Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

17

juyawa tayi dan ganin wani d'an bu'kulun ne? dan wannan damar data samu ba karamar dama bace" idonta ne yasauka kan mommyn ta" d'an tsaki tayi ta kauda Kai,
          Matsawa gun ta hajiya Rahamu" tayi cike da tarin tambayoyi ta tsurawa yar ta ido, ganin irin kallon da take mata ne yasa a' kufule tace wai mommy meye haka?

Zaki zo guri babu excuse?

Lallai Salam"kin ri'ka to dan ubanki na shigo d'in,, banda ke wawuya ce zakiyi abu irin wannan amma shine bakya rufe 'kofa? da ace kuma wani ne ya shigo bani ba kuma fa?

           mtsss"hakane kuma amma ai mantawa nayi.... duk ba wannan ba bani labari mai kika sha'ka masa. Rahamu" ta fad'a tana mai Kai duban ta gun Zaid" dake kwance tamkar mataccce,

               Kwalbar Salma"tanuna mata, d'auka Rahamu"  a ranta tana jinjina iskancin yar ta wai har tasan dabarar da zatayi wa namiji fyad'e?  Lallai komai na mutanen zamani daban ne ita lokacin da tayi tashen iskancin ta ina tasan wani ayiwa namiji fyad'e? Kawar da wannan tunanin tayi,, tace salma"zo muje side d'ina muyi magana... Wani kallon ban gane ba salma tayi mata,  cikin taushi Rahamu tace maganar tana da mahimmanci ne, kuma akan Zaid" ne.

  Jin hakan yasa tace Jeki ina zuwa!

Batyi musu ba tafice daga d'akin, salma"gyarawa tayi had'i da sumbatar goshin sa kafun ta fice....

********yau ce ranar tafiyar su zuwa kasar Saudi" dan haka tun asuba hajiya Rukayya bata zauna ba Sai faman kaiwa da kawowa takeyi dan ko'karin ganin ta tafi da duk wani abu da ya kamata..

Alhaji farouq" ne yakara wayar sa a kunni da alamu Kira yake, sai da yakira kusan sau uku kafun a d'auka,, sallama yyi bayan yaji an d'auka.

Daga d'aya bangaren a kace yi ha'kuri Yaya ka kirani ina kitchen wayar tana parlour, murmushi yayi yace Amina ta bata laifi ftn kin tashi lfy da yaran gaba d'aya,?

Lfy qlu Yaya' yawwa Masha'Allah, dama kira nayi in sanar dake zamuje saudiyya check-up, a sanyaye tace Yaya badai jikin maman MUS"AB bane ko?

Dan murmushi yayi mai cike da kaunar kanwar tasan saboda yadda take kaunar iyalinsa yana matu'kar jin dad'in hakan.

A a Amina ba Jikinta bane, Zadai muke ne dan sake tabbatar da lafiyar ta. to Yaya Allah ya tsare gashi baka fad'amun da wuri ba da nazo sallama, dariya yyi bbu komai Amina.

Kiyi Zaman ki, to Yaya adawo lafiya ka gaida mamn MUS"AB d'in.

to zataji!

Katse wayar yayi yana murmushi,  a haka hajiya Rukayya ta same shi hannunta d'auke da traya wanda ke d'auke da mug d'in kunun gyad'a,  sai chicken pepper soup wanda yaji kayan yaji da dnkali, sai kamshi yake yi.

Zama tayi ta ajiye tray d'in akan center rough d'in dake palan.

to Abba" ga kayan break d'in fa.
Yawwa"sannu yar aljanna ta, nagode... Murmushi tayi wanda saida ushiryar ta ta fito har saida yaji gabansa ya fad'i dan ganin da wacce tai masa kama, take kuma ya kauda tunanin gefe d'aya.
Yashiga yin breakfast d'insa.

Ita kuwa tafiya tayi gun baby dan bata nata abincin,, a zaune ta ganta hannun ta ri'ke da gashin ta tana wasa dashi... Murmushi Mami ta sakar mata dan haka kawai take jin kaunar yarinyar,

Itama baby murmushin tai mata kamar yadda taga tayi, ajiye tray d'in hannun ta.

Isa tayi kusa da baby, ta shafa kanta had'i da fad'in gud Morning beautiful angel, tana fad'a ne tana dariya, itama baby dariya tayi.

Nan ta sauko da ita daga gadon tasoma bata abinci.. Saida ta tabbatar ta koshi ta karasa shirya ta itama ta shiga kimtsa wa dan lokacin tafiyar na gabatowa.

*********Inna"lillahi wa'inna ilaihim"raji'un, Allah'humma inni a'uzu bika min'sharri ma, ra'a fil'manami, an'yaddurani,fi deeni"wa duniya'ya. Shine abunda ummi"take ta fad'a tunda ta farka daga mummunan mafarkin da tayi (wannan addu"ar itace akeso mutum yayi a duk lokacin da yayi mummunan mafarki,..... Fassarar addu'ar shine... Ya Allah ina neman tsarinka daga abunda nagani a cikin bacci na, gar ya cutar dani a cikin addini na da kuma duniya ta. bayan mutum ya karanta sai yayi tofi sau uku a hannun hagunsa ya kuma sake sauya kwanciya daga yadda yake da, Allah yasa mu dace ameen.)

           Sosai take gumi, saboda mafarkin ya razana ta, Baby taji tana kwala mata kira l,, Koda ta waiga sai taga ita d'in ce dai, mamaki tayi ganin ta cikin shiga ta alfarma tayi kyau sosai... tana shirin isa gareta tace nifa ummi tafiya zanyi garki wani ce sai kin biyoni, ki zauna cikin aminci byee_byee tashiga d'agawa uwar hannu,, da sauri UMMIN ta zabura tana cewa ke garki tafi tsaya inzo tana ko'karin cimma babyn wani mutum da fuskar sa ke rufe yashiga tsakanin su, ya da'bawa babyn wu'ka shine fa ummi tayi salati da 'karfi... daga nan ta farka,,

Gumin taci gaba da gogewa kafun ta Mike ta shiga toilet"alwala tayi tashiga jera nafila.


**********Salma" shin kinason ZAID"da gaske?

Kallon rainin hankali tayi wa uwar  kafun tace bnason sa nake wahala a kansa? Ji mommyn nan fa?

Murmushin takaici Rahamu"tayi a ranta tace kema a sannu zanci ubanki Shegiya yar gadon mugun Hali (ikon Allah jama'a 😂Yo naga a gunta ta gada meye na zaginta?)

Salma" kinsan dai so baya 'kar'ko babu yayan banki ko?  bata amsa ba Sai kallon ta take.
Inaso ki tuna cewa ZAID"ba d'an gidan nan bane, d'an cin arziki ne dan ko yau Alhaji ya mutu babu abunda Zaid zai samu.

"dan haka nakeson mu had'a Kai mu samu mu yagi Rabon mu, dan kinsan Alhaji ba karamun mai arziqi bane, kuma Nima idan ya mutu tumin takaba za'a bani kawai , ina Fata kina gane mai nake cewa.
Salma" ta dubi uwarta tace kuma mommy da gaskiyar ki,

Murmushin samun nasara Rahamu"tayi kafun ta cigaba da cewa, yawwa nayi magana da boka yace Zaid ne kawai zai iya kwaso mana dukiyar Alhaji, amma yanason aje da Zaid d'in gurin shi, daga nan sai yasa masa asirin da zai aureki,

Da gaske mommy?

Gyad'a Kai Rahamu"tayi tace ina wasa ne?
A a mommy to mai muke jira mukai shi tunda baya hayyacin sa.

Murmushin takaici tayi kafun tace, kedai salma Sam bakida wayau wlh shikenan, sai mu kwashe shi sakaka mukai Ghana da yake gana nan da suleja ce ko?

Mtsss ni bnason shirme, Kinga ne?

Ta gyad'a Kai,, to abunda nakeso dake wannan maganar sirri ce dagani sai ke kuma ma ai dan ke nake wannan ya kin, dan haka ban amince inji maganar ko a gurin zeema ba. Ai kin fahimta?

Eh mommy, babu wanda Zaiji,, ina wannan abun shaken? bata tayi, tace yawwa, kingane?

Kije kici gaba da harkokin ki zan San yadda zanyi, cike da murna salma tace to mommy"

Bayan fitan ta hajiya Rahamu" tace Kai yaro yaro ne, ita ta yarda wai Dan ita nake fighting... Hhhhhh ta bushe da dariya tace wlh ko ke sai in bada ki dan biyan bu'kata ta

******
Sun isa Saudi lafiya, inda suka Sauka a Riyadh,,
'D'an su tilo guda d'aya bugawar zuciyar ko wannen su, shine yazo tarbar su a Airport,, sosai farin ciki yakasa boyuwa akan fuskokin su, Shima yana ganin iyayen nasa ykasa boye farin cikin sa, dukan su ya rungume kyakyawar runguma,,

dariya sukayi su duka Mami ce tasoma cewa, Bubun Mami baya girma ko? gaba d'aya suka sake saka dariya kwa'be baki yayi yace Mami! har yanzun?

Har gobe... ta bashi amsa tana dariya.

Baby dake gefen Mami batasan mai ke faruwa ba ita dai ganin an rungume kowa ba'a rungume ta ba Sai kawai ta kutsa tsakiya wanda sai lokacin suka tuna da ita dukan su, shikam MUS"AB kallon mamaki yabita dashi, a ransa yace... ta cika kyau!

Bai gama mamakin wacece ita da kyanta ba yaji tayi masa kyakyawar runguma wacce yaji ta har ransa,,

Su Mami kam dariya sukayi cike da tausaya wa... Abba"ne ya za meta daga jikin MUS"AB d'in. Yana dariya...mus"ab nason sanin wacece ita kuma daga ina meye had'in mamin sa da abban sa da ita? Saidai shi mutum ne wanda baya son magana, gashi da zafi, Sam baya son raini shi yasa kullum dariyar sa a iya murmushi take mutum uku ne kawai mutanen da ke ganin hakwaran sa a filin Allah yayin dariya,

Iyayen sa, da kuma muradin ransa!

d'unguma sukayi zuwa mota dan nufar gida.

*******

💕✌️🙏😢

Xinnee smart 👌💋

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro