Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

BABI NA HAMSIN DA DAYA







Thank you for coming this far🥹❤️









~
BABI NA HAMSIN DA DAYA
~





Rike take da kanta tana murza shi saboda wani irin sarawa da ya yi. Ƙara kara wayar ta yi a kunnenta. "Yanzu yaya a ke ciki? Har ta iso?"

Sam Maimoon ba ta ji dadin zancen ba da Ummi ke fada mata Inna zata zo.

"Ba ta dade da isowa ba," Mimi ta amsa mata ta dayan bangaren. "A bangaren Jaddati za a sauke ta."

"To," ta ce tare sa sakin ajiyar zuciya. "Keep me updated. Baffa fa?"

"Yanzu ya fita daga falon zai isa chan."

Kai ta gyada daga nan su ka yi sallama. Cillar da wayar ta yi kan gado. Ba ta lura da Sayf ya shigo ba sai da ya yi magana.

"Lafiya Noor?" Ya tambaya yana isa gabanta inda ta ke zaune a bakin gado.

Daga kai ta yi ta kalle shi. "Inna ta iso."

Kai ya jinjina. Tunda ta ji labarin Inna zata zo ta daga hankalin ta. "Anjima da dare sai mu je ko?"

"Ba yau ba gaskiya sai gobe," ta ce tana zumbura baki.

Bai ce komai ba ya sa hannu ya mikar da ita sannan ya ja ta gaban madubi. Itama kuma tana bin shi kaman rakumi da akala. A gaban madubin ya tsayar da su ita a gaba shi a baya. Ya rankwafo ya daura habar shi a kan kafadar ta ta dama, ta cikin madubin su ka hada ido.

"Raihanatul Qalb," ya kira a hankali yana sumbatar gefen wuyan ta. Hakan ya sa ta runtse ido. Sai da ya bari ta bude kafin ya cigaba da cewa. "Ina son kin manta duk wasu kalamai da Inna ta taba fada miki, ki goge su sannan ki saurare ni da kyau. You. Are. So.Beautiful."

Juyo da ita ya yi suna fuskanta juna, idon shi cikin nata. "Kin taba fita da dare garin ya yi duhu amma hasken wata na haskawa? That's exactly how I see you Mahnoor, like the glow of moon light on a dark night."

Murmushi ta yi idanunta cike taf da kwalla. Sayf ya girgiza kai ya na share mata hawayen kafin ma su sauko. "I fell in love with your eyes. Fa tabarakallahu ahsanal khaliqeen. Mahnoor idanunki na rikita ni."

Daya bayan daya ya sumbaci idanunta sannan ya hade bakunan su wuri daya. Sayfullah ya tabbatar Maimoon ta haddace duk abunda ya fada mata.

***

Sam babu dokin da ta saba ji idan zata gida, kaman ta yi zamanta a fasa fitan ta ke ji. Wato ba zaka san yanda wani ya cutar da kai ba sai kana bada labari, a lokacin ne zaka gane tsananin  yadda aka cutar da kai.

Tana cikin mota Sayf ya rufe gidan. Bai ce mata komai ba da ya shigo mata sai riko hannunta da ya yi. A haka su isa Asokoro. Gidan Ummi su ka nufa Maimoon ta bar Sayf a falon kasa ta haura sama.

Ummi na zaune a dakin ta Maimoon din ta iso. Da murmushi Ummin ta tarbe ta. Ita ko Maimoon ta kura mata ido tana son ta ga ko akwai alamun damuwa tattare da mahaifiyar ta.

Ummi da ta gane kallon na me ye ta yi dariya. "Ni daina mun kallon kurilla. Ina Sayfullah din, mu je in gaisa da shi."

"Ummi...."

"Na ce mu je ko," ta ce tana saka hijabi. Har sun fita ta juya ta kalli Maimoon. "Ki kwantar da hankalin ki kuma."

Ajiyar zuciya ta yi ta bi bayan Ummi. Sayfullah ya sauko daga kan kujeran ya gaida Ummi. Ta amsa fuska a sake ta ce mai ya koma ya zauna. A kullum addu'ar ta Allah Ya basu zaman lafiya mai daurewa, ba karamin chanji take gani tattare da Maimoon ba kuma hakan na saka ta cikin farin ciki mara misaltuwa.

Mai aiki ta kawo musu ruwa da kayan kwalama ta ajiye kan tebur. Sayf ya bude robar ruwa ya sha.

"Ku isa wurin Inna ko? Tana sashen Jaddati."

Cikin Maimoon ya kara daurewa tana tuna lokutan da ta ke zuwa bangaren Daddy gaida Inna idan ta zo. Irin munanan kalaman da ta ke jefanta da su. Tana gaba Sayf na biye da ita su ka isa falon. Da Jaddati su ka fara haduwa. Tsohuwar ta yi mata murmushi.

"Maraba da takwara."

"Ina wuni Jaddati." A gefen kafarta ta zauna. Jaddati ta amsa tana shafa mata kai sannan ta juya su ka gaisa da Sayfullah.

Ba dadewa sai ga Inna ta fito. Sai da gaban Maimoon ya fadi tayi ta tasbihi a zuciya.

"To, su Maimuna ne. Sannun ku da zuwa."

"Ina wuni Inna. Ya gajiyar hanya, an iso lafiya."

"Lafiya lau. Gajiya kuwa babu ita dan a jirgi nazo, cikin minti kadan sai gamu mun iso abun mamaki."

Maimoon ta yi murmushin da a ke kira yake. "Masha Allah."

Inna ta maida kallonta kan Sayfullah. "Wannan ne mai gidan na ki?" Maimoon bata ce komai ba. Sayf ya sake gaishe da ita. "Lafiya lau. Ka dai san ni wacece ko? Ko ai baza ka sani ba tunda ba a dauke ni da daraja ba tunda har a ka yi auren ban sani ba. Idan da mutunci ai har Bauchi ya kamata a kai ka ka gaishe ni. Amma babu komai duk wannan ya wuce yanzu. Ya mutanen gidan duk kowa lafiya ko?"

"Lafiya lau Inna." Sayf ya amsa. Kowa ya yi kaman bai ji zancen da ta gama yi ba.

"Madallah. Oh Allah mai iko. Maimuna ke din ashe ba rabon Ashmaan ba ce shi ya sa abun bai yiyu ba."

Dif! Wuta ta dauke wa Maimoon. Mai tsohuwar nan ta ke shirin yi.

"Allah sarki, Hajiya ba ki ga irin soyayyar da yaran su ka yi ba amma kin san abunda Allah bai nufa ba...."

Runtse ido Maimoon ta yi. Ina ma kasa zata bude ta nitse. Me ye haka matan nan ta ke yi tsakani da Allah. Wani sabon salon cutar da ita ne ta samo ko mai. Ji yanda ta ke magana kaman ba ita ta gama cewa ba zata hada jininta da marasa asali ba. Dan rashin sanin abunda ya dace kuma a gaban mijinta zata dauko zancen da baya da tushe bare amfani.

Jaddati ta yi saurin katse Inna ta hanyar dauko wani zancen.

Maimoon ta ki bari su hada ido da Sayfullah dake kallonta tun dazu ta kasan ido. Ba su taba maganan da shi ba ko da wasa, asali ma bai san waye Ashmaan ba. Amma dai Inna sai a barta kawai.

Mikewa ta yi ta ce za su tafi. Bata bari Hajiya Inna ta fara sababi ba su ka yi gaba. Sayfullah bai ce mata komai ba itama sai ta basar. Tasan idan ba tsare shi ta yi ba zai iya cewa ba yanzu zai shiga wurin Ammi ba sai ya dawo daukan ta dan ya cika a gurguje yanda ba zai dade ba.

Ta san halin kayanta dan kuwa hanyan motar shi ya yi. Ganin babu kowa a harabar gidan ya sa ta janyo hannun shi ba tare da ce mai komai ba. Sayf ya girgiza kai dan ya tsammaci hakan. A kofar falon Ammi ta sakan mai hannu su ka cika tare. Sun ci sa'a Ammin na zaune a falo ita da Sameer.

Kamar kullum Ammi ta kasa boye tsanin murnar ganin Sayfullah. Sayfullah din da ta ke watanni bata ji ko muryar shi ba yau shi ta ke gani a gidanta a kai a kai. Sameer ya mika mai hannu su ka yi musabaha.

Kaman ko yaushe da ya gaishe ta ya ke yin shiru bai sake cewa komai sai sun tashi tafiya. To ya ce me? Da Maimoon su ka yi ta hira bayan an gaisa. Sayfullah Allah Allah ya ke ya tafi, gashi ba ya da wani abun da zai yi bare ya ce yana sauri.

"Sayfullah," kiran Ammi ya tsayar da tunani da ya ke yi. "A kawo tuwo, na san yanda ka ke son shi."

Jumlan 'na san yanda ka ke son shi' ya bata mai rai saboda bata san komai a kan shi ba. Kai ya girgiza mata. "Alhamdulillah, na koshi."

Maimoon ta runtse ido ganin yanda murmushin fuskarta ya gushe, amma duk da haka bata karaya ba, ta ce. "To bari a kawo maka snacks, jiya kanwar ka ta yi su."

An ci sa'a ya ci samosa da cake din da Sameer ya kawo mai. Kiran sallar la'asar ya tada su daga wurin. Sayfullah bai dawo ba sai text da ya aiko mata na cewar ya tafi.

A nan bangaren Ammi ta yi sallah. Bayan ta idar ta isa kitchen inda ta jiyo maganar Ammi. Ta sameta tana dauraye plates ta yi sauri ta amsa. "Babu wani abun da za a yi miki Ammi?"

Kai ta girgiza mata. "Babu komai."

"Ammi," Maimoon ta ce tana wasa da yatsunta. "Ina son in tafi da tuwon, zan iya diba?"

Murmushi Ammi ta yi. "Gashi nan cikin kula diba yanda zai ishe ki."

"Nagode."

Bayan ta diba abinci ta koma sashen su ta samu kannenta sun dawo. Suka zauna su ka sha hira abun su.

Sadiya ta ce, "Wai baku ga Inna wani salihacin munafunci ta ke yi ba."

"Kaniyarki Sadiya." Maimoon ta ce tana yi mata dakuwa.

"Allah kuwa Adda. Sai ka ce ba ita ba, yanzu haka wani abun take so."

"Ta ce miki?"

"Ina goyon bayan Sadiya Adda," inji Mimi. "Nima na yi tunanin haka. Daga gani akwai wani abu a kasa. Ba ki ga yanda ta yi wa Ummi jiya da ta iso ba harda rungumeta fa. Inna ta rungume Ummi wai duk cikin murnar ganinta ai kuwa kin san ba lafiya ba."

Maimoon ta bude baki cike da mamaki. Eh lallai dole su ce haka. Babban magana. "Allah Ya kyauta to. Ko ma me ye ita dai ta sani."

"Tofe ta kawai za mu yi da addu'a." Sadiya ta ce.

Sai dare Maimoon ta tafi. Ta ji dadi da bata ga wani chanji a tattare da Baffa ba, yanzu hankalinta zai kwanta. A gurguje ta yi wa Jaddati sallama saboda Inna.

Sun tsaya a hanya sun siya bredi da za su yi breakfast da shi gobe. Sayf ya bude kofar gidan sannan ya kunna wuta. Sun yi isha'i dan haka su ka baje a falo abun su.

Maimoon ta kwanta a kasa tana maida messages din whatsapp dinta. Akwai order ma da ya kamata ta mike ta shirya amma gaskiya yanzu ta gaji. Ji ta yi an fizge wayan kafin ta motsa Sayf ya danneta.

"Wayyo!" Ta dan yi kara tana dariya. "Zaka karya ni."

"Waye Ashmaan?"

Bata san lokacin da ta fashe da dariya ba. "Au dariya kike yi." Ya sake danneta daman chan ba wai ya saki nauyin shi a kanta bane.

"Yi hakuri zan fada."

Jin haka ya dagata tana sauke lumfashi. "Yaron Daddy ne."

"Ba haka Inna ta ce ba," ya daga mata gira. "Ex din ki ne?"

Kai kawai ta gyada mai. Daga nan bai sake cewa komai ba hakan kuwa ya yi mata dadi dan bata son zancen abunda ya wuce. Zancen Ashmaan kuwa ya dade da wucewa.

"In kawo maka tuwo?" Idonta a kan shi tana son ganin yanda zai yi (reacting).

"Ci kayanki na koshi."

"Me ka ci da ka koshi?"

"Ba komai," ya amsa yana mikewa tsaye. "Bana jin cin abinci, ki hado mun tea ina da aikin da zan yi."

Bai jira amsarta ba ya yi gaba. Maimoon ta girgiza kai. Bata taba sanin haka ya ke da taurin kai ba. Amma, babu komai, hakan ba zai sa ta karaya ba har sai ta cin ma burinta.




****

Kwanan Inna shida a garin Abuja. Mama ta karbe ta hannu bibbiyu saboda ba karamin ganin darajar Inna ta ke yi ba. Ta kulan mata da Muhammadun ta a lokacin da bata nan. Bata da abunda zata biya ta da shi.

Da Inna ta iso gidan kasa rufe baki ta yi dan duk hasashen ta bata hasasho irin wannan katafaren gidan duk da kuwa Bello ya yi mata bayanin su din su waye. Gwiwarta bata kara san yi ba sai da ta shiga ciki, ashe wajen ba komai bane. Gashi tunda ta iso a ke nan-nan da ita ko basarake sai haka.

Tana dakin da aka saukar da ita a zaune wayarta ta yi kara. Yanzu haka hatsabibin yaron nan ne Bello ke kiranta. Tunda ta zo garin nan ya ke addabarta. Dole ta amsa dan idan bata amsa ba haka zai yi ta kira.

Ko gaisawar kirki bai bari an yi ba ya ce, "Inna wai ya na ji ki shiru har yanzu?"

"Na rasa yanda zan yi Bello." Ita gaba dayan su cika mata ido su ke yi har Muhammadu kuwa da a da bata jin ko dar ta ke wanke shi tas! To yanzu har Rabi ma kasa hada ido ta ke yi da ita. Idan ta yi yunkurin fadin wata magana sai taji kaman an kama makogwaron ta an daure gam.

"Inna mutanen a yanzu ko mai kika ce su ba ki ba ki za su yi kar ki bari damar nan ta wuce."

"To zan gani."

"A'a fa Inna ba gani za ki yi ba, yi za ki yi. Idan ba so kike yi ki ganni bayan kanta ba ko a kurkuku."

"Subhanallahi! Me ya kawo wannan zancen kuma?"

"Dole in ce haka mana kin san halin da na ke ciki kuwa. Gina gani dai Abdulkarim ya yi kirilli mirilli ya ki bada ko sisi bayan tare a ka ci kudin nan da shi. Ki yi mai magana kuma kin ki."

"Ka fi kowa sanin yanda dan uwan na ka yake ni bana son fitina."

"To ai kuwa idan ba kiyi magana ba za ki gayyatowa kan ki fitina ne dan har ke sai an kama tunda ke ma kin ci kudin, ba kadan ba kuwa."

"Me ka ce?" Inna ta yi salati tana dafe kirji.

"Na dai fada miki. Mutanen nan kudin su har basu san ya zasu yi da su ba dan sun bamu kaso kadan a ciki ba ji za su yi ba. Kuma in kin kasa yi mu su magana kai tsaye ki yi wa uwarsu mana ita ai zata iya saka su yi ko basu yi niya ba, ba kin ce tana ganin girman ki ba."

"Sosai ma kuwa kai ka ce ciki daya muka fito."

"To kuma! Inna ki daina bata lokaci jibi fa za ki bar gidan kuma wa yasan lokacin komawar ki."

"A'a haba ai na san a sa a sake kawo ni mana."

"Ni dai ki yi mata magana Inna."

"To na ji jidalalle. Kai wannan in maye ne da an bani."

Da dare bayan sun gama cin abinci tare da Mama Inna ta yi gyaran murya. "Dama wata magana na ke so mu yi dake Hajiya."

"Wace magana Inna, lafiya dai ko?"

"Eh to, alfarma ce na ke nema ban san ko zan samu ba."

"Ah haba, fada ko me ki kike so in Sha Allah ba zai gagara ba."

"Auta na ne Bello ya ke cikin wani hali. Na san kin san shi ai dan a nan gidanshi Muhammadu ya zauna na tsawon shekaru. Dan kasuwa ne shima kaman su Nasiru to kin san yanda kasuwa take tsautsayi ya rutsa da shi kwanakin baya shine na ke neman a taimaka mai. Ya ce su Nasiru na taimakawa kamfanoni shine na ce ko za a yi musu magana a bashi ko miliyan hamsin ne ya kara hannun jari."

Mama ta jinjina kai, bata sa baki a harkar kasuwancin yaran amma, "Kar ki ji komai Inna."

"To to madallah Hajiya. Nagode. Wannan zumunci da aka kulla Allah Ya sa albarka ya bamu lada."

"Ameen."

Da Inna ta zo tafiya ta ga yanda manyan mutane ke abun su cikin girma da karamci. An hada mata sha tara ta arziki baki ya ki rufuwa. Inama a ce ta yi zamanta a nan kawai dan fatarta har wani sheki ta fara yi kwana biyun nan. Ana gobe zata tafi Maimuna da mijinta su ka zo yi mata sallama shima mijin ya bata kudi masu tsoka.

Tare da Baffa a ka kaita (airport), Sameer ne ya tuka. Ya fita ya fitar da akwatin Inna hakan ya ba ta daman yi wa Baffa magana. "To Muhammadu da fatan dai abun duniya ba zai rufe maka ido ba ka manta wanda su ka taimake ka a baya."

Baffa dai bai ce komai ba ta cigaba da cewa, "In an kwana biyu dai a rika waiwayon mu tsoffi kasan duniya baka da tabbacin za ka kai gobe ma. Yauwa Bello zai kira ka na nasa an aika mai sabuwar lambar ka."

"To Inna. Allah Ya kiyaye."

Kaman yanda ta zo an hadata da wani a cikin ma'aikatan da zai taimaka mata. Idan ta sauka a chan Bauchin kuma an tanadar mata motar da zata kai ta har gida.

Da dare sai ga kiran Bello. Baffa bai ma san shi bane sai da ya daga dan ba da lambar da ya ke da ita ba ya kira.

Bello a bangaren shi yana takaicin wai yau shi ke daga waya neman taimakon Muhammadu. Amma ya san idan be yi haka ba shi zai kwana ciki dan zai iya wayan garin ko wurin kwana bai da shi a yanda abubuwa su ka tafiya. Inna ta ce ta yi wa uwarsu magana amma har yanzu ya ji shiru. Ya yi ya yi da Inna ta sake magana amma ta kiya wai tana so ta kama girmanta itama kar a ga karantar ta. Ya san zance ne kawai tunda ta samu abunda ta ke so shi ko oho.

"Muhammadu kenan. Ganin ka sai an tona ya ya kwana biyu?"

"Lafiya lau Bello. Ya iyali?"

"Alhamdulillahi, ka yarda mu ai."

Baffa ya yi dariya.

"Mun ji abunda a ka yi wa Inna Allah Ya saka da alkhairi. Na ji dadin da baka manta da mutanen da su ka taimake ka a baya ba."

"Ameen," Baffa ya amsa yana share sauran zancen ko da chan ba tanka mai ya ke ba in ya fara sababi irin na Inna.

"Na ce Inna ta fada maka halin da muke ciki ko?"

"Eh ta sanar da ni. Allah Ya kiyaye gaba."

"Ameen, kuma ta sanar da kai inata zuwa ofishin Lamido group ban same su ba. Rashin sani ashe ma 'yan uwa ne."

"Mmm."

"So na ke yi kamfanin su ya sa mun hannun jari cikin kasuwanci na ko kuma su bani kudin a hannun ni nasan yanda zan yi da su...." nan ya yi ta kwararo bayani. "Kana jina Muhammadu."

"Ina jin ka Bello."

"Yauwa. Dan Allah ka sanar da su, a yi abun nan da gaggawa."

"Kaman yanda ka ce kamfanin nan ba nawa bane kaga saboda haka banda ikon sa su ko in hana."

"Me kake nufi?" Ya tambaya a harzuke. "Ba za ka taimaka mun ba ko me? Duk abunda na yi maka abunda zaka saka mun da shi kenan."

"Ba sai ka yi mun gori ba Bello. Tabbas ka taimaka mun kuma kullum addu'ata Allah Ya saka maka da alkhairi. Amma kaman yanda na ce maka bani da ikon sa su ko in hana su, ba da gumi na a ka yi komai ba dan haka bana da ikon yi musu katsalandan a cikin al'amari. Zan iya yi musu magana dan magana kaman yanda Inna ta yi wa Mama idan baka manta ba. Suna da ka'idoji da tsare-tsaren da su ke yin amfani wurin aikin su, idan komai naka ya yi daidai to zaka ji su idan kuma a cikin bincike da su ke yi sun ga wata matsalar da zata hana su tarayya da kai to. Sai anjima a gaida Suwaiba da yaran."

Kit ya kashe waya ba tare da jiran Bello ya ba shi amsa ba. Ummi na dakin amma ta yi kaman bata ji abunda ya gama cewa ba.

Sam Baffa bai ji dadin maganan da Inna ta yi da Mama ba. Duk yanda yaso boye haleyen ta sai da suka bayyana.

"Allah Ya kyauta," ya ce yana girgiza kai.










~Maymunatu Bukar💕

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro