Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

27

Tunda safe Abba yabi jirgi zuwa Abuja, saidai ko da ya'ki says Airport d'in, babu mus"ab babu alamun sa.

Sosai hankalin Abba ya tashi ganin iya bincike anyi tun daga Airport har zuwa guraren shiga mota, shiru kake ji babu wanda yace yaga ko da mai kama da mus"ab d'in ne, har yamma Abba yana tare da jami"an tsaro dan gano inda mus"ab d'in yake,

       Anje har kamfanin layin mtn, anyi bin diddigin layin mus"ab d'in saidai wayar har lokacin a kashe ta ke. tun bayan inda yayi waya da iyayen sa a Airport kenan bai sake amfani da layin ba.

                 Abba bai samu ya koma a ranar ba Sai kashe gari, cike da gajiya da tashin hankali ya koma kano.

Wanda har ya kasa boye irin halin damuwar da yake ciki.

Mami kasa jurewa tayi lokacin da Abba yayi mata bayanin duk yadda akayi, kuka ta saka masa tana kiran.... Shikenan Abba na rasa d'ana shi ma....!kamar yadda na rasa kowa nawa... Rarrashin ta ya shiga yi yana nuna mata ba wai sun rasa mus"ab bane, suyi ta addu'a Allah zai bayyana shi.

Baby" ma ganin yadda Mami da Abba suke cikin damuwa ne yasa itama tashiga damuwa har da hawayen ta duk da idan dan ta ita ne mus"ab d'in ma Kar ya dawo saidai kuma ganin yadda Mami take ta kuka ne yasa ta ji tanason yin addu'ar Allah ya bayyana mus"ab, d'in a Karo na farko da taji zata iya masa addu'a tun farkon al'amarin.

*********
Wasa wasa karamar magana ta zama babba, babu Zaid babu salma" sosai hankalin Dad ya tashi, da wannan al'amarin, har yar rama saida yayi duk inda ya kamata ayi cigiya anyi amma ji kake shiru,

A bangaren Rahamu" tuni taron biki ya watse sai yan zuwa jaje.

Sosai ta tashi hankalin ta, a cewar ta watan tonon asirin ta ya tsaya, sosai tayi rama saboda wannan masifa, gashi abu a gun wanda addini ma bai dame shi ba, babu addu'a bare yadda da kaddara.

Abunda yafi damun ta shine tsayawar cikar burin ta.

A bangaren Ummi"sosai ta tashi hankalin ta kan cewa Rahamu"ce ta salwantar da Zaid d'in dan a cewar ta tun lokacin da aka soma zancen auren hankalin ta bai kwanta ba dan haka akama Rahamu ta bayyana inda takai Zaid d'in.

Saida iyayen ta suka nuna mata bacin ransu akan zancen kafun ta hakura ta shiga addu'ar Allah ya bayyana zaid d'in.

*******
Bangis kamar yadda ya fad'awa salma cikin daren ya shigo gun ta, haike mata yayi ya shiga yin yadda yaga dama da ita babu tausayi bare tausaya wa.

Saida ya tabbatar ya gajiyar da ita ta yadda ko d'an ya tsan ta bata iya daga wa kafun Sauka kan ta.

duban ta yayi a kaskance, yace wannan shine sakamakon raina mun hankali da kikayi, akwai saura kuma, wayar shi ya nuna mata duban ta takai kan wayar fuskar Zaid" ta gani a ciki gashi zaune duk bakin sa jini alamun yaci duka.

Kuka ta fashe da shi tana fad'in dan Allah bangis ka barmu mu tafi haka idan ni nayi maka laifi ai shi Zaid babu abunda yayi maka, dan Allah ka sake shi.

Wani mugun maka yakai wa bakin ta.

Au dama har haka kike son shi da har kike rokona in sake shi? lallai! to billahillazi kin koma janyo masa dan yanzun babu sassauci... bari indawo Zanzo kanki.

Ficewa yayi daga d'akin yana huci kamar wani kumurci.

Wani mugun kuka salma tasa tana dafe cikin ta dake mata mugun ciwo.

Zeema dake labe a kofar d'akin tana jin su, tana jin alamun fitowar bangis da sauri ta labe ta baya, le'kawa tayi taga ya shige cikin gidan, a sad'ad'e tabi bayan sa.

Wani gini taga ya nufa wanda yake incomplete, a hankali ta dinga bin bayan sa, har ya shige ginin.

a sad'ad'e ita ma ta shiga wani d'aki taga ya bud'e da key, ya shiga.

Wanda ko tantama babu a d'akin Zaid yake,.

Ganin ta samu abunda take so ne yasa ta juya da sauri kafun wani cikin yaran sa ya ganta ko shi kansa.

Komawa tayi d'akin da take tanason sa'ka yadda zata samu kubutar da Zaid daga hannun bangis ga kuma labarin da take son ji gurin salma"!

Zuciyar ta ce tashiga fad'a mata fitar da Zaid daga gidan yafi jin labarin salma mahimmanci, dan haka shine abu na farko da ta d'auki damarar ai watar wa.

*****
babu irin tashin hankalin da su Mami basu shiga ba, musamman ma ita dan har yar jinya tayi.

Sosai ta shiga damuwa akan batan d'an tilon d'an ta, wanda tun ana saka ran kidnappers ne har ansoma zargin ko yan yankan Kai ne, tunda yau sati d'aya cikin na biyu babu labarin mus"ab sama ko kasa.

Baby ma duk ta shiga damuwa da taga abun dai da gaske ne.

Hajiya jameela ma da su hajiya azumi da babarta Inna Rabi" duk dasu ake ji manta wa, (wannan shine makashin ka yana tare da kai)

               *****
Zaid"tunda ya farka ya fahimci inda yake, waton dai Sato shi akayi,, ya shiga tunane2. Waye wannan ya Sato shi mai yake so ko ya d'auka shi d'an Alhaji ne yayi garku wa dashi dan yasamu kud'i?

    Irin dai abunda ya faru da mus"ab shi ya faru dashi yana soma zancen kud'i ya sha bugu a baki. Saida sukai masa lilis kafun suka barshi.

***
Hajiya Rahamu" babu irin tashin hankalin da bata shiga ba duk tayi wata iri da ita, taje gun bokan ta yafi a kirga, amma maganar dai d'aya ce shine ta kwantar da hankalin ta, har tasoma jin haushin kalmar.

                      ****Zeema ce tare da bangis, tana masa tausa.
shi kuwa sai faman sauke numfashi yake kamr mai naquda.

Wata muguwar giya ta tsiyaya masa tana kalailame shi, ya karba ya shiga sha, itan kuwa sai wasu abubuwa take masa dan ta d'auke hankalin sa, aikuwa tayi nasara dan sosai shirin ta, ke aiki a kansa,

Janyo ta yayi zuwa jikin sa, bata wani damu ba ta biye masa kamar abun arziqi, yana ko'karin auka mata giyar tai masa uban karfi, har yakasa controlling karfin sa, zubewa yayi a kan gadon ya shiga sambatu muryar sa ko fitowa ba tayi,

              Da sauri Zeema" ta shiga maida kayan ta, tana gama wa ta shiga neman key d'in d'akin,   cikin ikon Allah ta ganshi a cikin wata drower.

sauri 2 ta fice daga d'akin, d'akin da Zaid d'in yake ciki ta nufa, dake dare ne,

Yawancin yaran bangis d'in sunje club wasu kuma sunje sace sacen su, Allah y shirya mana!

      Koda ta samu ta bud'e d'akin, ganin sa tayi a kwance duk ya galabai ta, da shi.

Zaid"zaid.... ta shiga kiran sunan sa tana d'an girgiza shi, a wahalce ya bud'e idon sa.

Yana tunanin wannan kuma wacece?

Ganin yana mata wani kallo ne yasa tace, ai ka gane ni, zeema ce kawar salma nasan ka ganeni kayi ko'kari mu ka tashi in fice da kai daga gidannan, bamu da lokaci!

     baya wani gane mai take cewa, hannun ta ta mika masa tana mai cewa kayi ko'kari ka tashi kaji.... Kama hannun nata yayi ya tashi suka soma ta fiya tana sagale da shi a kafadar ta saboda sosai jikin sa ya saki saboda uban dukan da yake ci gashi babu wani abincin 'kwarai.

               a hankali suke ta Kawa zuwa mota, dukan su babu wanda yake da takalmi.

a wahalce suka ga sun Kai mota.

taimaka masa tayi ya shiga baya ya zauna ta rufe... ko'karin zuwa bude gate takeyi taji alamun dawowar wasu daga cikin yaran bangis.

Da sauri ta labe bayan motar, har sanda suka shigo... Cikin gidan, suna yan surutan su na yan duniya,

                Suna daf da shigewa cikin gidan tari ya sarke zeema da sauri suka dakata had'i da saurara wa.

Wani irin dafe baki tayi. tana Jan numfashi tamkar zata si'ke nufar motar sukayi dan ganin ko waye hannun ko wannen su ri'ke da bindiga.

       Suna daf da motar wata mage ta gitta gaban su tana miuuuuu... Tsaki suka saki, d'ayan yana mai cewa.... Fuck wannan cat d'in anyi Yr banza, d'ayan yace billahillazi da ace da ne da sai na 'kaddamar mata. Inyi rebun ta in cinye.... Kai aljani baka da mutunci magen zaka ci?  cewar d'ayan.... Yo bazan ci mage ba ai ni nan har bera nayi yayin ci Kai ni tun ina kankani na ko tansoni ban raga wa ba Yaseen....

Haka dai sukai ta surutan su har suka shige ciki... Wata wawuyar ajiyar zuciya zeema ta sauke da sauri taje ta bud'e gate d'in ta koma ta shiga mota.

Key tayi wa motar a guje ta sharci hanya,,

      Gudu teke sosai a kan titi dan hakannan take jin hankalin ta bai kwanta ba.

duban Zaid dake faman sauke numfashi tayi, tace kana Jina,? akwai abunda nakeson sanar da kai... Akan mahaifiyar salma da salmar, amma ban riga da na na gama bincike na ba, amma....... 'karar harbin da taji ne yasa taci wani uban burki ba tare da ta shirya ba da sauri kuma ta sake take motar.

                       du'ka...... du'ka take cewa Zaid,dan ko shakka babu, yaran bangis ne suka biyo ta.

     Da wani irin mugun gudu suka dinga binta, ita kuwa duk inda ta samu fad'awa takeyi.

******
Hajiya azumi... A gskiya wannan plan d'in Sam bai mun ba!

Cewar hajiya Jamila,

Shikenan, Jamila idan dai bazaki je ba. babu damuwa.

dama wai dan dai kiga yadda za'a kaddamar wa, fitsararren yaron ne.

Kuma fa zanso ingani... Saidai haka kawai nake jin hankali na bai kwanta ba.

Kinga idan dai zuciyar ki bata so to kawai kiyi zaman ki.

A a... Azumi zanje!

dole inje inga yadda za'a kashe mun shi a gaba na, zanyi farinciki yayin da naga  gawar sa a kwance.

tamkar wacce aka tsikara ta tashi daga zaunen da take.

murmushi hajiya azumi tayi wanda yafi kama da kin fad'a tarko na!

               

*****
Abba" ne zaune a parlour shi kad'ai yana kurbar furar da Mami ta dama masa, dan yanzun Sam baya wani cin abinci kusan kowa a gidan ba wani abincin kirki yake ci ba.

Wayar sa ce tayi kara, d'auka yayi, ya kara a kunnin sa. had'i da sallama" Eh inajin ka commissioner, OK tom shikenan Allah yasa muji alkhairee.

     sauke wayar yayi daga kunnin sa bayan yayi sallama da cp.

duba number da ake ta faman kiransa da ita yayi, dan yana magana da cp yanajin wani kiran yana shigowa, kafun yakai ga bin kiran an sake kiran sa saidai wannan karon da private number aka ki rashi.

A sanyaye ya daga kiran dan hakannan yaji gaban sa ya fad'i.

Sallama yayi wanda tun kan ya gama kaiwa karshe yaji ansoma magana da wata irin Murya.

Alhaji farouq" matu'kar kana bu'katar d'anka a raye to kaje, Ahmadu Bello way, xnturo maka da address inda zaka samu d'anka.

        daga haka aka katse kiran.

rawa jikin Abba" ya shiga yi tamkar mazari karar text yaji hakan yasa yayi saurin dubawa, address d'in ne.

cikin rawar jiki ya danna kiran cp bayani yayi masa a gaggauce.

            da sauri ya fice daga gidan ba tare da sanin Mami ba.

*********Zeema gudu kawai take zubawa, har saida ta tabbatar ba yaran bangis kafun ta tsaya a gefen titi, numfashi ta shiga sauke wa da wani irin fargaba hakan nan take jin Jikinta yayi sanyi ga  wata irin muguwar na dama da ta shige ta lokaci d'aya.

      a sanyaye ta sauke numfashi duban ta takai kan Zaid"wanda a lokacin ya gama jigata,

         Sake cewa tayi....
na fad'a maka hajiya Rahamu" tana da mugun 'kulli a kanka, wanda take ko'karin cinma wani buri na ta, shi yasa take amfani da kai,... Saidai idan na gama nawa binciken zan sanar da kai inajin son taimaka maka.

Shi dai kallon ta kawai yake dan sam baisan inda zancen ta ya dosa ba, waye Zaid? Wanda take amfani da sunan sa yayin kiran nashi sunan?

Da zai iya da wannan tambayar ya fara mata kafun ya d'ora da son sanin ita d'in wacece? Meye had'in ta da Rahamu salma ?da yaji tana fad'a?

Saida Sam bazai iya wannan dogon maganar ba dan bashida wannan zarafin.

      sake tayar da motar tayi, a guje ta nufa titin da zai sada ta da gidan Alhaji Tahir yuguda"dake unguwar wise2.
sosai take zabga gudu, tana ko'karin shiga layin gidan yaran bangis suka sha gaban ta,

Wani irin burki ta ci, kamar ta tsaya, saida suka yi tunanin tsayawa tayi, ta shammace su, ta raba ta gefen su a guje, aikuwa take wani daga cikin su ya sakar mata bullet, a gefen ka fad'ar ta, wata irin razananniyar kara ta saki, batayi yunkurin tsayawa ba saida ta isa kofar gidan,

a wahlace ta bud'e kofar da Zaid yake tura shi waje tayi.

Ya fad'a sharaf dan ba wani karfi ne a tare da shi ba.

uban horn ta saki, kafun taja motar a guje jini na mata tsiya ya a inda aka harbe ta.

Am sorry bbu editing, kuma maybe baza kuji ni ba gobe jibi, yadai dangan ta da time d'in da nasamu😜🤗

Son_so fi'sabilillah ✌️

Xinnee smart💋👌

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro