Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

BABI NA ASHIRIN DA SHIDDA

**Sadam

  "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un."
  Sa'id da ke tsaye gefensu ya faɗa, tare da matsawa yana duba idanun mahaifin nasu, kasancewar shi likita, anan kuma ya tabbatar da Baban nasu ya ansa kiran mahaliccinsa.

  "Lafiya?"

   Sadam da ke zaune ba tare da ya fahimci abinda ke faruwa ba ya tambaya yana kallon Sa'id.
  Bai iya cewa komai ba, illa kafaɗarshi da ya dafa, ya juya ya fita idanuwansa taf da hawaye, hakan ya ba sauran 'yan uwan damar k'arasawa bakin gadon domin gane ma idanuwansu abinda ke wakana.

    "Ya rasu."

  Cewar ɗaya a cikinsu, hakan yasa Sadam ya mik'e ya koma jikin bango ya dafe kanshi, kuka yake bil hak'k'i da gaskiya, har sai da 'yan uwan suka tausaya ma yanayin da yake ciki.
  Basu ɓata lokaci ba suka fito da gawar, bayan anyi duk abinda ya kamata, suka shige motocinsu, suka ɗauki hanyar Dutse.

  Shigarsu gidan kenan, tun ba'a shigo da gawar ba suka samu mutane na faman rirrik'e Haj. Daso da kanta ya mimmik'e tsaye, tana faman k'wacewa ita a dole sai ta fice.
   Hauka take tuburan, domin kuwa duk wani abu da ke ɗakinta sai da ta fasa shi, kafin aka samu taimakon k'attin maza majiya k'arfin da suka rik'e ta.
  Sa'id da ya fara shigowa ne ya ci karo da diramar da ake yi, gefe ya jingine yana kallon yadda k'aik'ayi ya koma kan mashek'iya, ta wani fannin kuma mutuwar mahaifinshi na damun zuciyarsa. Kallon mutanen da suka rik'e ta yayi

  "Ku sake ta, dama zaman jiran lokaci kawai take yi."

  Suna sakinta kuwa ta runtuma da gudu, ta fita a gidan, yayin da jama'ar k'ofar gida ma babu wanda yayi gigin tarye ta.
  Gawar suka shigo da, 'ya'yan nashi ne suka taimaka wurin gyara ta, in banda Sadam da har yanzu bai daina zubar da hawaye ba.
  A haka suka ɗauke shi zuwa makwancinshi na gaskiya, suka saka shi cikin k'asa, duk kuwa da irin dukiyar da ya tara, wacce shi bai ci ba, bai kuma bar 'ya'yansa sun anfana da ita ba lokacin da yake rayuwa.
  Bayan sun gama duk abinda ya kamata, suka dawo gida suka cigaba da zaman makoki, sai dai kuma ruhi da gangar jikin Sadam Baffa Kazaure, ko alama basa tare da shi. Domin kuwa sunyi nisa sosai ga al'amurran da suka addabi rayuwarsa, wanda suka haɗa da ɓatan Jay, da kuma mutuwar mahaifinshi.

***Jay.

Idanuwanta da ke kulle ta buɗe lokacin da ta ji motar ta tsaya, hakan ya tabbatar mata da sun shigo cikin gidan.
  Ido ta ware tana kallon yadda gaba ɗaya gidan ya canja mata, yayin da maganar SS ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta dulmiya.
  "Muje ko?"
  Yayi maganar lokacin da ya fito, yasa hannu yana k'ok'arin buɗe masu k'ofa.
  Kai ta fara girgizawa, zuciyarta a raunane, haka hawaye suka gagara zubowa a busassun idanuwanta.

  "Its okay, na fahimci abinda kike son faɗa, ku fito mu je please."

  SS yayi maganar ta hanyar katse mata ta ta maganar da ta so yi. Bata iya cewa komai ba, illa hannun Rukayya da ta kama ta fitar da ita, ta zuro k'afafuwanta waje, ta biyo bayanta, sannan ta juya ta fito da Jafar shima.
  Wata doguwar baranda suka mik'a, wacce da alama ita zata sada su da k'ofar shiga, duk kuwa da kasancewar ba su da tabbas, ganin yadda aka canja tsari da yanayin gidan baki ɗaya.
  A k'ofar palon suka tsagaita, SS ya danna doorbell ɗin da ke mak'ale jikin rufaffen k'yauren, wata yar budurwar da bata fi shekaru ashirin zuwa da ɗaya ba, ta iso, ta buɗe k'ofar.
  Cikin rashin sani ta gaishe da su, SS ya tambaya
"ko masu gidan suna ciki?"
  "Suna nan."
  Ta bashi ansa lokacin da ta koma gefe, hakan ya bashi damar sanya kai ciki, ya juyo yana yi ma su nuni da su shigo suma.
  Kanta a k'asa ta ɗaga k'afarta dak'yar, ta shigar a tsararran palon da ya wadatu da sanyin AC, mai haɗe da k'anshin turaren wuta. A karo guda bugun k'irjinta ya cigaba da tsananta lokacin da suka k'arasa cikin palon, kowannensu ya nema ma kanshi mazauni.
  Wucewa 'yar budurwar tayi zuwa ciki domin ta sanar da masu gidan, hakan yasa SS ya kai duba gareta, yanayinta kaɗai, ya fassara tashin hankalin da ke shimfiɗe cikin zuciyarta.

   Gaban Goggo da ke biye da yar budurwar da taje kiranta ne yayi mummunar faɗuwa lokacin da ta tunkaro palon tun bata k'arasa fitowa ba.

  "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un."
  Shine kawai abinda ta iya furtawa a dai-dai sa'adda ta ziro k'afarta cikin palon da suke.
  Kamar wacce aka mintsina, ta ɗago idanunta da suka zama tamkar garwashin wuta, sai dai babu ɗigon hawaye ko k'alilan, ta sauke su a kan kyakkyawar dattijuwar mahaifiyarta, wacce rabon da ta ga wannan fuskar ta ta mai cike da haske da annuri, shekaru biyar kenan cif-cif.

  Hawayen da take ta son su zubo mata ne suka fara kwarara tamkar an buɗe famfo, a haka Goggo da ta kasa ɗauke idanunta a kan Jay ta idasa shigowa, ta zauna daɓas, a kujerar da ke gefen Farouq.

  Duk da bak'i da lalacewa da jikinta yayi, hakan bai hana mahaifiyar ta ta gane ta ba, haka kuma duk da shekarun da ta kwasa ba tare da su ba, haka zalika bai canja k'auna da soyayyar da take mata ta ɗa da mahaifi ba.
    "Ummi!"
  Goggon ta fada cikin wata irin murya mai k'arfin amo, ba tare da ta maida kai ga gaisuwar da mutanen wurin ke yi mata ba.
  Kai take jinjinawa, alamar ita ɗin ce, yayin da zafafan hawayen da suke zuba, ba su tsagaita mata ba, har zuwa lokacin da Goggon ta iso gabanta ta mik'ar da ita, ta haɗa ta da jikinta suka k'ara fashewa da wani gagarumin kukan da ya tsuma zuciyar SS da ta Farouq, har ma da ta 'yar budurwar da ta shigo ɗauke da tray domin kawo masu abubuwan motsa baki.

  Babu wanda yayi gigin tsayar da su, sai da suka yi mai isarsu suka gama, sannan Goggo ta zaunar da ita, ta juya tana kallon sauran jama'ar wurin.
  SS ne ya fara gaishe ta, ta ansa tana mai mai son tuna inda ta san fuskarsa, sai dai ta kasa a haka ya gabatar da Jafar a matsayin  ɗanshi, Farouq kuma k'aninshi.
  Gaishe ta suma duk suka yi, ta juya tana kallon Rukayya.

  "Wannan kuma fa?"

  Shiru kawai suka yi babu wanda ya iya ansa ta, sai Jay da ta zube a k'asa tare da dafa gwiwoyin k'afarta tana kuka, tana neman yafiyar mahaifiyar ta ta.

  "Ki yafe ni Goggo. Ki gafarta mini, ki ji k'aina ki yafe mun laifin da na yi. Na san na bak'anta zuciyarku, na san nayi laifin da ban cancanci yafiya ba, amma kuyi hak'uri, ku gafarce ni domin Allah."

"Kinyi kuskure Baby, kinyi babban laifi na fifita namiji akan iyayenki, sai dai kuma mu muka taimaka miki wurin hakan, mu ne bamu tsaya mun kula da ke mun tarbiyyantar da ke ta hanyoyin da musulunci ya tanada ba, mune muka bi son zuciyarmu, muka bi da ke ta yadda muke so, dan haka ba ke kaɗai zaki nemi yafiya ba Ummi, nima ki gafarta mun, ki yafe mun a bisa irin tarbiyyar da na baki, wacce duk itace ta kai mana rayuwa izuwa haka."

  Ta mik'ar da ita ta zaunar a gefenta, a lokaci guda ta daga hannunta sama

  "Allah nagode maka da ka dawo mun da farincikina. Allah nagode maka da ka bani wata dama domin gyara ɓannar da nayi, Allah nagode maka da ka dawo mun da Ummi lafiya."

  Juyawa tayi tana kallon SS, ta rasa ma abinda zata ce da shi, gashi tana jin a zuciyarta kamar ta san fuskarshi, sai dai ta kasa tuna ko a ina ne, a k'arshe ta mik'e tana cewa

  "Barin sanar da mai gidan. Ta so muje Ummi."

  Ta faɗa tana kallon Jay da har yanzu kuka kawai take yi, sai dai ta samu wani ɗan sassauci ganin yadda Goggo ta anshe ta hannu bibbiyu.
  Girgiza kai tayi, alamar baza ta je ba, bata takura ta ba, ta juya cikin hawaye da murna ta doshi part ɗin Baffa da ke hagu da palon da suke ciki.
  Dawowarshi kenan daga sallar isha'i ya zauna da niyyar fara kallon labarun duniya a tashar Aljazeera, Goggo ta shigo da sassarfa, tamkar wacce aka biyo da gudu.

  "Lafiya?"

  Baffa ya tambaya yana gyara zaman medical glasses ɗin dake idonsa.
  Bata iya cewa komai ba, illa

  "Akwai babban al'amari a palon bak'i, taso ka gani Alhaji."

  "Me ke faruwa?"

  "Ta so ka gani da idonka."

  Ta juya zata fita, yayin da ya ajje remote ɗin hannunsa, ya mik'e ya rufa mata baya.

  Duk da yawan shekarun da ya kwasa bai ganta ba, da canjawar da halittarta tayi, da kuma baya da ta juya mashi, ba shi yasa ya mance yanayin wacce ke zaune gabansa ba, ba shi kuma ya hana shi danne k'auna da soyayyarta da suke barazana da lafiyar da Allah ya bashi ba.
  Cikin tsananin fushin da ya kasa ɓoyuwa a saman fuskarsa ya juya da zumar komawa inda ya fito, SS yayi saurin mik'ewa, ya isa gabanshi tare da rissinawa ya gaishe da shi.

  "Sagir?"

  "Nine Alhaji."

  "Dama kana duniyar nan?"

  "Tabbas ina raye. Sai dai ba matsala ta ba ce ta zo da ni a yanzu."

  "Ta wacece kenan?"

  "Ta Jameela ce."

  "Wacece haka kuma?"

  "Jameela dai 'yarka."

   "Ni nike da 'ya Jameela? A ina ka samu wannan labarin?"

  Yayi maganar yana nuni da k'irjinsa.

  "Ka ganta fa Alhaji. Ummi ce ta dawo kallo nan ka ganta."

  Goggo tayi maganar tana nuni da inda Jay ke zaune tana wani irin kukan da Baffa ke jin shi har cikin zuciyarsa.
  Juyowa yayi a fusace, ya fara magana cikin wata dakakkiyar murya mai k'arfin amo da karsashi.

  "Ban san maganar da kuke yi ba, domin ni Alhaji Kabiru bani da wata 'ya mai suna Ummi, ko kuma Jameela kamar yadda kai ka faɗa. Dan haka minti ɗaya na ba mutanen da suke cikin palon nan su tattara su fita su bar mun gidana."

  Kuka Goggo ta saka mai wani irin sauti, wanda yasa Rukayya fashewa da kuka ta matsa ta k'ank'ame mamanta, a dai-dai lokacin Baffa ya kai idanunsa kan 'yar yarinyar da ke asalin kama da mutumen da ya fi tsana a gaba ɗaya duniyar nan, wanda yayi silar rugurgujewar jin daɗi da farincikinsa.
  Kawar da kansa yayi, sannan ya juya ya fara tafiya, yana kwaɗa kiran mai gadi.
  Ganin haka yasa duk suka mik'e, suka doshi hanyar fita, amma Goggo ta kama hannun Jay da Rukayya ta rik'e k'ark'adam.

  "Me sa ka bar irin mutanen nan suka shigo mun gida? Me sa baza ka fara neman izinina kafin wani ya shigo ba?"

  "Ayi hak'uri yallaɓai, ban san za'a samu matsala ba wallahi."

  "Tashi ka fitar mun da wannan."

  Yayi nuni da Jay, sannan ya cigaba.

  "Kuma daga yau, ko katangar gidana bance ka barta ta kara taɓawa ba."

  Cikin tashin hankali mai gadin ya mik'e yana raba ido, hakan yasa Goggo ta k'ara matse hannun Jay

  "Babu inda zata je Alhaji, idan kuma ka matsa akan a fitar da ita, to k'afarta k'afata, sai dai duk mu bar maka gidan ni da ita."

  "Ya isa haka."

  Cewar SS da ya matso gabansu. Sai kuma a yanzu Goggo ta tuno inda ta sanshi.

  "Sake ta muje."

Yayi maganar yana kallon Goggo, yayin da Baffa ya juyar da kai.

  "Matsawar kika k'ara ɗaga k'afarki daga inda kike, to ki tabbatar zamanmu ni da ke ya zo k'arshe Maryama."

  Daga haka ya juya da sauri, kasancewar wasu zafafan hawaye da suka taho suka wanke dattijuwar fuskarsa.
  Suna kuka suna komai, haka SS ya raba hannun Jay da ke cikin na Goggo da kalaman rarrashi, suka fita daga palon, suka doshi inda suka yi parking motarsu.

***
B

abu wanda ya iya cewa wani abu a cikinsu, hatta da yaran. 
  Kowa ka kalla a cikin motar, akwai abinda yake sak'awa a k'asar zuciyarsa, in banda Jay da har yanzu sheshshekar kukanta ke tashi, ta wani ɓangaren kuma tana da buk'atar k'arin bayani jin yadda Baffanta ya kira sunan SS kai tsaye, wanda ita bata ma san cikakken sunan nashi ba.
  Farouq ne yayi gyaran murya, idanunsa a kan titi.

  "Ya kamata ace Baffa yayi hak'uri ya saurari abinda ke tafe da mu, duk da dai naga alamar kun san juna kai da shi."

  Shiru SS yayi mashi, hakan yasa ya ɗan juyo yana satar kallon shi.

  "Yaya fa. Baka ji me nace ba ne?"

  "Ina jinka Farouq, amma sanin kanka ne yanzu ba lokacin magana ba ne, dan haka ka kula da tuk'inka muje gida tukun."

  Babu wanda ya k'ara cewa uffan, har suka shigo cikin Barhim, unguwar da ta kasance inda mahaifiyar tasu ke zaune.
  Gida ne madaidaici, mai yalwar wurin ajiyar motoci, (parking shade) inda suka samu mota guda biyu a ajje, ɗaya lullube da riga, yayin da ɗayar ke ajjiye a gefe, da alama ita aka fiya hawa.
  Sai da Farouq ya gama gyara parking, sannan kowa ya fito, SS ya buɗe bayan motar ya ɗauko Jafar wanda yayi bacci a saman kafaɗarsa, Jay ta kamo hannun Rukayya suka mik'a zuwa cikin gidan.

  Fuskar dattijuwar matar da suka samu zaune k'unshe da kyakkyawan murmushi, hakan ya fito da asalin kamarsu da SS. Farouq ya isa ya zauna gefenta yana gaishe da ita, labbanshi k'unshe da murmushin farinciki shima.

  "Sannunku, sannunku."

  Fara kyakkyawar dattijuwar mai shekaru kusan hamsin da bakwai ta rink'a maimaitawa, ta yi saurin kama hannun Rukayya tana kiran
"yar budurwa"
duk da ba taɓa ganin su ta yi ba, daga ita har Jameela.
  Karamcin matar ne ya sa Jay shafe hawayenta cikin gaggawa, fuskarta da murmushin da iyakarsa laɓɓanta, ta rissina har k'asa tana gaishe da ita.

  Cikin jin daɗi ta ansa, a karo guda ta kai duba ga fuskar SS wanda babu walwala a tattare da shi, lokacin da yake shimfiɗar da Jafar saman doguwar kujera, ya koma gefe ya zauna.

  "Sannunku Hajiya, ina wuninku."

  "Lafiya lau Sadic. Ya hanya?"

  Jin sunan da Hajiya ta kira SS da shi wanda ya sha ban-ban da wanda Jay ta ji Baffanta ya kira shi yasa tayi saurin ɗaga kai tana kallon yanayin da ya ke ciki.
  Ba tare da wata damuwa a fuskarsa ba ya ansa da

  "Alhamdulillah. Mun same ku lafiya?"

  "Lafiya lau muke. Ya ka ji da rigimar Farouq?"

  "Ga shi nan fa, exams zai fara amma saboda rigima sai da ya biyo mu, na faɗa mishi final year tana buk'atar karatu, amma rigima irin ta Farouq ta hana shi maida hankali wallahi."

  "Ya zaka ce haka Yaya? Bayan kai da kanka kana yaba ma k'wazona a karatu, kawai dai ina missing Hajiya ne, bazan iya ganin mai zuwa garin nan in k'yale ba."

  Yayi maganar yana kallonta, da 'yar dariya k'unshe a bakinshi.

  "A dai maida hankali Farouq. Allah kuma ya taimaka."

  "Amin."

  Gaba ɗaya suka ansa da shi, sannan 'yan mazan suka mik'e domin sauke faralin sallolin da ke kansu, ba tare kuma da Hajiya ta tsayar da su don sanin wacece matar da suka zo da ita ba, illa ma mik'ewa da suka yi tare da Rukayya a hannunta, ta juyo da murmushinta tana kallon Jay.

  "Tashi kema kije kiyi sallah, kafin su gama ku ci abinci, na san ba komai kuka ci a hanya ba."

  Tashi tayi ta bi bayanta, suka isa ɗaki ta nuna mata toilet sannan ta fito.
  Sai da suka gama duk abinda za suyi, suka ci abincinsu, bayan sun dawo palon sun zauna, sannan SS ya yi ma Hajiya bayanin wacece Jay, da dalilin da ya sa suka kawo ta nan.

  Fuskar Hajiyar kawai zaka kalla ka gane yadda tsantsan tausayin Jay ya mamaye ta, a hankali tasa hannu ta gyara ma Rukayya da tayi bacci a gefenta kwanciya, sannan ta maida kallonta ga SS.

  "Yanzu menene abin yi? Wanene mahaifin nata?"

  "Jikar Mal. Baba ce."

  SS ya faɗa a tak'aice. Hakan ya sa Hajiya fito da ido waje, a karo guda ta furta

  "Allah sarki. Lallai ka cika ɗan halak Sadic. Allah ne yasa zaka rama karamcin da mutumen nan yayi maka ta wannan hanyar."

  Tsagaitawa tayi, tana kallon Jay cikin wani irin yanayi, sannan ta cigaba.

  "In sha Allahu komai zai warware kinji. Ki saki jikinki, ki ɗauka tamkar a gida kike, da izinin Allah za'a samu mafita."
  Bata iya cewa komai ba, saboda yadda maganganunsu suka ɗaure ta, inda ta fara tambayar kanta wai shin wanene wannan SS Tafseer?

  "Tafseer?"

  Ta maimaita sunan na k'arshe a cikin zuciyarta.
  Duk yadda aka yi yana da alak'a da family ɗinta, kasancewar inkiyar kakanta Mal. Baba kenan, haka zalika shine cikon suna na ukku, da mahaifinta yake amfani da shi.

  "Wanene wannan?"

  Ta k'ara tambayar kanta, duk kuwa da cewar ta tabbatar bata da ansar, matsawar ba wani a cikin mutanen da ke zaune gabanta bane ya ansa ta.
  Da wannan sak'e-sak'en a zuciyarta, suka mik'e zuwa ɗakunansu, domin kuwa dare ya riga yayi, sai dai daga ita har Sagir S. babu wanda ya samu damar runtsawa a cikin daren kai tsaye.

***Washe Gari.

  Da shirinshi ya fito cikin ɗanyar farar shadda ɗinkin kaftani, riga da wandonta. Bak'ar hular da ya ɗora a kanshi, ta k'ara haskaka santaleliyar fuskarsa, mai cike da kwarjini da annuri, yayin da ya fara takowa cikin palon Hajiya, k'afafunsa lulluɓe cikin bak'in takalmi na H&M.
  Ita kaɗai ce a palon, sai 'yar budurwar da ke taimaka mata da aikace-aikacen gida, wacce tana ganin shigowarsa ta gaishe da shi, ta mik'e ta wuce kitchen.
   "Ina kwana."
  Ya gaishe da ita, cikin jin daɗi ta ansa, tana k'are ma yadda yayi wani ɗan wuya kallo, ma'ana ya rame, duk da kasancewar kusan wata guda kenan, bata ganshi ba.

  "Lafiyar ka kuwa Sadic? Ni sai naga duk ka rarrame."

  "Lafiya lau Hajiya. Ina Jameela?"

  Ya tambaya ta hanyar kawar da maganar da ta kawo, domin kuwa shi kanshi ya lura da hakan cikin 'yan kwanakin nan.

  "Tun da suka ci abinci ta shiga yi ma yara wanka, kaga har yanzu basu fito ba."

  "Zan koma gidan Alhaji ne, zan je muyi magana da shi, idan nayi sa'a ya saurare ni to, idan kuma banyi sa'a ba, daga can zan wuce Daura kawai, duk da alk'awarin da na ɗauka na ba zan k'ara zuwa gidan Mal. Baba ba, amma dole in hak'ura inje ko dan samuwar farincikin ita Jameela."

  "Hak'uri dai zaka yi Sadic, shi mutum a kullun alkairin da aka mishi ya kamata ya rink'a tunawa, ba wai sharri ba. Kuma ma banda abinka, Malam ai ba laifinshi bane. Allah dai ya taimaka ya kuma bada sa'a kai dai."

  "Amin."

  Ya faɗa, kafin ya mik'e, hannuwansa cikin aljihu, idanunsa a kan k'ofar ɗakin da Jay ke ciki.
  Bai jira fitowarsu ba, yayi ma Hajiya sallama, ya fito harabar gidan.

  Gidan Baffa ya dosa, zuciyarsa taf da fargaba, domin kuwa shi ya san wanene Baffan, matsawar ya hau dokin nak'i, to fa sauko da shi sai wanda ya shirya.
  A farfajiyar gidan ya same shi zaune k'asar wata canopy da ke gefe kadan da inda suke parking motoci.
  Jaridar WeeklyTrust ce rik'e a hannunsa yana dubawa, idanunsa ɓoye cikin medical glasses ɗin da ya k'ara ma dattijuwar fuskarsa annuri.
  Wannan ba shi zai hana ka gane yanayin bak'incikin da zuciyarsa ke ciki ba, ta yadda yake sakin tsaki lokaci-zuwa-lokaci, a karo guda kuma yana kai duba ga k'ofar shigowa ta gidan, tamkar mai jiran wasu gagaruman bak'i.

  Ganin motar Sagir da ta shigo, ba k'aramin farinciki ya ji a cikin zuciyarsa ba, hakan yasa shi sauke wata ajiyar zuciya ba tare da saninshi ba, duk da ba wai ya nuna jin daɗin a saman fuskarsa ne ba.
   Jaridar da ke hannunsa ya ajje, ya tattara hankalinsa zuwa ga SS da ya tunkaro inda yake zaune.

  A kujerar gefenshi ya zauna, tare da rissinawa ya gaishe da shi, shima cikin halin ko in kula ya ansa duk da yanayin guiltiness da ya samu zuciyarsa a ciki.

  "Na zo ne a kan maganar Jameela."

  Yayi maganar kanshi a k'asa.

  "Idan wannan ne maganar da ta kawo ka, gara tun baka ɓata ma kanka lokaci ba, ka tashi ka koma inda ka fito."

  "Ka daure, ka yi hak'uri ka saurari batun da nazo da shi."

  "Batun menene Sagiru? Batun 'yar da na haifa na mutunta na gwada mata soyayya ta watsa mun k'asa a ido shine batun da zan tsaya in saurara? Ko ko batun 'yar da ta fifita soyayyar wani k'ato a kaina? Haba mana, kuyi mun adalci mana, ku tuna irin k'ask'anci da tozarcin da Ummi ta yi ma rayuwata, ku tuna bak'inciki da tashin hankalin da ta cusa ma zuciyata mana."

  "Alal hak'ik'a Ummi tayi kuskure babba, kuskuren da ya koyar da ita darussan rayuwa, kuskuren da yasa ta fuskanci hukuncinta tun ba'a je ko ina ba, kuskuren da ya hana mata jin dad'i da walwala. Sai dai ina son ka tuna dukkan wani dan Adam ajizi ne, kuma mai laifi ne, a haka kuma Allah yake gafarta mana, ka tabbata kuma da ace ba'a yafiya a duniya da babu abinda zai kawo ni gabanka har in nema ma 'yar da ka haifa yafiyarka, ka tabbata da idan naga 'yarka cikin wani mugun hali babu dalilin da zai sa inyi k'ok'ok'arin fitar da ita. Kayi hak'uri, ka gafarce ta, ka dauki tafiyarta a matsayin k'addara wacce ta rigayi fata, kuma isahara ce akan iyaye masu hali irin naku, haka kuma rabo ne na yarinyar da ta dawo da ita, domin kuwa idan Allah yayi rantsuwa akan aure, ko wata irin matsala za'a samu sai fa an daura, haka kuma idan rabo ya ratsa tsakani to ko akan titi ne sai an haifi yaron. Ka gode Allah da bata dauko maka wannan abun kunyar ba, ka kuma gode Allah da ya bata ikon gane kuskurenta, har ya karkato maka da hankalinta gida. Ka tuna cewar ba ita kadai ke da kamasho a tafiyarta ba, akwai taimakon ku, ku iyayenta da kuka hane ta tarbiyya mai kyau, wacce kai ba haka aka yi maka ba, domin kuwa ni shaida ne akan haka. Ka dubi darajar Allah, ka rungumi 'yarka domin kaima ka samu damar gyara laifin da kayi. Wannan ne kawai abinda zan iya yi, zuciya dai taka ce, kai ne kuma wanda zaka yi controlling duk abinda ta ayyana maka."

  Da gama faɗar haka da wasu 'yan mintuna ya fara k'ok'arin mikewa, jin shirun da Baffa yayi kanshi a k'asa, da alama ba shi da niyyar cewa wani abu.

  "Na bar ka lafiya."

  SS ya kuma faɗa, sa'adda ya sanya kai zuwa inda yayi parking motarsa.

  "Sagiru."

  Baffa yayi kiran shi cikin wata dasashshiyar murya, marar k'arfin amo, wacce ta sanya SS tausaya mishi, saboda juyowar da yayi, ya ga hawaye na zuba a fuskar babban mutum kamar shi..

Allah Sarki Baffanmu😭

Tsakanin da da mahaifi sai Allah...

What's between SS Tafseer and Kasad family?

Stay tuned, to find out 💃💃💃💃

Lubbatu😍✌

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro