Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

10

This is for you beb "(SURAYYAHMS) 😂🤣u made me laugh today 😂😂,, can't express how much happy I am, I just pray for you that may God make u happy more than the way you made me,
Ina kuma tayaki murnar fitowa d kyakyawan sakamako
All the best 🤝🏻 💕💋💕🙏

Wani irin murmushin farinciki, salma"tayi,,dan bata d'auka mommyn zata amince da wuri haka ba, shi yasa taji wani farinciki,

Yayinda hajiya Rahamu"  tashiga kitsa nata tunanin zuwa lokacin da zata tabbatar dashi, tabbas akwai amfanin da salma zatai mata wannan karon Sam ba zatayi wasa da damar ta, dole burinta yacika!

*****
Salma gani d'aya taiwa zaid taji tana 'kaunar sa, wanda hakan baya rasa nasaba da kyan fuskar sa da kyan kyakyawan'kirar jikinsa, dan zaid akwai Kira mai kyau duk da ba wani babba bane dan a yanzun bai fi shekaru 25 ba,, salmar ma ta girme shi da shekara 1.
Saidai saboda yanayin siran tar ta bazaka ce ta girme shi ba dan siririya ce sosai, tanada doguwar fuska da dogon hanci saidai baka ce wanda bata godewa Allah da kalar da yabata ba saida tashiga cikin jerin marasa godiyar Allah ta hanyar shafa man kanti dan haka ma bazaka ce mata baka ba saidai kanayin tozali da 'kafar ta zaka sheda hakan dan sosai kafar ta takeda baki duk da irin kashe mata kud'i  da take na mayukan dake haska bakar kafa, saidai kafar sam taki karbar hasken.

Wannan kenan!

Rayuwar Zaid" a gidan Alhaji Tahir yuguda"  rayuwa ce mai tattare da tsantsar farinciki da sakewa wanda zai iya cewa sai yanzun ne yake rayuwar freedom dan idan ya had'a da rayuwar da yayi a baya tabbas waccan zai iya sata a rayuwar bauta!

Sosai yake girmama ummi yake bata matsayin mahaifiya dan ko babu komai ta cancanci wannan matsayin, dan ita d'in mace ce mai saukin Kai fara'a mutumci da tausayi tunda yazo gidan take ko'karin sakewa dashi had'i da bashi wani gurbi na musamman a cikin gurbin da uwa kan baiwa d'an ta.

Wannan alkhairee nata yana dad'a saka shi jin a duniya bashi da iyaye sama dasu domin Alhaji Tahir ma, haka yake masa yana ko'karin bashi ha'k'kin sa na matsayin da a gunshi,, dan tuni yasa aka gyra masa sashen da a da yake matsayin na Khaleel.

Yake zaune a ciki haka ma, bangaren sitirru saida aka tabbar da an sha'ke clothes set d'insa da kaya na alfarma.

A bangaren karatun sa ma, tuni ya rubuta jamb, inda yasamu shiga jami"ar Abuja... A inda yasoma karantar liktanci,,

Shakuwar sa da UMAIMAH"kuwa sai abunda yaci gaba, dan haka Zaid"  bashida matsala a gidan hatta hajiya Rahamu"  bata nuna masa komai,

Saboda shirin ta da Allah ne kawai yasani, saidai shi Zaid yakasa yarda da ita wanda shi kansa yarasa dalilin rashin yardar.

*****
Zaune yake a garden d'in gidan yana duba takar dunsa dan kullum haka yake matu'kar yadawo makaranta d wuri, sanye yake da riga da wando na kaftan, wanda suke kalar ruwan madara d'inkin gajeren d'inki ne, sosai kayan sukayi kyau a jikinsa kansa yasha askin saisaye, wanda babu gashi kuma ba tas aka kwashe kan ba.
hannun sa kuwa daure da agogon azurfa, mai kyau da tsada sai takalman sa budadu masu kalar brown.

a kasa yake zaune kan carpet, yayinda baby take daga gefen shi a zaune itama tasha kwalliyar ta cikin doguwar riga mai sirrin hannu, rigar kalar coffee ce dan haka tadace da kalar kyakyawan fatar jikin ta. Kanta babu d'an kwali dan haka ma dogon gashin ta yake a bayyane,, wanda akaiwa kitson Kalba da suka kwanta a gadon bayan ta,, kunnenta d'auke yake da d'an karamun eye rings.

Wasa take da ci yayin dake gurin tamkar 'karamar yarinya,, wanda a lokacin kamata yayi tana ajin islamiyya,, saboda yammaci ne,

Saidai dalilin lalura gata a zaune tana wasan da yan shekaru uku hud'u ne yakamata suyi bawai ita da a yanzun take da shekaru 14 ba.
Zaid ne yake wannan tunanin yayinda yake dubanta,, cike da tausaiya wa, wani murmushi ne yasu'buce masa lokacin da yaga itama tanayin murmushin wanda baisan dalilin yinsa ba kawai ya tsinci kansa da taya ta murmushin.

ajiye takardun hannunsa yayi"matsawa yayi zuwa gare ta, a hankali yakama hannunta dan ta tsayar da wasan.

d'ago da Fuskarta tayi ta dubeshi. kallon juna suka shiga yi na yan seconds kafun yace... bakya gajiya da wasa ne?

Bata amsa shi ba Sai rawan da kanta keyi. a hankali yace.. Mai yasa bakya son d'an kwali? Ummi"  tace... idan tasaka miki sai ki cire, uhmm mai yasa? ita dai kallon sa kawai take. Cigaba da kallon idonta yayi.. bakisan babu kyau zama babu d'an kwali ba? kinason mukeyin fad'a ne? langwa'bar da kai tayi yana cigaba da rawa rawa, had'i da bata fuska, murmushi yayi a ransa dan ya fahimci bataso kenan tunda tayi hakan, dan a Zaman su duk motsin da tayi a duniya yakan gane mai take nufi hakama idan ciwon ta zai tashi matu'kar yana guri yana saurin fahimta shi yasa yana ganin yana yinta zai fara mata addu'a cikin ikon Allah kuma ciwon baya tashi, shi yasa tunda yadawo gidan ciwon ta bai cika tashi ba har mamaki ummi take dan da kusan kullum sai ciwon ya bugeta.

Shafa fuskarta yayi yana murmushi, yace OK bataso muke fad'a ko?
to tadaina zama babu d'an kwali ta dinga sakawa,
     da saurin ta taja yar gajerar rigarsa ta shige ciki... Wata irin dariya ce tazo mai bai San lokacin da yadara ba,, sosai yake dariya itama dariyar take saidai mara sauti sai bakinta da take budewa alamar dariyar take itama.
Suna cikin haka, yaji ance Zaid!

a d'an tsorace ya juya dan ganin waye mai kiransa haka, tozali yayi da salma wacce take cikin shigar wasu riga da wando da suka kama Jikinta sosai gwanin tausayi dan sai tayi babu tsari a cikinsu ga kanan yasha uban gashin doki,, mai color biyu black and brown.

ta"awizi yayi a zuciyarsa,, kafun yadaure fuskar sa dan ya fahimci yadda kwanan take yawan cusa kanta a gunsa wanda da tasan yadda yake 'kyamar ta da bata dinga masa shisshigi ba.
Cike da kwarkwasa ta isa gareshi had'i da zama dab dashi,, baby dake gefensa dukar da kanta tayi tamkar bata gurin,,
Zaid"  magana nakeso muyi please?

Kallonta yayi kafun ya d'auke kansa,, yace.. Ina jinki!
d'an shiru tayi daga bisani tasoma magana,, Zaid"  a gskiya am in love....

Wani 'kazamin kallo yabita dashi daga Samanta har 'kasa kafun yace... Idan bakida abun cewa ni inada abunyi,,

Cike da jin haushin kalaman sa, tashiga cewa, bngane ba,, saboda Allah so kake kace baka fahimce ni ba? Ko kuma so kake kace baka sona?
Kalle ni da kyau maza ire iren ka da suke kawomun hari Allah ne yayi yawa dasu Bana kulasu sai Kai ne zaka dinga wani jamun aji....  to nagama magana ina sonka kuma sai ka aureni either u like it or not u most marring me, period nagama magana,,

Mikewa tayi da zummar tafiya taji an fyad'o 'kafara timmm kake ji,, ta fad'i a 'kasa,, kafun tayi yunkurin tashi taji wata irin muguwar shaka.

Wani mugun ihu tasaka na neman d'auki da sauri Zaid yayi gunsu dan janye baby daga kan salma.

Saidai tamkar wani sinadarin 'karfin aka saka a jikin babyn,, tsabar rudewar da yayi ma bakinsa yakasa furta ko addu'a d'aya shidai burinsa ya Raba salma da baby dn yasan matu'kar wani abun yafaru tabbas bazai fita ba. Sake daddage wa yayi yaci gaba da kokar rabasu...

Baby kam duk inda tasamu a jikin salma yaga take yayinda salma sai ihu take,, wanda ihun nata ne yajanyo hankalin ma"aikatan gidan. Aikuwa da sauri suka zo gurin dan ganin maike faruwa..

Ganin abunda yake faruwa ne yasa mazan sukayi saurin taya Zaid rabasu. Allah ytaimaka aka 'kwaci salma a jikin baby da 'kyar..  tuni salma ta fita hayyacin ta dan duk Fuskarta ta lalace ga uban sundumewa da bakinta yayi.. a takaice dai tasha one block seven die 😂lol

Da sauri hajiya Rahamu"tayi kan salma tana ihun an kashe mata ya bazata yarda ba.

ranga ranga,, aka kwashi salma sai clinic.

Baby kam ana janye salma tayi shiru had'i da sunkuyar da kanta.. ko Fuskarta baka gani saboda gahin ta da yabar bazu ya rufe mata fuska.

bayan kowa ya watse yarage daga shi sai ita... Kasancewar ummi bata nan taje asibiti ganin likita..

a hankali ya isa gurinta, zama yayi a gabanta zuciyar sa na d'an bugu a hankali,, a sanyaye yasa hannu ya yaye gashin da ya rufe mata fuska,, d'ago da kanta tayi ta dubeshi da jajayen idanuwan ta, dasuka gama canja launi zuwa ja duk sai yaji tai masa wani irin 'kwarjini mai cike da ban tsoro,, kallon seconds sukaiwa juna,, kafun tai masa wata irin runguma,, d'an ware idonsa yayi a tsorace,, ji yayi ta sauke wani irin kuka.. a hankali tanayi tana ajiyar zuciya.. wani irin abu ya dinga ji a game da ita wanda baita'ba jin kwatankwacin sa akan ko wace mace ba. dan dukan bayan ta yashiga yi alamar lallashi.

a hankali ya dinga jin saukar numfashin ta alamun bacci yayi gaba da ita,, d'ago da ita yayi ya'kurawa Kyakyawar fuskarta ido"

Murmushi yasaki lokaci d'aya ba tareda yasan dalilin yinsa ba.

d'aukar ta yayi zuwa d'akin ta, ajiye ta yayi kan kyakyawan gadon ta yayi mata addu'a, ya rufe ta. fad'awa uwani yayi tana d'aki tayi bacci dan Allah ta dinga dubata shi yatafi masallaci, amsawa uwani tyi shi kuma ya fice.

*****
Salma"wai uban mai kikai mata taimiki wannan d'anyen aikin?

Mommy... dan Allah kibar ni da abunda yadame ni tun d'azu kin wani saka mutum a gaba sai masifaffen tambaya kike masa.. ha'a... Ko kuwa ke lokacin da haukar ta ta motsa ta shigo miki d'aki wani abun kikai mata?

Naga dai tasha yiwa mutane haka idan haukar ta ta motsa ko?

Dn Allah Kinga ni kibar ni.

ido hajiya Rahamu"ta zuba mata,, kafun tayi 'kyacci tafita,, irin tarbiyar da tabaiwa yarta kenan, gashi tana matu'kar son yar tata shi yasa Sam bata cika yi mata fad'a ba Sam hasali ma bata ganin laifin ta.

Salma"tunanin mafita tashiga yi,, tanason auren Zaid kuma ba taga alamun mommy tanason taimaka mata akan hakan ba yazamar mata dole ta nema wa kanta mafita saidai kafun nan tana bukatar taji sauqi ta yadda zata samu karfin yin al'amuran ta cikin sauqi.

Murmushi tasaki ganin tasamawa kanta mafita cikin sauqi.....

Toh fa!

Yanzun ne fa 😂😂Ni kaina yanzun nakejin dad'in labarin lol 🤣

Hhhh

Son_so 😍😘😍

Xinnee smart 😂💕💋👌

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro