Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

22

💕Mamn gid'ad'o na😘💖

Masu comments, lots of love💕💖😘💋

Haka kuwa akayi, bayan sallar aka gabatar da d'aurin auren mus"ab da Rukayya" akan sadaki dubu dari daidai da kud'in Nigeria.

Inda Abba yakasance mai bayarwa sheikh abu haula yazama mai karba.

******tunda Rahamu, tasamu ta kawar da salma kusa ta sake babbaKa wa Zaid"rashin albarka da uzzura wa, yau tace ya turo mata dubu kaza gobe kaza.

Kasancewar Daddy" ya amince da Zaid fiye da tunani dan haka yake damka masa Atm d'in sa yace yaciro masa kud'i ko kuma yakai masa Bank. ga 'kadarorin sa da yasoma fayya cewa Zaid d'in.

gane hakan da Rahamu tayi ne yasa take yawan saka Zaid d'in ya bata kud'i, duk hakan bai isheta ba saida tasa shi yasoma Sato mata wasu daga cikin takardun qadarorin Alhaji!

A bangaren Zaid" abun na matu'kar da mun shi saidai bashida wani katabus anbi anbaibaye shi da zallar asiri, da aka had'a da uban tsafi, wanda kullum ake babbaka masa ba tareda sanin shi ba.

Sam yanzun Zaid baya iya yiwa Rahamu"musu, ko kad'an kullum abunda tace shi yakeyi.

A bangaren karatun sa yana matu'kar ko'karin ganin ya maida hankali dan ganin ya samu kyakyawan sakamako, bai bari damuwar rashin baby yayi tasiri a bangaren karatun sa ba Sam.

*****hajiya azumi" wankin hula fa na neman Kai ni dare!

ban gane ba!

Hmmmmmm! Hajiya azumi maganar dai d'aya ce wacce muka saba yi kullum.

garki ce mun ZANCEN yayan ki da matar sa?

Wlh kuwa zancen kenan har yanzun dai babu biyan bukata, shekaru na dad'a tafiya girma na sake kamani ga dukkan alamu dai bazan mori duniyar yadda nake so ba... ta fad'a tana sharce uban gumin da ya zubo mata a gefen fuskarta.

        ruwa azumi ta bata,

Ungo karbi ki sha, sai muyi magana.

Karba tayi saida ta shanye kaf kafun ta sauke kofin,   tasoma magana kamar mai tabin hankali,

Shekaru sama da ashirin da biyar kenan... Amma har yau... har... yau nakasa nasara a kan komai na yaya... Kullum ganinan jiya I yau, ya handame komai!

Kinfi kowa sanin kaf a cikin dangi bani da aminiya kamar ki, ke ce kawai nake fad'awa sirri na duk duniya,, kinsan komai dan wasu abubuwan kece kike dorani akai, amma dan Allah ace wai har yanzun babu wani ci gaba?

Wannan wani irin bala'i ne?

Rukayya"tabi komai ta handame yaya ba yajin zancen kowa sai na ta, kullum maganar sa Rukayya" da tilon d'an su.. ni kuma ko ohho.....

Ta karasa fad'a cike ba bakin ciki, wanda hassada ke gadarwa.

Azumi dariya tayi a zuciyar ta, daga bisani ta rungume ta tana rarrashi, daga bisani tace zasuyi magana akwai shawarar da zata bata, amma sai lokacin ai watar wa yayi... Jameela taso ta fad'a mata amma taki, a cewar ta isn't the right time.

******Mami!  ina bu'katar nutsuwar ki,

    Kallon sa tayi dan ganin yadda yayi magana cike da kamewa a muryar sa, ta kuwa San ko wace magana ce to tabbas, akwai mahimmanci a cikin ta.

Abba"inajin ka fatan dai lafiya?

A d'azu da naje gun sheikh nake masa bayani game da maganar da muka tattauna da ke jiya,

To shine yabada wata shawara wanda naso in nuna masa hakan ba mai yuwa bane, amma sai yabani wasu hujjoji wanda ni na gamsu dasu, dan haka ina fatan ke ma zaki fahimce ni kuma ki d'auka wannan rubutacce ne a cikin rayuwar mu,,  nasan ki a kullum kina jin magana ta haka kuma kina ko'karin goya mun baya a duk abunda na zo dashi wannan ma nasan baza ki 'ki ba...

take zuciyar Mami tashiga cewa to ko auren UMMIN yayi?

dan haka sheikh yabni shawarar aurawa mus"ab ummi kuma, na amince andaura auren bayan munyi sallar zuhur.

Wani numfashi Mami ta sauke,, ba tare da tace komai ba,.
bayani Abba yashiga yi mata kamar yadda sheikh d'in ya wayar masa da kai,

Sai a lokacin tasamu damar cewa... Hmmmm! ni bawai auren ba idan dan ta ummi ne nasan bata da matsala saidai shi mus"ab d'in ne gaskiya ina ganin yadda yake ma UMMIN Sam baya raga mata ina tsoro Kar ya cutar mun da yarinya...

Ta karasa fad'a a raunane.

hannun ta Abba ya kama.. Kinga Mami karki damu zanyi magana dashi insha'Allah zai karbi auren da mutunci nasani karki damu, d'ana ba shida matsala...

Babu wani nan Kai dai kana kareshi ne kawai, alhalin d'anka ko fa fara'a baya yi mata haka kullum yake treating d'in ta so hash, gaskiya ni idn haka zaiyi I don't think zan iya bar mishi ita a nan.

To idan kika tafi da ita ai sai inga yadda za'ayi ta zauna, ai hikimar yin auren kenan.

    To nidai kaja wa Zd'anka kunni.

d'ana fa bashi da matsala!

Ai dama, abba's son ina zaiyi matsala...?

dariya yayi yana cewa to zanyi masa nidai a saki fuskar.... dukan su sukayi dariya.

*****ummi"tana ci gaba da rayuwar ta a kasar Niger cikin walwala, sai damuwar ta da Allah ne kawai zai mata magani kuma ta saka ta a kasan ranta ta binne.
     
   Lokacin da Zaid ya kawo mata ziyara, ta tambaye shi game da aurenshi fad'a mata yayi, cewa ai salmar ma baisan inda take ba, shi ya dade bai ganta ba kuma uwarta bata sake zancen auren ba, ummi dad'i taji a ranta kuma tana sake yin addu'a Allah yasa ma Kar akoma tada zancen auren,
Dan fatan ta Allah ya Bawa Zaid d'in mace kamila nutsatsiya ba irin salma ba.

    A cewar ta irin salma" saidai kaddara kaddarar ma mummuna,
Wacce kuma Annabi ma yace mu nemi tsari daga mummunar kaddara, dan haka ita tana nemawa Zaid tsari da Macce irin salma.

********,
Zeema"matuka ranta ya baci kan rashin ganin salma"wanda tasan yana daga cikin shirin Rahamu"

    A binciken ta ta gano salma bata garin ma, dan haka tad'auka alwashin duk randa ta dawo sai taji komai da suke rufewa duk wani 'kullin su sai ta tarwatsa shi,

Wannan shine burin ta. Hakan ta kudurta a ranta,

Bangis ma ya neme ta dan jin ko tana da labarin salma?

fad'a masa tayi itama bata San inda take ba,

Sosai ran Bangis yabaci da salma, amma yayi alkawarin idonsa idonta, sai yaci uwarta... ko ta ina!

*****
Mus"ab! ka yarda a matsayin mu na iyayen ka ba zamu cutar da kai ba?

gyad'a kansa yayi... Yana mamakin mai yakawo wannan maganar?

Abba yaci gaba da cewa,

Mus"ab yanayin yadda ummi ta shaku da kai wanda munsani ba wai shakuwar bace a tsakaninku saidai ita tana nuna wa tamkar tasan ka, bugu da kari baza ta rayu cikin farin ciki ba a duniyar da babu Kai a ciki,, alamun da muka gani kenan wannan ne ma dalilin da yasa muka yanke wani hukunci mai girma a tsakanin ku!

Wani irin bugawa kirjin mus"ab yayi, a ransa yana mamakin wani irin hukunci ne wannan? bai gama tambayar kansa ba yaji amsa daga bakin da bazai masa 'karya ba.

Waton mus"ab mun d'aura auren ka da ummi! da fatan zakayi mana biyayya?

       Da sauri ya kalli iyayen nasa cike da tashin hankali....

Aure Abba?

' kwarai kuwa mus"ab, aure nasan Kai yaro ne mai biyayya, wanda yake jin maganar iyayen sa dan Allah mus"ab kar ka bamu kunya,,

shiru kawai yayi yana jin mahaifin na sa.

Mami ce taci gaba da cewa, ka dubi girman Allah, ka dubi maraici, ka karbi auren ummi ko dan kasamu ladan kula da marainiya, dan mu a gurinmu marainiya ce dan kuwa bamu ga uwarta ba bamu ga ubanta ba.

Na sani kana da zafin Kai, da miskilanci, dn Allah kayi ko'karin kyauta tawa wannan yarinyar, mus"ab.

Shiru dukan su sukayi, yayinda mus"ab ke jin tamkar, yayi ihu shikam an gama dashi.

Mus"ab ba kace komai ba?

Maganar Abba ce ta dawo dashi daga suman wucin gadi da yayi,

A matu'kar kasalance yace, babu abunda zance Abba face ince Allah yasa hakan shi yafi zama alkhairee.

gyad'a kai iyayen sukayi, had'i da sa masa albarka.

Mikewa yayi ya nufa d'akin sa jiki a mace.

Fad'awa yayi kan makeken gadon shi, ya shiga sauke huci tamkar wani zaki,

Sosai ransa ke sake dugun tsuma, aure? Shi d'in? kuma ma wai da wannan yarinyar?

Yazama dole yanema mafita shi da yake ta Allah Allah ya gama watannin da ya rage masa yakoma nija ya auri zabin sa,shine yanzun wannan kaddarar ta shigo rayuwar iyayen sa, yana Zaman Zaman sa gashi Za ta lalata masa Rayuwa, ko yace ma ta lalata,

Mai zai fad'awa masoyiyar sa?

Yace mata anyi masa aure?

bashi da wannan amsar abunda yasani kawai bazai iya fad'a mata anyi masa kadda rarren aure ba, har ranar da zai rabu da shi.

Ba shida wani buri a duniya sama da ya gama karatun sa ya auri zabin ransa sai gashi wannan MAYYAR"ta shigo masa Rayuwa.

Haka ya dinga saka yadda zai wahalar da baiwar Allah UMAIMAH"!

Wacce bama tasan mai yake ciki ba, taso shi a rashin dalili ko makama, tana nane masa saboda nata dalilin na shine mafarkin ta shine burin ta ko wani numfashi na ta shi d'in dai take sauke wa, komai game da shi tana duban sa a mizanin rayuwar ta, wanda idan babu shi babu ita.

       *****
Salma" ko da ta dawo hayyacin ta ganin kanta tayi a wani d'aki da bata San ina bane, sosai ta shiga firgici,

Wani d'an gajeren mutum ne ya shigo d'auke da plate d'in abinci. da bottle water,

duban sa salma tayi kanta na wani irin Sara wa.

Bai ce mata komai ba ya ajiye abincin ya fita, Salma tashi zaune tayi har yanzun mamaki na cin ranta,,

   A ranta ta shiga sake2 to ko Bangis ne ya sace ta?

Amma mai zai kawo Bangis Ghana?

Kai ba shi bane... tana cikin wannan tunanin ne wani gabjejen mutum ya shigo, baki dashi ga idanuwan sa wasu jajaye.

Zama yayi kan kujera yana duban ta, baice mata komai ba ya fito da wayar sa.

Kira d'aya biyu aka d'auka, Mika wa salma yayi.

Bata amsa ba Sai kallon sa take,

Da razananniyar Murya yace mata... Karbi mana.

Salma jiki na bari, ta karba ta kara a kunni..

Muryar da taji ne yasa ta zaro ido waje had'i da fad'in....

Mommy!

A bangaren Rahamu. Cewa tayi ke saurare ni kiji,

Ni ce nasa a boye mun ke na d'an wani lokaci, dan naga kina yunkurin tona mana asiri dake ke d'in bakisan ciwon kanki ba.

Dan haka garki sake ki ce zaki musu wani rashin kunya a gurin, dan tsab zasu gyara miki zama.

Tana fad'in haka ta kashe wayar,

Sauke wayar salma" tayi a kasalance, Lalla yau ta Kara tabbatar da shu"umancin mahaifiyar ta.

Amma dole ta nuna mata, lokacin da d'an zaki yake girma to gawurta yake yafi mahaifin sa, dan haka jira kawai Za tayi ta tabbatar da auren ta da Zaid, daga lokacin zata soma bata ciwon kai wanda bata ta'ba tunani ba.

      Kwantar da hnkalin ta tayi tahau cin abincin ta, a ranta tana ci gaba da kitsa yadda zata rama wannan abubuwan da uwarta ke mata, ta kira ta mara sanin ciwon kai, haka kuma wacce bata da amfani.. Shasha. wadannan kalmomin baza su taba goguwa a ranta ba, dan haka ma tayi alkawarin sai ta nuna wa mommyn renon da tayi ya bun'kasa.

Kuma ta kanta zai fara bi kware wa da iyawar ta a kanta zata soma gwaji.

********

Xinnee smart 💋👌

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro