani numfashi ya motsa jin ta yake a cikin 'kashin sa.

Gizo fuskar ta, ta shiga yi masa, murmushin sa mai kyau yayi kafun ya furta kalmar.

Inason ki yarinya ta!

a haka bacci yayi awon gaba da shi.

****
Tun Asuba da yaje masallaci dama da shirin sa ya fita' ana gama sallah dashi yayi azkar d'in sa, har gari yayi haske kafun ya fice daga masallacin, kai tsaye ya tari taxi.

    Tashar shiga motar kano ya nufa, cikin ikon Allah yayi sa'a, mutum biyu ake nema, ya biya duka na mutum biyun,

take suka hau hanyar kano.

Koda suka isa kano shiru yayi yana karewa tashar kallo da jama'ar dake kaiwa da kawowa, wani mai saida news papers ne ya isheshi da fad'in asiya jaridu Alhaji kasai jarida.

kallon sa yayi yaga yadda yayi uban gumi haka kawai sai ya bashi tausayi, dan haka yace, bani ta wannan satin.

Kud'i miko masa yayi jiki na rawa, tambayar sa nawa kud'in sa mus"ab yayi, ya fad'a masa take ya ciro dubu biyu ya bashi, sosai Mutumin yake zuba masa godiya.

gaba yayi abun sa, adaita2 sahu ya samu zuwa unguwar su, kallon hanya yake,, daga bisani ya soma bude jaridar dake hannun sa, gaban sa ne yayi mummunar fad'uwa.

Sake kallon Hoton jiki yayi Abban sa ne da Hoton sa ranbadadau.

Soma karanta labarin yayi,take jikin sa yasoma rawa, a ransa sai kiran Allahu"akbar yake.

muryar sa har rawa take yace da mai napep d'in ya juya zuwa asubitin malam Aminu kano.

amsawa mai adaidaita sahun yayi dan daga ganin mus"ab d'in ba d'an tsulla tsulla bane dn haka yasan baza a samu matsala gun biya ba.

********
Zaid" baccin sa yake hankalin sa a kwance,

    Yaji an d'an bubbuga shi farka wa yayi yana mai addu'ar farkawa daga bacci.

kallon Mutumin dake tsaye a gaban sa yayi saidai kuma baya iya ganin fuskar sa.

Saboda hular sanyin dake kansa haka haka kuma yasaka hular Hana sallah a kansa wacce ta taimaka gurin boye fuskar sa.

lafiya malam?

Waye Kai?

Wani kake nema ne?

Sauke hular dake kansa yayi had'i da sauke ta sanyin.

Kusan lokaci d'aya zukatan su suka buga!

Washhhhhh Allah na 😂🤣

More comments more typing 😍

Xinnee smart 😘

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro