Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

16

da sauri ta 'karasa gunda baby take'kudun dune cikin ruwan wankan da aka had'a mata sai zaran ido take,, sosai hankalin Mami yatashi, a ranta tashiga lissafin anya kuwa yarinyar nan lafiyar ta 'kalau kuwa?d'ago ta tayi daga cikin Rowan,

baby kam tana ganin tafito cikin ruwan  ta fashe da kuka, da sauri ammi ta rungumeta a jikin ta, cikin tunanin da yayiwa zuciyar ta katutu, taja hannun baby suka fita daga bathroom d'in.

cire mata kaya tashiga yi, ganin yarinyar Sam babu abunda zata iya yiwa kanta ga dukkan alamu.
Saida ta cire mata kayan ta saka towel ta goge mata jikin ta, zaunar da ita tayi bakin gado, ta fita. Kitchen taje ta had'o mata breakfast, tea, cheaps and liver paper soup, ta had'o su kan tray ta kawo mata,
         
             Wani d'an stool ta janyo ta d'ora tray d'in a Kai tasoma bata abincin a baki take baby ta shiga amsa da sauri da sauri, dan ba karamar yunwa taji ba, ido kawai Mami ta zuba mata cike da tausaya wa, saida ta koshi ta daina amsa, hakan yanuna wa Mami ta koshi.  towel tasa ta goge mata baki ta kwashi kayan zuwa kitchen, anan tasamu Indo mai aikin ta d'auke da kaya, tana ganin ta tace, yawwa hajiya ga sa'konki inji amadu yace in baki.
                      Karba tayi... Nagode indo tafad'a tana ko'karin fita daga kitchen d'in.

Bedroom d'inta takoma, bud'e ledar kayan tayi tashiga dubawa, murmushi tayi ganin ansamu duk abunda ta rubuta, take tashiga shirya baby cikin wata doguwar riga Yar madina.

          Taje mata kanta tayi, ita kam baby sai kallon ta takeyi, kamar taga wata halitta.

       hannunta ta rike suka nufa side d'in Alhaji'farouq.   a zaune yake yana kallon tashar aljazeera" ganin su yasa ya maida hankali kansu,   zaunar da baby Mami tayi kan d'aya daga cikin kujerun parlour, guri tasamu kusa da mai gidan nata ta zauna, murmushi suka sakar wa juna cike da kulawa tace Daddy"ga yar taka fa... Wanda fad'ar hakan da tayi saida gabanta yayi wani irin bugawa.

                      Fad'ada murmushin sa yayi, kafun yace... Masha'Allah" fatan ta tashi lafiya, duban inda baby take Mami tayi, cike da damuwa ta zuba mata ido ganin sai faman wasa da abubuwa takeyi tamkar wata Yar 5years wanda tasan a kiyasi yarinyar zatayi 17years. Amma sai dabi'ar Yara takeyi.
duban Alhaji farouq tayi, wanda Shima ita yake duba, cikin taushin Murya tace.. Abba"! Yarka fa ina ganin sai mun dangana da hospital"  dan ga dukkan alamu bata lafiya.
Cikin nuna rashin fahimta yace bangane ba!

Ina nufin yarinyar kamar bata da lafiya ka duba kaga yadda take halayyar Yara kananu, kuma ma da da lafiyar ta ai da muka shigo nasan da ta gaishe ka, kuma haka jiya tadinga yin wasu abubuwa, nan tashiga bashi labari har zuwa yau da tayi kwanciyar ta cikin ruwa... Inna"lillahi wa'inna ilaihim"raji'un!
Haka Alhaji'farouq yashiga maimaita wa cike da damuwa. da tausayin yarinyar mai tsanani, idanu ya zuba mata cikin tausayawa, daga bisani ya maida duban sa ga matar tasa..... yace.. Ya kike ganin za"ayi?

To nidai ina ganin kawai mukai ta asibiti likitoci ne zasu fad'a mana meye matsalar ai..

Hakane,, to ni a ganina tunda a 'karshen shekarar nan zakije Saudi check-up kawai sai mu bari idan zamu tafi sai muje da ita kuma nima sai inyi hutu na a can tunda manager na nan ya kula da harkokin company,wani murmushin dad'i hajiya Rukayya"tayi kafun tace kaga kenan MUS'AB" Zaiji dad'i matu'kar ya ganmu gaba d'aya... Murmushin Shima yayi had'i da rungume matar tasa suna ci gaba da firan tilon d'an nasu... Basu Ankara ba sukaji ihunn baby.......

***********
Hajiya Rahamu"gadan gadan ta nufa sashen ummi"  matu'kar iyayen suka gani to duk asirin jikin su zai karye... Ki kula! Ki kul! Ki kul!...... Sautin maganar boka ce tashiga dawo mata,, da sauri ta jingina da kofar side d'in ummi, tana sauke wahalallen numfashi,
Ita kam ta bonu da wannan bala'in ina zata saka ranta,.....

Wannan ba lokacin Karaya bane...  bai kamata ki soma damuwa tun yanzun ba...garki damu da damuwar kowa kiji da kanki duk wanda yace zai bata miki shiri to garki barshi......zuciyar ta ce mai mata wannan hud'u ba.

Da sauri ta juya kamar kububuwa takoma side d'inta.. Cike da dakakkiyar zuciya tashiga saka da warwara, 

******
Daddy"ina matu'kar jin tausayin yaron nan Zaid" hakika shi mai kaunar baby tsakani da Allah ne. bana son rayuwar sa tashiga hadari saboda baby, ta karasa fad'a da karyayyar Murya tamkar mai shirin fashewa da kuka,
"Numfshi Alhaji Tahir yuguda" ya sauke cikin damuwa, Shima yashiga cewa...  Wannan gaskiya ne ummi" Zaid mai son mune tsakani da Allah, ni yanzun burina ya kwantar da hankalin sa, dan karatun shi Bana wasa bane, dole sai ya mayar da hankali,, saboda son da yakewa Yar mu ne ma yasa nake sake jin in taimaka masa, dan nan gaba bansan yadda Allah zaiyi ba, baby kuma idan Rabon mu ce... Allah ya bayyana mana ita cikin aminci...

Amin ummi ta amsa tana mai sauke hawayen bakinciki.lallashin ta yashiga yi cikin tausaya wa kansu.

********beb wlh na matsu inkoma ko dan in ai watar da nufi na, cewar salma, wacce ke zu'kar shisha, tana fesar wa,

   Hhhhhhhh"zeema ta fashe da muguwar dariya, tace Kai Sal baby.. Wlh kekam narasa mai yasa kike tsoron bangis har haka, kawai hajiya ki gudu kije samu sabon flower ki kibata ruwa, kin wani tsaya gun bangis wanda yake tsohon kwanu mtsss d nice da yanzun tuni an wuce gurin,, ta'karasa fad'a tana sake kaiwa tabar hannunta zu'ka.
duban ta salma tayi da jajayen idanuwan ta,

Zeema"bazaki gane bane,, zeema bata dubeta ba Sai Jakarta da ta janyo, wata yar kwalba ce ta ciro kamar ta turare jijjiga kwalbar tayi kafun tace Kinga wannan? Salma bata amsa mata ba Sai jajayen idanunta da ta zuba mata,
 
    Murmushi zeema"tayi kafun taci gaba da cewa... Idan kika fesawa mutum wannan sai ya kwana ya wuni yana zuba bacci baima San inda kansa yake ba,   idan kinason yayi miki aiki da yawa to ki feshe d'an karamun kyalle dashi ki bursunawa mutum a hanci.

Saida ta saki fito kafun tace,, shikenan, kici Karen ki babu babbaka. ta karasa fad'a tana wani ware hannu irin na yan duniya.

kamo hannun salma" tayi ta dam'ka mata kwalbar, enjoy my darling friend, takarasa fad'a tana sha'ka cocaine...

*******sub'hanallah..... Yanke wa tayi fa Alhaji kagani jini sai zuba yakeyi mukai ta asibiti hajiya Rukayya"ta fad'a a rud'e dan ganin yadda baby ke kwaza ihu tamkar wacce ake cirewa ido, ga kuma yadda jini ke tarara,

    A nutse Alhaji yashiga duba dame ma ta yanke, idonsa ne yasauka akan key holder d'in motar sa, wanda yake had'e da Yar karamar aska, saidai tana da murfi...

      d'auke key holder d'in yayi yanufa bedroom d'insa wani d'an karamun tile yasamu ya kwashe jinin dake jikin key holder d'in,  ya mayar ya 'boye.

First aid box d'insa ya d'auko, Koda yazo yasamu Mami rungume da baby da sai faman ihun kuka take, itama mamin kamar zata fashe da kuka ganin yadda fuskarta ta sauya.

ga dariya ga tausayi!

Cikin rarrashi da kulawa yashiga wanke yankan wanda ba wani yanka bane jini ne dai yake zuba da yawa, nan yasa mata a iodine, ya nannad'e gurin da bandage...
Baby ansha kuka har angode Allah sai faman ajiyar zuciya take,  rungume ta Mami tayi, tana taping bayan ta, take tasoma bacci mai cike da shesheka,

duban su Abba"yayi suka had'a ido suka saukewa juna murmushi.

********
Zaid" dukan mu musulmi ne kuma cikar musulunci shine imani da qaddara.
Haka ne?
gyad'a Kai Zaid yayi zuciyar sa Sam babu dad'i, Daddy"yaci gaba da cewa... dan haka Zaid ina mai baka shawara da ka dangana da bata baby muyita addu'a har Allah ya bayyana ta. Inaso kasaka wa zuciyar ka ruwan sanyi ka koma makaranta ka fuskanci karatun ka.

Ummi"ta d'ora da fad'in... Zaid gaskiya Daddy"ya fad'a maka a du duniya karatun nan shine kawai gatan ka,  Zaid Allah ne ybamu baby kuma shine ya jarabce mu da 'batan ta, Zaid mu daga hannu mu gode mishi, domin yafi mu son baby, kuma yafimu sanin abunda yadace da rayuwar mu da ta baby. Zaid mu iya jarabawar mu kenan fa.

Wasu na nan tasu jarabawar tafi wacce muke cike.. Nunkin banunkin, kuma sunyi ha'kuri sunyi ta wakkali, to mu dan meye baza muyi ba?

Allah ne fa da kansa yace duk wanda yayi tawakkali dani to na isheshi, shin mu Bama so ne Allah ya ishemu?

A karye taci gaba da cewa... Zaid idan dai har na isa da kai Zaid" to na ro'keka da ka kayi ha'kuri ka maida hankali kan karatun ka, nidai na bari ga Allah Allah yayi mana mafita da muwa'faqah.

Tana kaiwa nan hawaye yasauko mata tasa tissue ta shiga sharewa, shikam Zaid dama tunda tasoma magana yake zubar da hawaye, Daddy"ma tuni zuciyar sa ta karye har baisan lokacin da yaji hawaye ba saidai yayi saurin sharewa dan Kar su Kani.

*****
Yawwa" Mami ina Fata kingama shirya muku komai da komai? Insha'Allah mun gama shirinmu har kayan ka duk na had'a.

To Masha'Allah, sai kuyi ko'karin tashi da wuri dan 8 zamu tashi da yardar Allah.

Toh Allah yakaimu,

Amin"
d'an zo ni kimun tausa, ya fad'a yana cire hular kansa dan dama daga company yake, murmushi tayi, had'i da fad'in to bari inkawo maka furar ka yadda zaka fi jin dad'in tausar anayi kana shan fura, dariya yayi had'i da fad'in wayau manya Rukayya, anmata,.. dariya tayi had'i da girgiza kanta, ta fita zuwa kawo masa furar.

********Rahamu"dama d'aya ce ta rage miki matu'kar kinason ayi nasara to fa, saidai ayi abu d'aya!

Meye shi boka? Fad'amun ko meye..

Tsafi!

Tsafin ma na Kai tsaye.

Boka na amince matu'kar bu'kata ta zata biya ayi Tsafin na yarda, bawai yardar ba Rahamu" matakan.

Meye matakan?

Mataki na farko... Dole azo da zaidu nan dan yadda Tsafin zai kasantu kenan.

Sauran sharud'an idan kinzo kyaji, d'ib, boka ya kashe wayar sa.

Numfashi ta sauke,  to Yaya za'ayi ta kaiwa boka Zaid" itakam taga ta kanta komai na ko'karin ca'be mata.. Gumi tashiga yi kota ina har a tafin 'kafar ta...

******Salma na ganin bangis yafita, ta duba agogo'karfe d'aya na dare ne, ko ba'a fad'a mata ba tasan operation suka fita, yau kuma wani gidan watan kukan su ya tsaya(Allah ka shirye mu)

Wayar ta ta d'auko kiran zeema"tashiga yi, da kyar ta d'auka.
Ke zeema akwai mota hannunki?

Eh yahdai? So nake kizo ki kaini gida nasamu shegen yafice sana'a.
OK gani zuwa,

Cikin daren zeema ta sauke salma bakin gate d'in gidan su takira layin mahaifiyar ta ta bud'e mata gate zeema kuwa cikin daren takoma gida, dan ita bata damuwa da dare dan tasaba zuwa club 3dare ta tafi gida, gashi gidan nasu uwa ba kwaba ne,, dan baban su ba mazauni bane haka kuma uwarsu,, itama barikin ta baiwa gaba dan Alhaji Ashiru sai yayi wata 8 bai zo gida ba saidai ya turo da kud'i... Ga yayanshi duk mata ne dn zeema itace ta hud'u sai karamar su zarah itace ta5  sauran biyu sunyi aure yayinda d'ayar itama irin rayuwar zeema take ita bata ma zama a gidan, duk cikinsu zarah ce kawai mai hankali dn idan kaga yadda take wa uwar nasiha tana kuka abun tausayi, wataran da ta fara taka mata ta bata Kashi haka kuma bata fasawa kullum cikin gayawa zeema da uwarsu gaskiya take saidai su ina.. Sunyi nisa.

Salma tana shiga gida ta shige d'akin ta ta fad'a gado, bata tsaya amsa tarin Tambayoyin da Rahamu take mata ba.

Rahamu zaginta tashiga yi, had'i da la'antar ta dn rashin sanin ciwon kai.

(Allah y kyauta)

******
A duniya babu abunda yakai bakin cikin zuciya radadi musamman na rashi rashin ma na masoyi masoyin ma irin baby, tabbas Zaid"ya shaida hakan, babbu shakka so babu nasara abu ne mai rada d'in ciwo wanda zuciya bata jurewa gangar jiki baya d'auka baki baya iya furtawa, haka kuma kwakwalwa kan iya fad'awa cikin rashin saiti Koda kuwa na wucin gadi ne,

  A bangaren Zaid"duk wannan abun jinsa yake tamkar ba a duniyar da yasaba numfashi yake ba, jin sa yake tamkar yanzun yana Rayuwa ne a duniya mai d'auke da garwashin wuta mai tiriri, har yakan ji cewa da haka so zai zo masa a hagunce babu nasa shikam da bai ziyarce shi ba domin bai amfana da komai a cikin sa ba Sai tsantsar damuwa da farga ba, 

Yaso baby yana kan son ta, yaso Rayuwa da ita, saidai ita kaddara abace da kan zowa mutum ba tare da shawara dashi ba,  gashi tazo lokaci d'aya ta rushe masa dukkan wani tanadi, a da kafun haduwar sa da baby ya yanke tsammanin Rayuwa mai armashi saidai ayita yi kawai,

Sai gashi shigowar baby rayuwar sa ta samar wa zuciyar sa sukuni, ba iya na zuciya kawai ba hatta da na ababen more Rayuwa baby ta bashi,   sai gashi lokaci d'aya mummunar kaddara mara dad'in suna tazo ta wargaza tanadin sa,

Ba haka yaso ba!

Saidai.. KANA NAKA ALLAH NA NASHI

Wani juyin yasake yi kan gadon sa, cike da muguwar damuwa,, ganin tunani ba shine mafita ba yasa ya shige toilet ya d'aura alwala, ya soma nafil'fili yana mai Kai kukan sa ga ubangijin talikai.

******karfe hud'u na yammar ranar asabar, salma tanufi d'akin Zaid" dan aiwatar da mummunan 'kudirin ta,

     Sanye take da riga da wando, fuskar nan taji bleaching har ta gode Allah. Kannan yasha uban attach, sai zuba kam shi take.

Hannunta ri'ke da kwalbar ta, da d'an handkerchief,

Knocking tayi a kofar parlour, shiru har sau uku ba'a bud'e ba, hakan yasa ta tura ta shiga... Shiru parlourn babu kowa dan haka ta kutsa Kai bedroom d'in, hango shi tayi a kwance yana bacci lullube da duvet......

Shikuwa Zaid"bayan sallar azhar ne, ummi ta shigo dan kawo masa abincin sa tasameshi yana fama da ciwon kai saboda rashin bacci ga damuwa, hakan yasa tasa shi yaci abincin, taje ta kawo masa magani a ciki ne ta had'a masa da maganin bacci... tasashi yaje ya kwanta ta rufe shi saboda Ac.

Murmushin mugunta,, salma"tayi....saida ta 'karewa Kyakyawar innocent face d'in sa kallo kafun ta fesa turaren ta, ta sussun suna masa a hanci, d'an motsi yayi kafun jikin sayasaki gaba d'aya,, dariya tayi ta bosawa,, hayewa tayi kan bed d'in tayaye duvet d'in,   fuskar sa ta shiga shafawa tana lasar baki kamar mayya,,

Haka tadinga bin sassan jikin sa tana shafawa, Fuskarta d'auke da murmushin ganin banza.

Bakinsu take ko'karin had'awa..... Taji anyi gyaran Murya uhhhmmm...

Gabanta ne yayi muguwar fad'uwa!


Bbu editing kuyi sorry 🙏

Thank you all for the prayers I do appreciate 😍

Gskiya to vote da comment d'inku yana mun kad'an 😢idn bakwa jin dad'in buk d'in ne please let me know.... So that indaina wahala 😖

Xinnee smart ✌️😘


Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro