Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

BABI NA TALATIN DA HUDU

Jay's Outfit..
***
A cikin sati biyun da suka gabata, ta mayar da kanta tamkar mai zaman takaba, kullun tana gida, a gidan ma a ɗaki take rufe kanta, cikin sa'a ta samu Rukayya ta fara sabawa da mutanen gidan, hakan yasa take barin ta tana sakewa. Jafar kuwa tun ranar da Babanshi ya zo, yayi mata text cewar ya tafi da shi, ko kayansa bai tsaya ya ansa ba.
In banda k'unci da rashin walwala babu abin da yayi katutu a zuciyarta, sai ɗan lokaci zuwa lokaci da ta kan taɓa karatun jamb ɗin da zasu zana sati mai zuwa.
Babban abinda ke addabar zuciyarta bai wuce yadda take son ta manta Sadam ba, amma ko sau ɗaya hoton fuskarshi, bai taɓa bacewa a cikin zuciyarta ba, ta kasa daina mafarkinshi kamar yadda duk lokacin da idonta ya kai kan Rukayya take ganin tamkar mahaifin nata ne, ba don komai ba sai dan asalin kamar da suke da shi.
Komai nashi ta ɗauko, hatta da manya-manyan idanunsa da sukan tafiyar da bak'in ciki da damuwar da ke zuciyar Jameela.

"Haba Ummi, ina kike shirin jefa kanki haka? Yanzu a yi mutum a duniya ba zai fito yayi fira da iyayenshi ya ma ji daɗi a ranshi ba? Sai dai tunda kika dawo gidan nan baki da wani aikin da ya wuce ki shige ɗaki ki kulle? Haba Ummin Baffa."

Da murmushin k'arfin halin da ta k'ak'alo ta ɗago tana duban Goggo wacce a zahiri bata san lokacin da ta shigo ɗakin ba.

"Wallahi babu komai Goggo, karatun jamb ɗin nan ne ya sako ni gaba, kinga Baffa bai tashi sanar da ni ba sai satin da ya wuce, kuma ni na ma rasa ta inda zan fara karatun wallahi, ga shi next week za ayi exam ɗin ban ma san ya zanyi ba."

K'arasawa tayi ta zauna a bakin gadon, kallonta take cike da so da kuma tausayawa kalamanta, Ummi da a da take mutum mai tsananin son karatu, yau itace take maganar ta mance yadda ake yi. Girgiza kai tayi, sannan ta kama hannunta, hakan yasa Jay ta mik'e daga kwancen da take tana murmushin k'arfin hali tana dubanta.

"Banda abinki Ummi ai daurewa zaki yi, idan kika yi la'akari da yanayin da muke ciki zaki gane cewar baya son ki rasa wannan damar a karo na biyu. Kiyi hak'uri ki daure kiyi karatu, kada ki tsaya wurin duba k'urewar lokaci. Kina jina?"

"Haka ne Goggo. In sha Allah zanyi iyakar k'ok'arina."

"Allah ya taimaka, ya miki albarka, ya kuma shige mana gaba baki ɗaya."

"Amin amin."

"Yanzu ki tashi ki je ga abinci can an kammala, ki daure ki saka ma cikinki wani abu."

"Zan tashi in sha Allah."

Da haka ta mik'e ta fita, ita kuma tayi baya da kanta, ta koma ta kwanta tana mai cigaba da aikin tunaninta.

***
Tsaye take gaban madubin tana k'are ma kanta kallo, ta kuma kasa gaskata irin canjin da take gani a tattare da ita cikin 'yan kwanaki.
Bak'ar abaya ce a jikinta k'irar India wacce aka yi ma ado da zanen filawa kalar ruwan gwal mai sheki, bak'in gyalen abayar ta lullube kanta da shi, bayan ta tattara cikakken gashin kanta ta ɗaure a tsakiyar kan, inda kuma tayi naɗin cikin wani salo da ya k'ara fito da doguwar fuskarta wacce haskenta ya k'ara dawowa a ɗan hutun da ta fara samu a gidansu.

Bak'ar agogon fata ta ɗaura wacce aka rubuta MK (Michael Kors) a fuskar agogon, ta sanya bak'ak'en sneakers a k'afarta, sannan ta rataya reddish brown ɗin jakarta kirar channel, ta ɗauki wayarta, ta matsa gaban madubin tana kallon yadda ta canja completely, duk da cewar ba wani make-up ta tsaya yi ma fuskar tata ba.
Murmushi ta saki, tana jin wani yanayi a tattare da ita, ta juya ta fita zuwa ɗakin Goggo.
Tsaye ta same ta tana k'ok'arin buɗe wardrobe, da alama shirin wanka ta ke yi, a haka ta isa suka gaisa, ta dube ta da fara'a da jin daɗin yanayin da ta ganta.

"Wai ba dai har kin shirya ba?"

"Na gama komai Goggo, Baffa kawai zan gani in tafi."

"Allah yasa ayi a sa'a, Allah ya bada rabo mai amfani."

"Amin. Amin"

Ta juya tana kallon Rukayya da ke kwance tana bacci kan gadon Goggo, sannan ta mata bankwana ta fita zuwa part ɗin Baffanta.

"Sannu da hutawa Baffa. Ina kwana?"

"Alhamdulillah Mamana. Har kin fito kenan."

Baffa ya faɗa lokacin da ya mik'e daga shingiɗar da yayi, jikinshi sanye da jallabiya mai gajeran hannu, hannunshi na dama rik'e da casbaha, hakan na nuni da lazumi ya ke yi.

"Na fito Baffa."

"Masha Allah. An shi nan, mota na nan waje na sa Ado driver ya fito da ita an wanke anyi duk abinda ya dace, ki kula da titi, Allah ya bada sa'a."

Yayi maganar sa'adda ya mik'a hannu saman stool ɗin da ke tsakanin kujerar da ya ke da wacce ke gefe ya ɗauko makullin mota yana mik'a mata.
Kasa ansa tayi, haka kuma kanta a k'asa tana girgiza shi.

"Nagode Baffana, amma ba ni da hannun da zansa in anshi kyautar ka a halin yanzu. Kayi hak'uri ka bar ni in saka maku da alherin da kuka yima rayuwata tun daga ranar da kuka haife ni har izuwa yau da baku gajiya ba."

Murmushin dattako Baffan yayi, a zuciyarsa yana alfahari da canjin da ya ke gani a tattare da 'yar tasa, sai dai ba wannan ba ne zai sa ya hana ta morewa da kuma jin daɗi daga dukiyar da ya tara domin ita da mahaifiyarta.

"Kada ki damu Mamana. A kullu yaumun ina alfahari da ke, ina kuma mai yaba ma k'wazonki wurin son ganin kin daɗaɗa mana. Anshi nan kiga, wannan kyauta ce ta musamman daga gare ni. Allah yi miki albarka."

Hannu biyu ta sa ta ansa, a karo guda idonta suka ciko da k'walla, tana cigaba da rattaba ma Baffa addu'o'i, ta mik'e ta fita.
Bin bayanta yayi da kallo, alal hak'ik'a yana jin daɗin yadda take rayuwa a natse yanzu, yana matuk'ar son yadda take girmama su tana basu wani matsayi na daban, take kuma sanya buk'atarsu a farko kafin tata. Ba dan ba dan ba da sai ya ce gara da aka yi haka, tunda ko ba komai, yanzu Umminshi ta zama mutum sak kamar kowa, yarinya mai ladabi da biyayya ga iyayenta, anan kuma dabarar samo mata malamin addini da zai cigaba da koyar da ita addininta ta faɗo masa. Yayi murmushi tare da cigaba da jan casbahar da ke hannunsa.

Bak'ar BMW M4 ta gani an parka a gab da k'ofar palon sai k'yalli ta ke, a hankali ta kai duba ga number motar ta gane number tsohuwar motarta ce a jiki, a karo guda ta latsa makullin da ke hannunta, a take ta ji motar ta ansa kuwwa, tare da nuna haske daga fitilun da suka k'awata gabanta.
Cikin jin daɗi ta shiga ta tada motar, Allah ya taimaketa automatic ce, amma ta san da manual ce da baza ta iya tuk'a ta kai tsaye ba.

Yadda ta juya steeringwheel ɗin, a take kuma tayi reverse, sai ya zamana tamkar bata kwashi wasu shekaru ba tare da ta yi tuk'i ba.
Da reverse ta fita daga gate ɗin gidan, sannan ta juya ta hau titi sosai, ta murza motar ta fara tafiya hankalinta kwance.
Titin F.C.E ta dosa kasancewar can ne centre ɗinta, cikin walwalar da ta rasa ko ta mecece ta isa har gaban hall ɗin tayi parking, sannan ta fito ta wuce ciki.

Sun kwashi kusan awa ukku kafin suka kammala komai, saboda tsaikon network da suka rink'a samu.
Fitowa tayi ta fara takawa zuwa inda tayi parking, sai dai jikinta ya bata tamkar wani yana kallon ta. Sai da ta isa gaban motar, sannan ta juyo, cikin rashin sa'a ta sauke idanunta a kansa.
Murmushi ya jefe ta da shi, hakan ya k'ara tabbatar mata da cewar shi ɗin ne dai ba wai mai kama da shi ba ne ba.
Murmushin itama ta saki lokacin da ya iso gabanta, idanunshi a waje yana binta da kallon mamaki.

"So it's you?"

"Sure. Nima ina ganin kamar kai, kamar ba kai ba. Me ya kawo ka garin nan?"

"Wallahi nine fa. k'anwata na kawo jamb, saboda d'aukar alhaki irin na mutanenmu duk garuruwan da ke kusa da Maid su rasa inda zasu cillota sai Katsina. Tun jiya muke garin nan."

"Sai hak'uri ai. Ina kwana bamu ma gaisa ba."

"Wallahi fa, Alhamdulillah. Ya ke kam me ya zo da ke nan? Ina Kazaure and baby na san tayi wayau ko?"

"Its a long story. Baby ta girma har tana shirin shiga school ma. Ya wurinsu Malam da Hajiya?"

"Kowa lafiya lau. But please ya aka yi na ganki nan?"

"Ka share kawai Faisal. Ba abinda zan ce wanda ya wuce Alhamdulillah. Please Ka bani number Malam da na Hajiya zan kira su in sha Allah. Dama ina ta tunanin ina zan samu numbers ɗinsu."

Bai k'ara cewa komai ba, ya karanta mata numbers ɗin, inda shima ya buk'aci tata, ta bashi suka yi bankwana ta shiga ta tafi, sai dai ta bar zuciyar Faisal Goni taf da tunani kala da kala, a ciki kuwa hadda wani bak'on lamari da ya ziyarci zuciyarsa, a take ya fara addu'ar Allah yasa hasashenshi ya zama gaskiya

***Bayan Shekara daya***

A hankali ta ɗago tana k'are mishi kallo. Ba fari ba ne, haka kuma ba za a saka shi a jerin bak'ak'e ba, irin chocolate color ɗin nan ne masu wahalan samu, sumar kanshi a cike take dam, wacce ta kwanto ta gefen fuskarshi, ta saukar da wani saje mai asalin kyau, da bala'in tsada, kasancewar ba a fuskar kowanne namiji zaka iya ganin irinshi ba.
Yana da madaidaitan idanu masu haske da shek'i, 'very attractive', haka kuma eyelashes ɗin da suka mik'e tsaye saman idon sai suka k'ara mishi kwarjini, suka kuma k'awata shi.
Idan ta koma ta kan siffar jikinshi, tsayayyen namiji ne dogon gaske sai dai bai cika faɗi ba.
Zubin jikinshi ya fi yanayi da zubin fulani, irin dogayen nan masu kalar jikin 'yan hutu.
Cak ta tsaida idanunta kan laɓɓansa, wanda suka kasance jajaye daga ciki, yayin da bak'i ya zagaye su, hakan ya k'ara ma santalar doguwar fuskarsa ado.
'Tabbas namiji ne, ya zo da zuwanshi, ta yadda ake son namiji ya zo, domin a wannan ɗan lokacin da ta karance shi bata hango makusa ko kaɗan a tattare da shi ba, most importantly, idan tayi duba ga kyawawan ɗabi'u da halayenshi, sai dai bata tunanin zata iya ansa tayin da ya zo mata da shi, kasancewar zuciya da ruhinta gaba ɗaya sun ta'allak'a wurin son mutumen da ta haramta ma kanta soyayyarshi, hakan yasa take jin tayi bankwana da soyayyar kowa a gaba ɗaya rayuwarta.

"Shekara guda din da ta gabata, na yi ta ne cike da rashin natsuwa da matukar tashin hankali, na takura zuciyata, na wahalar da ita, na sanya ta cikin wani hali na tunani, na bari har sai da lokaci yayi sannan na dawo gare ki. Ba zan ɓoye miki ba, na kamu da wani zazzafan ciwo a taakanin kirjina, wanda matsawar baki taimaka wurin bani magani ba, Jay bana tunanin zan samu sauk'i ko kuma sassauci a tare da ni."

Kai ta fara girgizawa, wasu zafafan hawayen da bata fahimci ko na menene ba suka yayyafo a idonta na hagu, ta kawar da kai ta goge su, sannan ta juya tana kallon shi.
Bata san me take ji game da shi ba, ta dai san ba so ba ne, sannan kuma baza ta kira shi k'i ba, dan ko ba komai, bai cancanci ta jefe shi da kalmar k'iyayya ba. Duk da cewar ta so ta fahimci hakan tun rana ta k'arshe da suka rabu, amma bata yi zaton zai iya tunkararta da wannan gagarumin batun da ya sosa mata zuciya ba, yanzu gashi nan ya dauke ta, ya mayar da ita ruwa tsundum a soyayyar Kazaurenta, wacce ta samu ta ɗan lafa a k'asan zuciyarta.
Hawayen da ta ke mak'alewa ne suka kasa tsayawa, hakan yasa suka gangaro a kumatunta.
Ganin hakan ba k'aramin tsirga zuciyar SS yayi ba, da sauri ya mik'e ya isa inda ta ke, hannu yasa ya dafa kujerar da ta ke zaune, kawar da kanta tayi saboda kallon da ya ke mata ba zata iya jurar irin shi ba.
"Watak'ila zaki kira ni mutum mai son kai, ma ci amana, ko kuma wanda bai san darajar abota ba. Idan kika yi mun kallon ɗaya daga cikin waɗannan, hak'ik'a kin zalunce ni. Jay ban zo wurinki da wata manufa ba face alkairi, haka kuma ko ta wane irin hali ba zan taɓa bak'anta zuciyar da zaki ara mun ba. Zan rik'e ki da amana da gaskiya, zan kula da ke in baki kowanne irin farin ciki a rayuwa. We ain't kids, balle mu tsaya muna ɓata lokacin juna, we're big enough to know what we feel about each other. If you don't like me, say it, and I promise I'll understand."

Mik'ewa tayi da sauri, tana ciigaba da girgiza kai, har tana bige hannunshi dake kan kujerar da ta tashi, bata iya furta komai ba, ta juya ta bi ta k'ofar baya ta wuce ciki, cikin sa'a babu kowa a palon, direct ɗakinta ta faɗa, ta maida k'ofar ta rufe, sannan ta zube kan gado a take ta rink'a kuka marar sauti, mai tsananin zafi.

Alal hak'ik'a ko a duniyar film ta ga namiji ya furta ma mace kalmar I love you, ba kowa take tunawa ba illa Kazaure, haka zalika yanzu da Sagir ya furta mata kalmomin, babu abinda ke yawo a cikin kanta bayan ranar da Sadam ya furta I love you a gare ta.
Ya zata yi da soyayyar mutumen da ya wulak'anta ta ya wulak'anta gudan jininta?
Ya kuma zata yi da SS da ya bijiro mata da tashi soyayyar? A matsayinshi na mutumen da ya taimaka wurin samun freedom a rayuwarta. Mutumen da yayi mata halaccin da ba kowa ba ne zai iya yin irin shi a wannan duniyar tamu da taimako ya zama abu mai matuk'ar wahala.

"Ya Allah kai ne gata na, bani kuma da zaɓi face wanda ka yi mun. Ya Allah Ka warware mun matsalolin da suka addabi rayuwata."

Ta k'arashe da kuka mai sauti, a dai-dai lokacin wayarta da ke jone jikin chaji ta ɗauki ruri alamar text yana shigowa.

'Da zaki san yadda kukan ki ke wahalar da zuciyata, na tabbatar da kin daina zubar da hawayenki har abada. I won't force you to like me, I just wanna let you know that I'm madly in love with you. See ya tomorrow.
....SS'

Wani abu ta ji ya tsirga tsakiyar kanta, a karo guda ya cigaba da yawo a cikin jinin jikinta.
Bata ankara ba call ɗin wata sabuwar number ya shigo mata, sai dai har wayar ta gama ringing bata da mu da ta ɗaga ba.
Kiran ne ya k'ara shigowa a karo na biyu, hakan yasa ta shafe hawayenta, sannan ta ɗaga wayar ta ɗora a kunne.
Muryar Faisal da ta ji yasa ta ɗan ɓata rai, a karo guda tana mamakin mutum irin shi, wato dan ya ga ta daina ɗaukar waccen number tasa, shine ya bijiro da kiranta da wata sabuwar number.

"Ina jinka."

Ta bashi ansar tambayar da yayi cewar
"kina ji na kuwa?"
"Ina ta kira baki ɗaga ba, and Malam told me kunyi waya, hakan na nufin tawa wayar ce bakya ɗauka ko?"

"Haba Faisal, me sa baza ka fahimci abinda nike kwatanta maka ba? Kai kanka kasan wutsiyar rak'umi ta yi nisa da k'asa. And by the way, wallahi ba abinda ke gabana kenan ba, kuma sanin kanka ne ko aure zanyi babu dalilin da zai sa in faɗa ma saurayi wanda bai taɓa aure ba. Kayi hak'uri mu bar maganar nan please."

"But ba haramun ba ne ai, idan kika lura ma sunnah ce mai k'wari, dan haka ki k'ara nazarin maganata, in sha Allah ina nan zuwa gobe da safe."

"What? Please I'm begging you kada ka ba kanka wahala, wallahi abinda kake nema a wuri na ba zai taɓa samuwa ba Faisal, kayi hak'uri mu cigaba da zumunci kawai."

"Ba zan iya ba Jay. Domin kuwa tun ranar da na ganki na kasa samun sukuni a zuciyata. A lokacin da kuka yi waya da Malam kika sanar mishi labarin rabuwarku da Kazaure ina zaune a wurin, kuma tun daga nan na ci alwashin sai na mallakeki ko ta wane irin hali."

Bakinta ta cika da iska ta furzar, wannan wane irin abu ne ke shirin faruwa da ita? Upon all people, why SS? Why Faisal Goni? Mutanen da suka fi kusanci da Kazaure. Hakan na nufin dama munafuntar shi suke yi kenan...

"You heard me ba. Ina nan tafe in sha Allah. Take care of yourself for me."

Ya kashe wayar, sai kawai ta tsinci kanta da bin wayar da kallo, abin ma mamaki ya rink'a bata, ta wani ɓangaren kuma yana bata dariya.
Me mutane suke son mayar da ita?
Tambayar da ta yima kanta kenan, amma bata san ina zata samo ansar ba.

***
Da shirinta ta fito hannunta sagale da jaka da makullin motarta. Inda Goggo da Rukayya ke zaune ta isa. A gefe ta zauna itama da murmushi a fuskokinsu, yayin da Rukayya ta isa da sauri ta faɗa jikinta.

"Mammy ina zaki je?"

"Tare da ke zamu je ai. So bana son surutu. Idan munje zaki gani."

Murna ta fara yi, sannan Jay ta juya tana kallon Goggo.

"Zan je gidansu Miemie. In sha Allah baza mu daɗe ba zamu dawo."

"Kai amma kin kyauta Ummi. Haka ake son mutum ya zama mai gyara kuskurenshi a duk lokacin da ya fahimci hakan. Allah ya tsare, a gaishe mun da Hajiya."

"Amin. Zasu ji in sha Allah."

Ta mik'e suka fito hannunta rik'e da na Rukayya, ta buɗe mota ta saka ta, ta ɗaura mata seatbelt, sannan ta zagaya ta shiga, ta tada motar suka tafi.
Cikin mintuna sha biyar ta isa gidan, ta fito ta zagaya ta fito da Rukayya tare da kama hannunta, ta rufe motar sannan suka sanya kai zuwa ciki.
Hajiya suka tarar zaune a palon, ta k'arasa suka gaisa, sai dai yanayin kallon da matar ke mata na alamar sani ne, amma ga dukkan alamu ta manta inda ta san fuskar tata.

"Jameela ce Hajiya. Miemie na nan kuwa?"

"Haba ko da na ji. Nifa ina ta yi miki kallon sani amma na kasa tunawa. Ina kika samo yar budurwa? Zo taho nan mu gaisa."

Ta k'arasa maganar tana mik'a hannu ma Rukayya, amma ta mak'e kafaɗa, ta matsa, ta kara mak'ale hannun Mammynta.

Murmushi kawai Jay tayi, bata iya cewa komai ba, illa Rukayya da ta kalla tana cewa

"Kije Hajiya na kiran ki."

Dagowar da zata yi, kwatsam ta sauke idanunta a kan Miemie wacce bata san lokacin da ta fito ba, har ta tsaya tana kallonta.

"Jay?"

Ta faɗa idanuwanta a waje. Sai a lokacin Hajiya ta juya,

"Kinga ashe tana kusa ma. Ku shiga ciki mana."

Mik'ewa suka yi, suna bin bayan Miemie, anan suka fara kallon-kallo. A k'arshe Miemie ta isa ta rungume Jay, take suka fara hawaye, suka yi mai isarsu suka gama, sannan suka zauna suka fara firar yaushe gamo.

Labarin duniya da na rayuwa suka tsunduma sosai, Miemie ta bayyana mata halin da ta shiga bayan ta samu labarin tafiyarsu da Sadam, yayin da itama Jay ta labarta mata yadda rayuwa ta kasance mata bayan ta bar gida.
Wani sabon babin kukan suka buɗe, dak'yar suka tsagaita, Miemie ta kamo Rukayya tana cewa

"Rabon wannan fine girl ɗin tamu ne. Gata nan kamarta sak da Kazaure, hatta idanun bata bari ba."

"Owh, wato har yanzu baki manta shi ba ko? Kodai har yau baki daina crushing ɗin shi ba."

"C'mon."

Miemie ta faɗa a tak'aice, a karo guda suka sa dariya, a dai-dai lokacin wayar Jay da ke ajje gefe ta fara ruri.

'Faisal Goni'

Shine sunan da ya bayyana kan screen ɗin wayar tata, idonta a waje
"Ba dai da gaske yaron nan yana Katsina ba?"


Diiiiiiiiiing!

So Jay an zama cele😂😂😂😂

I dey team... which team are you?😁😁

Lubbatu👏😍

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro