Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

26

Mami" ce ke ta faman kiran wayar Mus"ab saidai abun haushin tun d'azu abu d'aya ake fad'a mata shine a kashe wayar ta ke.

          Hmmmmmm! ta sauke numfashi, cikin 'kosawa da tunanin ko lafiya? baby dake zaune kusa da ita duban ta tayi, saidai bata iya tace komai ba, tadai fahimci layin Mus"ab take kira kuma ga dukkan alamu baya tafiya, a ranta cewa tayi Allah yasa ma Kar ya dawo!

             Mami" kallon baby tayi... Ummi" wai kin kuwa gwada kiran yayan naki?
Shiru tayi daga bisani ta ce a a Mami, saboda Sam bata iya karya ba shi yasa ta fad'a wa mamin gaskiya.

Shiru Mami tayi tana duban ta,  har saida babyn ta tsalgu da irin kallon da mamin take ma ta.

  Ummi" tunda ya tafi kunyi waya ma kuwa?

a sanyaye tace a a Mami.

Wani irin abu ne ya darsu a zuciyar mamin, saidai kuma bata da hujja ko dalili to kuma Kar yaran nan su maida su kananun mutane mana.

  Amma ko ma dai Menene, idan Mus"ab d'in yadawo, za ta saka musu ido.

*************
Hajiya azumi" a duniya ke kad'ai ce masoyiya ta Sam bani da kamar ki, kinyi mun halarci, naso ace yaya na ke ce wacce ya aura amma ya Je ya auro dangin mayu,

  Hajiya Jamil ce mai wannan zancen tana dafe da ka fad'ar hajiya azumin,

Murmushi hajiya azumi tayi,  haba Jamila ai ni dake d'aya ne garki manta da mahaifiya ta da mahaifin ki uwa d'aya uba d'aya ai ta wuce wasa..... Abunda nake so kawai ki gane nidai mai kaunar ki ce.

Lemo hajiya Jamila ta kai bakin ta... Saida ta zuka da kyau, kafun ta sauke cup d'in daga bakin ta.

    Aminiya ta, ga Mus"ab a hannu kuma kawar da shi zamuyi, dan haka meye next target?

garki damu Kawa ta, Adai kaddamar wa magajin, domin idan kanason cin dukiya da kyau, to ka kaddamar wa da magajin ta wanda ya mallake ta kawar dashi bazai yi wuya ba.

Hhhhhhaaahhhhaa, kai kawata kuma zancen ki dutse,.

Wani gyada Kai azumi tayi, tana jin kanta ita ga boss, a ranta tana saka yadda zata ci wa Jamila Amana!

******
Wai salma" dun ubanki ba nace ki kira Zaid" ba?  Mommy wlh na kira shi amma a kashe ake cewa tun d'azu.

         a birkice hajiya Rahamu"ta je d'akin ta inda Kawayen ta suke cike, wayar ta ta shiga nema,

Garden d'in gidan ta zagaya, kiran wayar Zaid" tayi a kashe dai,

Shiru tayi gaban ta na tsananta fad'uwa, wata shawara ce ta zo mata.

Da sauri ta danna layin bokan ta, yana d'auka ta soma masa bayani Zaid" tun bayan awa uku dagann yaje ya d'auko friends d'in sa shiru har yanzun bai dawo ba. Itafa tana tsoron kar ya gudu ya tona mata asiri.

           kashe wayar boka yayi bayan yace da ita ta da kace shi. Shiru tayi tana jiran kiran boka, tsawon mintina talatin.

   Yana kira da sauri ta daga jiki na rawa.

Boka ne yashiga yi mata bayani,

Rahamu"ki kwantar da hankalin ki babu inda Zaid" ya gudu, yana nan saidai banga mai ya hana shi dawowa ba.. dan haka Kuci gaba da shagali ko ranar d'aurin aure ne kiyi ko'karin ganin an d'aura auren ko baya nan!

Murya na rawa Rahamu" ta shiga cewa boka kenan zai iya kai wa ranar d'aurin auren bai dawo ba? 

bance ba! saidai kiyi amfani da abun na fad'a miki.....!

yana kaiwa nan ya katse wayar.

Jugumm! Rahamu tayi,, daga bisani ta ja jiki zuwa jikin gidan, tana kokarin danne damuwar ta.

Salma"ce ta dubi zeema ta ce... Zeema da mota kika zo? Eh da mota na zo,

Dn Allah zo muje ki kaini airport, inason inje in duba Zaid ko lafiya har yanzun bai dawo ba daga zuwa taro friends d'in sa. ni wlh gabana sai fad'uwa yake,
                                                to Allah yasa alkhairee ne, cewar zeema tana ko'karin basar da zancen, a ranta kuwa babu abunda take so sama da zancen, saidai dake Yar duniya ce sai ta bagarar da zancen.

Fita sukayi zuwa Airport.  Koda suke mota haka salma tai ta sakin layi da zancen auren nata, zeema dai na jin ta bata nemi karin bayani ba.har suka isa Airport d'in,

Sunyi duba iya duban su shiru, sunyi tambaya saidai ko wanda yaga mai kama da Zaid basu gani ba, dan haka suka hakura zasu koma, lokacin idon salma ya Sauka kan motar Zaid d'in.

da sauri ta karasa jikin motar, ita da zeema. duban motan suka shiga yi saidai kuma a kulle take.

          Haka suka kamo hanyar dawowa salma" duk ta firgice.

Wani mugun burki zeema taci ganin wata mota ta sha gaban su, salma ma a razane take kallon motar da ta tsare su,

Yaran bangis ne suka fito daga motar.

Salma sai cewa take Zeema ja motar mu gudu bangis ne, nasan d'auke ni zaisa suyi kuma wlh bazai barni in dawo ba na shiga ukku. Kafun Zeema tayi wani yunkuri tuni d'aya daga cikin su ya ja ta ya jefa baya ya had'a da salma,

      Ya shiga mazaunin driver, wani yaron ne ya zauna a gefen salma" had'i da nuna ta da bindiga, idan kika sake kikayi mana ihu nan zan fasa kanki da harsashi, banza karamar karuwa.

            ********
basu tsaya da su salma ko ina ba Sai boyayyen gidan bangis.

        Wani d'aki aka ajiye su dukan su,

Salma"sai kuka take gaba d'aya abun duniya yayi mata yawa ita Sam batasan haka TARAYYA(Mamuhlo 💋) da bangis yake ba da bata tura kanta ga wahala ba.

      Zeema kam shiru tayi,, tana tunanin ta yadda zata samu jin sirrin su salma, a bangare d'aya kuma tana tunanin ina Zaid"yake mai ya hana shi dawowa?

        A haka bangis ya shigo d'akin,
Fuskar nan tashi a turbune, sunkuya wa yayi daidai fuskar, salma ya sakar mata lafiyayyen Mari guda biyu hagu da dama.

Murmushin mugunta yasakar mata yace Abar kauna ta fatan kina lafiya? Samla bata ce komai ba Sai kuka da take saki.

Hannun ta da yasha zanen lalle, ya kalla had'i da kama hannun yana shafawa,

daga bisani ya wani irin murda hannun wanda yasa salma sakin wata irin gigitacciyar Kara had'i da sakin fitsarin azaba,

    Ke ni dan ubanki, ni zan dinga kiranki amma bakya d'auka? ohhhhh ni ga maloho ko ke zakiyi aurenki ki bar bangis ko?

      To kiji in fad'a miki ba zakiyi wannan auren ba, ke bazaki sake fita daga d'akin nan ba ma, ba aure kike so ba? to gaki ankawo ki gidan miji, anjima ki shirya taryar mijin ki.

Yana gama fad'in haka yaja hannun Zeema ya fice da ita. Suna fita aka rufo kofar garam.

Salma kuka ta rushe da shi gashi bata zo da wayar ta ba, yau ta shiga uku.....

Wani daki bangis suka shiga shida Zeema, kan gado yayi musu masauki, giya ya d'auko ya zuba mata Shima ya zuba suka soma sha,

A gskiya Zeema kina sona da yawa,  dariya Zeema tayi haba dai bangis dan nayi maka wannan d'an aikin shine kake ganin soyayyar ka tanada girma a guri na? Ai kawai ka bari akai gun da zaka yaba tukuna. baka ga komai ba ma tukuna....ta fad'a tana sake kwankwadar giyar, shafan ta ya shiga yi yana mai cewa wlh naji dad'i sosai da wannan aikin.

    Hhhhh bangis kenan baka da matsala.

dariya Shima yayi, suka shiga masha"ar su son rai... Inda bangis a cikin maye yashiga fad'in.... ga d'an iskan saura yin ta ma nasa ankawo min shi.... Surutai dai kala kala, wanda Zeema dama bata sha da yawa ba so taji duk abunda ya fad'a, sosai tashiga tunanin yadda zata fidda Zaid daga hannun bangis tun bai kashe shi ba.

*********
Abba"a gaskiya hankali na ya kasa kwanciya da wannan shirun na Mus"ab. bai taba yin irin wannan tafiyar ba,   Mami ta fad'a fuskar ta na sake bayyanar da damuwar ta,

                 Shiru Abba yayi daga bisani ya ce, Rukayya" na fad'a miki ki kwantar da hankalin ki mu gani zuwa gobe ko ya tsaya abujar ne gurin wani abokin sa.

   Yana zancen ne amma shi kansa hankalin sa ba a kwance yake ba, cike yake da tsantsar damuwa, dan Shima yana mamakin irin wannan abu lokacin da Mus"ab ya hawo jirgi daga Saudi ya kira ya sanar, lokacin da ya Sauka a Abuja, ya kira ya sanar da cewa zai shigo mota saboda babu jirgin da zaizo kano a lokacin.

to gashi dai har dare babu Mus"ab babu labarin shi.  ya zama dole gobe a Je har abujan dan bincika wa a Airport da guraren shiga mota.

ci gaba da rarrashin Mami yayi yana mai kwantar mata da hankali.

*******
Wlh yau salma ta dawo gidannan sai naci ubanta.... banda tana Yar iskar yarinya ace wai ta fice bata fad'a mun ba ga wannan shegen yaron ya zo Shima bansan inda yaje ba?

Rahamu ce mai wannan zancen tana zagaya d'aki kawar ta Hajiya Falmata na tausar ta gar a gane da matsala, ita kuwa sai ci gaba da hauka take... Eyee saboda Allah fa... Kai yaran nan so suke su tona mun asiri, wlh so suke su wula'kanta ni, gashi alamu sun nuna,

Aikuwa duk saina ci musu abu ta kaza... ni zasu raina wa hankali, duk sai sun gane dani suke wlh.

Wai ke Rahamu ba a baki shawara kiji ne?  sai zance d'aya kike na fad'a miki koma miye kiyi ha'kuri su dawo gidan sai kiyi, amma ynxun dan Allah mutane fa kika tara ana jin kina haya niya sai ya zama abun tsegumi, ko a cikin friends d'in mu ma. tunda ba kowa ne ke zaune da kai da zuciya d'aya ba.

to Falmata ya zanyi abune ya sha min kai, Yara suna kokarin zautar dani, kigani fa yau yakama ta ace anyi mother's day amma saboda yar banzar yarinyar nan sai bada ha'kuri nayi, wani tozarci salma keson janyo mun jikina ke bani komai na kokarin cabe mun...

Wlh bazan bari ba bazai taba yuwa ba, bazan bari ba.

Sambatun dai taci gaba da yi.

Ganin haka yasa hajiya Falmata ta fice daga d'akin tana mamakin irin wannan abu na Rahamu"tamkar idan anfasa auren shine karshen rayuwar ta.

******
Mus"ab ne ya bud'e ido a galabaice, saboda ya mugun da kuwa.

  Lallabawa yayi ya tashi zaune, 'karewa d'akin da yagan shi a ciki kallo ya shiga yi, sosai yake kallon d'akin, ina ne nan?

ya tambaya kansa, abunda ya faru ne ya shiga dawo masa, take ya baiwa kansa amsa da kidnappers ne suka d'auko shi, gaban sa ne ya shiga fad'uwa.

        Ya jima a zaune yana tunka da warwara. Ji yayi an bud'e d'akin da yake Kai kallon sa yayi ga mai shigo wa.

Wani d'an dogon saurayi ya gani wanda duba d'aya zakai masa kasan cewa d'an daba ne,, kallon Mus"ab d'in yayi daga bisani ya fita, mintina biyar da fitar sa sai ga, wani daban ya shigo.

Da wani irin kallon tsana Mutumin ya dube shi. Kafun ya soma magana.

Kai! Ya dakawa Mus"ab tsawa wacce ta razana shi.

Dubeni da kyau,, inaso kasan duk wanda ya shiga gona ta to fa baya kwashe wa lafiya.

Meye wasiyyar ka ta karshe dan kashe ka zanyi!

Wani irin duba Mus"ab d'in yayi wa mai maganar, ya ce kashe ni fa? to mai nayi muku kuka kawo ni nan?

      Ina ce kud'i kuke so? Ku fad'i ko nawa kuke so zan baku dan Allah garku kashe ni.

Ya Karasa fad'a a raunane,

Wani irin mugun naushi Mutumin ya kai Masa a baki wanda har saida bakin nasa ya fashe.

        Dan ubanka an fad'a maka tsiya da talauci ne suka sa na d'auko ka? to kasani ban d'auko ka dan aban kud'i in sake ka ba kashe ka nake son yi, a zuciye Mus"ab ya ce... Ka kasheni wai da nayi maka me?

Inace kidnapping d'ina kayi,? Ka fad'a ko nawa kakeso so nasan Abba na zai baka,

   Wani irin taka masa kafa yayi, saida ya saki Kara. Ya ce, idan ka sake mun magana akan banzan kud'in ubanka, saida yayi masa mugun kallo kafun ya ciro wata Yar karamar wuka ya yanke shi a hannu yace, to ba a nan zan yanke ka ba, wuyar sa ya nuna da wuka yace a nan zan maka aiki.

   Ficewa yayi daga d'akin. Mus"ab kam mamaki ne ya ishe shi. Waye wannan kuma mai yayi masa da har ya keson kashe shi? Bashi da amsar wannan tambayoyin dan haka ya shafawa kansa lafiya, ya shiga Jinyar bakin sa da hannun sa da aka yanka.

******
Zaid"kam tunda aka d'auke shi bai farfado ba, saboda hodar da sukai masa amfani tana da matu'kar karfi, dan haka baima San inda kansa yake ba.


******

Saboda Allah da kika roqeni yasa nayi,

My zuby😍dn hka page d'in naki ne duk yadda kika so kiyi dashi naki ne ke kad'ai 😘

        
                       

Xinnee smart 👌💋
           

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro