Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

BABI NA HAMSIN DA BIYAR









~
BABI NA HAMSIN DA BIYAR
~







A kwana a tashi babu wuya wurin Ubangiji. Sayfullah da Maimoon suna rainon cikin su cike da kauna da kulawa. Kaunar da Sayfullah ke nunawa Maimoon a baya ba komai bane idan aka hada da yanzu, kaman ya hadiye ta dan so. Da ta motsa zai ce lafiya. Kafin ta bude baki ta ce tana bukatar wani abu har an kawo mata. Duk wani abu da ya zan zata bukata ko kuma zata nema saboda yanayin da ta ke ciki ya kawo ya ajiye.

Ta kan tsokane shi ta ce, "Habibi anya kuwa," sai dai ya yi murmushi ya girgiza kai ya ce, "Noor kenan."

Cikin kaman jira ya ke a san da zaman shi. Laulayi ta ke yi sosai har ya kai ga wani lokaci dole ta ke hakura da zuwa makaranta. Sayfullah ya so daukan hutu wurin aiki Maimoon ta ce sam maganan haka bata taso ba.

Yanzu ta gama amayar da duka abunda ke cikin ta. Sayfullah ya kawo mata da gurasa da ya dawo daga wurin aiki. Ba ta dade da gama ci ba ta dawo da shi, ko matsawa bata iya yi ba a nan falon tayi.

Sayfullah na tayi mata sannu yana shafa mata baya har ta gama. Hawaye ne suka cika mata ido musamman da ya je ya dauko kayan da zai gyara wurin da su. Babu alamun kyama ko takaici ya tsaftace wurin tas. "Tashi mu je ki kuskure bakin ki," ya ce mata bayan ya gama. Kawai sai tasa kuka. Sayfullah yayi tsaye yana kallonta. Kuka ta ke yi kaman wanda aka yi wa duka.

"Noor menene?"

"Dama gurasan bai isheni ba kuma gashi yanzu na amayar da shi. Kuma bakina babu dadi."

"To ki yi hakuri, yanzu zan sake siyo miki gurasar."

"Bana so, ni ice cream zan sha."

Dariya ke cin shi amma ya san idan ya kuskura yayi ze janyowa kan shi ne dan haka ya gimtse abun shi. Kayan zaki da basu dameta a da ba su suka zama abincinta yanzu. Da zai kyaleta su kadai za tai ta ci. Yanzun ma bai kamata ta sha ice cream ba amma idan ya ce a'a shima ya san sauran.

"To mu je ki kuskure bakin sai in dauko miki."

A kicin ta kuskure bakin Sayfullah ya bude freezer ya dauko babban robar ice cream. Cikin satin nan ya siyo amma har ta sha rabi. A nan kicin din ta shanye abunta tas harda sude bowl.

"Shikenan?" Ya tambaya. "Babu wani abun da kike so?"

Kai ta girgiza. "Babu. Nagode Habibi."

Hancinta ya ja a hankali. "Mu tafi."

Falo su ka koma inda yake aikin shi kafin ta yi amai. Laptop din shi ya dauka ya cigaba da aiki ita kuma tana zaune a gefe tana kallo.

Sayf yana ta aiki bai lura da tayi barci ba saida ya ji ta daura kanta a kafadar shi. "Daga shan zaki sai barci as usual," ya ce yana girgiza kai. Laptop din ya ajiye gefe ya dauketa ya kaita daki.

A gefen gadon ya zauna yana kallon fuskarta. Hannu yasa ya shafa kumatunta yana ji sonta da tausayinta na ratsa shi. Murmushi yayi yana hango da ko 'yar zata haifan musu. Kafin ya iso duniya son shi ya cika mai zuciya. Babu shakka babyn zai samu duk wani kulawa da Sayfullah bai samu ba. Sumbatar goshinta yayi sannan ya koma ya cigaba da aikin shi.

Bayan sati daya su ka je asibiti awo. Tana cikin sati na sha uku ta kusan fita daga (first trimester) anyi gwaji komai na tafiya daidai yanda ya kamata sai dai har yanzu (morning sickness) din na nan duk da likitar ta ce zai tafi.

"Girman babyn bai wuce lemun tsami ba." Cewar likitar bayan ta gama yi mata scanning.

Subhanallah! Allah Mai Iko! Kwalla ya taru a idonta, ta juya ta kalla Sayfullah da shima fuskar shi ke nuna tsantar farin cikin da ya ke ciki.

Bayan likitar ta sake tabbatar musu komai lafiya su ka kama hanyan gida.

A haka Maimoon ta cigaba da rainon cikin Sayfullah na kula da ita.


***

Sameer ya dauko su daga makaranta dama tun jiya ta fadawa Sayf tana so ta zo gida. Taso ta kwana amma bai yarda ba. Tana fitowa daga aji ta kira Ummi ta roke ta dan Allah ayi mata tuwon shinkafa da ko wace irin miya banda kuka.

Motar na tsayawa tayi hanyar gida miyaunta na tsinkewa. "Ina tuwon?" ta tambaya Ummi da ke falo bayan sun gaisa.

"Ba'a kawo ba."

"Waye zai kawo?"

"Ammi."

Maimoon ta zaro ido. "Ammi kuma? Ita da kanta?"

Ummi ta gyada kai. "Ina falonta kika kira, da ta ji tace zata yi duk yanda na so ta barshi taki."

Ummi na gama magana mai aikin Ammi da shigo da kuloli. Bayin da ke kasa ta shiga ta wanko hannu sannan ta zubo tuwon. Wayyo Allah! Tun kafin ta kai baki ma tasan irin dadin da zai yi. Miyar sai kamshi take ta sha kifi da nama. Ta ci abincin sosai sannan ta kora da (fresh fruit juice) mai sanyi da Ammi ta hado da shi.

"Adda in ci?" Sadiya tace tana bude kulan.

"Kar ki kuskura da kayana zan tafi."

"Kaiii Adda, yanzu ko malmala daya baza ki bani ba wallahi rai na ya biya."

"Ai baza ki taba bari na inyi kiba ba Sadiya, dauka amma fa daya."

Ummi na jin su ta girgiza kai da murmushi a fuskarta.

Maimoon ta kasa motsawa daga wurin da ta ci abinci. So take yi taje ta gaida Ammi kuma tayi mata godiya amma ta kasa tashi. Tana zaune a kasa jingine da kujera hannunta a kan cikinta da ya tasa.

Da kyar ta iya tashi ta nufi bangaren Ammi. Ta sameta a falo. Maimoon na shirin durkusawa ta gaisheta Ammi tayi saurin hana ta. "Haba Maimoon, a halin da kike ciki ai bai kamata ba. Ki kiyaye kin ji."

Cikin jin kunya ta gyada kai sannan suka gaisa. Bata dade ba ta koma sashen su saboda barci da take ji. Ta koma ta iske Baffa ya dawo. Sama sama suka gaisa tayi daki sai gado.

Karfe bakwai Sayfullah ya isa Asokoro. Jaddati ya fara gaishewa sannan ya nufa sashen mahaifiyar shi. A da zuciyar shi a cunkushe yake takawa ya isa bangarenta amma yanzu akasin haka. Dangantakar su har yanzu da sauranta amma an samu cigaba sosai.

A dining table ya same su suna cin abinci gaba dayan su harda Baba Nasir.

"Sayfullah," inji Ammi. "Bismillah shigo mana. Waahidah ta shi ki daukowa yayanki plate."

Waahidah ta mike don bin umarnin Ammi. A kujerar dake gefen Sameer ya zauna tare da mikawa dan uwanshi hannu. "Sannu da zuwa Ya sayf," inji Sameer.

"Yauwa Sameer," ya amsa sannan ya juya. "Ina wuni Baba."

"Lafiya lau Sayfullah, ya aiki?"

"Aiki alhamdulillah."

"Madallah."

Ammi ya kalla. "Ina wuni Ammi."

"Lafiya lau Sayfullah. An taso aiki kenan."

"Eh, Ammi."

"Masha Allah. Allah Ya taimaka Ya sa albarka."

"Ameen Ameen." Sayf ya amsa yana jin dadin addu'ar har zuciyar shi. A cikin fushi ya manta muhimmancin addu'ar uwa. Yanzu a duk lokacin da Ammi tayi mai addu'a yana jin farin ciki sosai.

Sayfullah na bangaren Ammi har aka kiran isha'i ya tafi masallaci tare da Sameer. Ba dangantakar shi da Ammi kadai ta chanza ba. Yana kokarin ganin ya saki jiki da kannen shi kuma ya janyo su jiki a matsayin shi na babba. Bature yace 'better late than never.' A hankali komai zai daidaita.

Maimoon na dakin Ummi suna hira. Ummi ta tambaye ta idan tana kula da kanta sosai. Bayan ta san tana da ciki ta rasa yanda zata sanar da iyayenta. Da alamomi suka bayyana Ummi ta cire kunya ta tambaye ta, taji kunya sosai musamman da Baffa shima ya kirata.

Mimi ta leko kai cikin dakin. "Adda Hamma Sayf yazo."

Ta same shi tare da Baffa suna magana. Sayfullah ya fara lura da ita ta kashe mai ido tana cizon lebe. Kauda kai yayi da sauri yana boye murmushin shi.

"Mamana kin fito." Cewar Baffa.

"Eh Baffa. Sai da safe."

"Allah Ya kaimu. Ku gaida gida."

Sadiya da Mimi suka raka su har mota. Sayfullah ya mika musu kudi su ka yi mai godiya sosai.

"Aiki ne ya rike ka sai yanzu?" Maimoon ta tambaya.

"A'a, tun dazu ina part din Ammi."

Ta jinjina kai. Wannan kadai ya isa ya sanar cewa akwai gagarumin chanji a tare da shi. Duk juma'a yana zuwa ya gaisheta sabanin da da sai ya dade ko kiranta a waya beyi ba. Allah abun godiya.

"Ammi ta yi mun tuwon shinkafa da vegetable soup mai dadi."

"Iyyeh! Ina nawa?"

"Na ajiye ma amma naji yunwa na cinye abuna."

Sayfullah yayi dariya. "Noor kenan, wasa tare ci banban ko."

"Ba laifina bane, laifin babyn ka ne."

Sayf ya dauke ido daga kan titi ya dubeta. "Kar kiyi wa baby na sharri, kin dai zama acici kawai."

"Ni ban zama acici ba."

"Mhmm, your cheeks tell a different story."

Maimoon ta sauko da mirror din motar da kalli kanta. Sai kuma ta turo baki. "Na yi muni."

"No Noor, you are prettier than ever."

Haka suka isa gida suna raha. Fitsari ne ya matsota, yana tsaida motar tayi cikin gida da sauri Sayf na ce mata ta bi a hankali. Wanka tayi gaba daya kawai da ta shiga rage mara. Bayan ta gama ta fito daure da towel, hakan ya kara fito da girman cikinta.

Sayfullah na zaune a kan gado ta fito. Ya samu kan shi da shagala da kallonta har saida tayi kaman zata tsone mai ido.

"Daina kallona."

"Never," ya ce yana kamo kugunta ya tsayar da ita tsakanin kafafuwanci. Hannu daya ya janye ya daura a tudun cikinta. "Hey baby, yau me kuka yi da Mamaa?"

Maimoon tayi murmushi ta rataya hannunta a wuyan shi. Tunda suka je awo likitar ta sanar dasu babyn ya fara ji kullum Sayf sai yayi mai magana da safe idan ya tashi da dare kafin su kwanta.

"..... I can't wait for you to join us," ya sumbaci cikin sannan ya mike.

"Ni baza ka tambaye ni mai nayi yau ba?" Ta tambaya tana turo baki. "Tun kafin babyn yazo har ka fara mantawa dani."

"Ni na isa, ina zan manta da Raihanatul Qalb dina. It doesn't matter idan prince ko princess kika bani, you will always be the queen."

Sadda kai tayi tana murmushi. Sayfullah ya dago habarta ya hade bakin su wuri daya. A hankali ya janye ya ce, "Wa kike wa winking dazu?"


****

"Tunda ya ce baza ki je ba sai ki hakura kawai." Muryar Ummi ta daki kunnen Maimoon.

"Ummi..."

"A'a Maimunatu ban sanki da gardama ba, ba halinki bane kar ki fara yanzu. Gardama ba hali mai kyau bane, duk mace mai gardama tana cikin wahala. Yiwa mijinki biyayya na gaba da komai, ki yi mata addu'a daga nan ma ya wadatar."

Kwallan da ya tarun mata a ido ya gangaro. Yanzu taya za a ce ba zata je bikin Safara'u ba, ba a yi mata adalci ba sam.

"To Ummi. Nagode."

"Kiyi hakuri. Kada kuma ki saka abun a ranki kin san dai halin da kike ciki."

Bikin Safara'u ne ya taso babu shiri. Dangin saurayinta Sa'ad sun je a saka rana bayan kai gaisuwa kawai kanin mahaifinta da yake shine waliyinta ya ce a daura auren. Wancan satin aka daura auren sati mai zuwa kuma za a yi taron biki.

Ta samu Sayfullah ta fada mai take yanke ya ce mata bazata je ba, bai ma tsaya ya saurareta ba. Kwana biyu kenan da faruwan haka. Shine dazu ta sake samun shi, amsar dai bata chanza ba.

A falo ta barshi tana shigowa daki ta fashe da kuka. Bayan ta saita kanta ta kira Ummi duk da tasan mahaifiyarta ba zata taba goyon bayanta ba.

Tuna yanda ko kallonta Sayf be yi ba tayi sai taji ranta ya sake baci. Data ta kunna messages daga group din da Habiba ta bude nata shigowa. Suna ta tsara abunda za a yi Habiba na tambayanta yaushe zata tafi Katsina.

Bata amsata ba ta kashe wayar ma gama daya. A dakin ta zauna tana cika tana batsewa. Tana kwance aka bude kofar, ta gyara kwanciyarta ta juya mai baya.

"Sauko kasa mu ci abinci." Bata motsa ba. Sayf ya sake maimaitawa nan ma ta sake yin banza da shi.

Bai sake magana ba ya juya ya fita. Dama mai neman kuka ne aka jefe shi da kashin awaki. Kiris take jira, ta sha kukanta kuwa ta koshi.

Bayan kusan minti talatin aka sake bude kofa. Tana ji ya ajiye abu akan tebur. "Maimunatu sauko ki ci abinci."

Zata iya irga sau nawa ya taba kiranta da sunan, kuma duk sanda yayi amfani da shi zai yi mata magana mai muhimmanci ne. Yanzu ma babu alamun wasa a muryar shi dan haka ta juya. Ido duk yayi ja. Bata kalle shi ba ta sauko kasa ta zauna. Farar shinkafa ce da vegetable sauce. Shi ya dafa shinkafar miyar kuma dumame ce.

Kaman an yi mata dole ta rika tura abincin. Sai kace karamar yarinya ya wani tsareta tana cin abinci. Dayake ranta bai so ba kwatakwata bata jin dadin abincin kaman tana tauna magani.

Da sauri ta ture plate saboda amai da ya taso mata. Shinkafar ko gama narkewa bata yi a ciki ba haka ta fito. Sayfullah na gefe yana shafa mata baya. Mikewar da zata yi jiri ya kwasheta da sauri ya kamota.

"A haka kike so in bari ki tafi Katsina."

Mouthwash ya dauko ya bata ta kuskure baki sannan ya kamata suka koma daki. A kan (ottoman) din dake gaban gado ya zaunar da ita shi kuma ya sa gwiwowin shi a kasa a gabanta.

"Maimoon," ya kirata a nutse. "Ki yi hakuri, da lafiya lau babu abunda zai sa in hanaki zuwa bikin kawar ki. Amma yanzu look at your condition, I don't feel comfortable in bar ki kiyi dogon tafiya. Zan kirata da kaina in yi mata bayani."

"Amma Habibi...."

"Kiyu hakuri amma bazan chanza shawara ba."

Babu yanda ta iya dole ta hakura. Tana roko Allah Ya bata ladan biyayya da tayi. A makwofin rashin zuwanta biki ya barta ta je tayi weekend a gida. Habiba ta kirata video call lokacin event din, tayi takaicin rashin zuwanta sosai. Kowa na wurin banda ita. A nan Katsina aka kai amarya.

A lokacin da cikinta ya shiga sati na ashirin ne suka tsinci kan su cikin firgici da tashin hankali.

Sun je anyi mata awo kaman yanda aka saba saidai wannan karon ba gyne din da ta saba gani ba ce ita tayi tafiya. Tayi mata test daban-daban wanda likitar baya bata cika yi ba. Tambayar taki ta kare har Maimoon ta fara gajiya.

"Kina amai da jin tashin zuciya sosai?"

"Eh, Dr. Hafsa tace morning sickness ne zai tafi."

"Haka tace? Kina experiencing shortness of breath ko kuma kiji bakya iya shakar lumfashi da kyau?"

Maimoon ta amsa mata da eh. Likitan ta jinjina kai tace gobe Maimoon ta dawo mata da sample dinta na fitsari dama ta dibi jininta.

"Habibi na tsorata da tambayoyin likitan nan fa," Maimoon ta sanar da Sayfullah a hanyar su ta komawa gida.

"Ki kwantar da hankalinki in Allah Ya yarda babu wata matsala."

Washegari su ka koma asibiti, lab suka nufa suka bada sample din. Nan da nan aka yi running aka kaiwa likitar. Sun sake yini a asibiti inda tayi mata gwaje-gwaje da dama wanda sakamakon a ranan ya fito amma sai yamma tun safe.

Maimoon ta tsinci kanta cikin faduwar gaba sosai tana tsoron sakamakon da test din zai ya nuna. Rike da hannu Sayf ta shiga ciki har suka zauna bata saki ba.

Likitar ta gyara zamanta. "A lokacin bincikenmu na ƙarshe, mun lura da wasu alamu, kuma ina so in yi magana da ku game da shi. Hawan jinin ki ya ɗaga sama,  sannan (the presence of protein in your urine have been elevated) kuma waɗannan alamu ne na yanayin da ake kira preeclampsia."

"Preeclampsia? Me hakan ya ke nufi?"

"Complication ne da ke faruwa a lokacin da mace ke da ciki. Hypertension ne wato hawan jini da cikin ke sakawa da alamun lalacewar gabobi, galibi hanta da koda. Serious complication ne da sai anyi takatsantsan saboda yana iya shafar lafiyar ki da ta dan dake jikin ki."

Maimoon ta runtse ido tana matse hannun Sayfullah. Hasbunallahu wa ni'imal Wakil!

"Babban (priority) din mu shine lafiyar ki...." sai kuma ta yi shiru.

Sayfullah ne yayi karfin hali ya ce, "Muna sauraron ki likita."

"Rashin ganowa da wuri yasa har ya fara taba hantar Maimoon. Idan aka yi la'akari da tsananin yanayin, akwai haɗari masu barazana ga rayuwa ki da ta jariri. Idan akai la'akari da wannan, dole ne in tattauna zaɓi na zubar da ciki don kare lafiyar ki."

Mutuwar zaune suka yi gaba daya. Basu taba zaton abunda zai fito daga bakinta ba kenan.

"Na fahimci cewa wannan bayanin yana da wahalar fahimta. Duk da cewa zubar da cikin shine zaɓi mafi aminci idan aka yi la'akari da tsananin preeclampsia dake jikinta. Ina so ku sani cewa shawarar ƙarshe ta ku ce. Za mu iya bincika wasu dama kuma mu sami ra'ayi na biyu idan kuna so."

Da sauri Maimoon ta mike ta bar ofis din. Shima ya mike zai bi bayanta kalaman likitar suka sa shi kasa motsi.

"Rayuwar matarka na cikin hatsari sosai. Cigaba da daukan cikin na iya sa ta samun stroke, organ damage da eclampsia wato seizure da kuma wasu complications din."

Babu kalaman da zasu yi bayanin irin tashin hankalin da su ka tsinci kan su a ciki. Duniyar su ta juya ta shiga cikin rudu. A cikin mota ya sameta ta rungume cikinta. "Ka kaini gida."

Sayfullah ya gurgura ya isa Asokoro. Bai motsa ba har Maimoon ta shiga gidansu. Kan shi ya daura kan (steering wheel) din.

Innā lillāhi wa innā ilayhi rājiʿūn, Allāhumma-'jurnī fī muṣībatī, wa akhlif lī khayram-minha.

Tunda ya zo duniya bai taba tsintar kan shi cikin irin wannan tashin hankalin ba. Ta ina zai fara? Mai ze yi? Wani hukunci ya kamata ya yanke? Kuma dole ya daure ya jure kada ya karaya, saboda idan ya karaya Mahnoor fa? Ita ya zata yi? Wa zai bata karfin gwiwa? Lumfashi ya saki har jikin shi na karkarwa.

Ammi ta fito zata wurin Jaddati taga motar Sayfullah. Tayi tunani ko ya shiga ciki saida ta matso kusa ta hango shi kai a duke. Jikinta ya bata babu lafiya. Da sauri ta taka zuwa inda motar take ta kwankwasa.

Sayfullah ya dago idanu sun yi ja jawur. Bai yi tsammanin ganin mahaifiyar shi ba. Da sauri ya kauda kai yana kokarin goge fuskar shi.

Ammi ta bude kofar. "Sayfullah?" Ta kira a tsorace. "Menene? Mai ya faru? Wani abu ya samu Maimoon?"

Kai Sayfullah ya girgiza yana ji zuciyar shi na kara karyewa. "Ammi..."

Ammi ta janyo hannun shi ta koma gidanta. Kaman karamin yaro haka ta ja shi har ta zaunar da shi kan kujera. "Menene Sayfullah? Ka fara firgita ni."

Ya bude baki yayi mata bayani kuka ya subce mai. Shikenan Ammi ta sake rudewa. Ta gama (concluding) wani abu ne ya samu Maimoon. Zama tayi kusa da shi ta janyo shi jikinta. Babu sauti ko daya saidai hawaye da take ji suna jika mata kafada.

"Ammi Noor da baby..."

Kukan shi ya saka ta kuka itama tun kafin taji mai ya faru. Tabbas duk abunda zai sa Sayfullah kuka ba kadan bane.

Da kyar Sayfullah ya samu ya saita kan shi. A hankali ya janye jikin shi daga nata. Kwalin tissue dake gefe ta mika mai ya share hawaye. Daga nan yayi mata bayanin duka abunda ya faru.

Ammi tayi matukar girgiza itama. "Sayfullah ba za a yi relying akan likita daya ba. Dole a nemo wasu options, there has to be another way."

"Ammi what if kafin a samu wani option din wani abu ya sameta. Ammi I can't loose her..."

"Babu abunda zai sameta Sayfullah. Ina Maimoon din tashi muje..."

A bangaren Maimoon kuwa tana shiga ciki ta fashe da kuka mai ban tausayi da ya razana su gaba daya. Sun zagayeta suna tambayarta mai ya faru amma ta kasa amsawa sai kuka da take yi.

A haka Sayfullah da Ammi suka shigo suka same su.

Baffa na ganin Sayfullah ya ce, "Sayfullah zo ka fada mana me ke faruwa dan Allah."

Ammi ta isa wurin Maimoon ta janyota jikinta sannan ta cewa Mimi su taimaka mata ta shiga daki. Ummi ta ce su shiga dakin dake nan kasa kawai. Ammi ta bi bayan su saboda ta samu ta rarrashe ta.

Sayfullah yayi wa su Baffa bayani. Ummi tasa kuka shima Baffa jikin shi ya mutu. Daidai lokacin Ammi ta fito bayan ta samu Maimoon ta daina kuka.

"Yanzu me ye abun yi?" Ummi ta tambaya tana kuka.

"Akwai kwararrun likitoci Ummi, ki kwantar da hankalin ki. Yanzu na gama magana da kawata Dr. Zainab, OB-GYN ce tana da asibiti gata nan zuwa."

Sayfullah ya mike ya shiga dakin da Maimoon ke ciki. Yana shiga su Sadiya su ka fita don su basu wuri.

"Habibi," ta sake fashewa da kuka.

Janyota jikin shi yayi yana danne na shi hawayen domin ya bata karfin gwiwa.

"Sayf kar ka bari su kashe mun baby. Kar bari su kashe mun baby." Abunda tayi ta maimaitawa kenan.

"Babu abunda zai same ku Noor, babu abunda zai same ku."

A jikin shi barci barawo ya saceta. A hankali ya kwantar da ita sannan ya shafeta da addu'o'i.

Dr. Zainab ta iso Sayfullah ya tattauna da ita. Ya bata sakamakon gwajin da aka yi tace tana bukatar Maimoon ta je asibiti saboda akwai wasu scanning itama da zata yi.

Sai da Maimoon ta farka wurin karfe biyar sannan su ka tafi asibitin a cikin gari. Nan ma tests da scanning din sun ki su kare. Bayan an kammala komai su ka koma ofis din Dr. Zainab.

"Wani asibiti kuke prenatal," Dr. Zainab ta jinjina kai bayan Sayf ya bata amsa. "Maganar gaskiya negligence din su ne yaja har abun yayi tsanani haka. Yawan amai da gajiya da kike yi duk alamomi ne na preeclampsia amma su kayi classifying din shi under morning sickness. Sannan amount of protein da ke fitsarinki ya nuna dadewar cutar a jikinki."

Ran Sayfullah ya baci matuka. Tabbas sai ya dauki mataki akan su. "Yanzu me ye abun yi Doctor?"

Dr Zainab ta gyara zaman ta. "Kaman yanda wancan likitar ta sanar da ku hanya mafi sauki da zai tabbatar da lafiyar Maimoon shine a yi stopping pregnancy din. Amma nasan wannan option din be yi muku ba. Sai dai kafin in yi muku bayani ina so ku sani wannan option din zai kara haɗari masu barazana ga rayuwa ki da ta jaririn ki."

"Cigaba likita." Maimoon tace.

"Goal din mu a nan shine mu yi controlling hawan jinin da kuma (function) din kodar ki sannan kuma mu tabbatar mun hana faruwar wasu complications din. Akwai magunguna da suke controlling hawan jini, sannan za mu kula da adadin (protein) din dake cikin fitsarin ki. (Prenatal) zai zama akai-akai saboda  bin diddigin ci gaban preeclampsia da aikin kodar ki. Sannan daga yanzu zamu baki (complete bed rest). Idan bayan duka wannan (precautions) din cutar yayi tsanani wanda bama fata zamu kwantar dake a asibiti har sai kin haihu

Yanzu kina sati na ashirin. Dalilin da yasa wancan likitar ta yi suggesting zubar da cikin shine ko an ciro yaron ba zai iya rayuwa a wajen mahaifa ba saboda be yi kwari ba. Amma idan har aka lallaba kika shiga watan ta na bakwai ko da ciwon ya cigaba za a iya ciro yaron (premature), ta haka za a ceto uwar da dan. Ku dauka lokacin ku kafin ku yi shawa..."

"Ba sai mun yi shawara ba," Maimoon ta katse ta. "We are going with the second option."

Dr. Zainab ta kalla Sayf. "Bari in baku wuri ku tattauna."

"Kar ka ce mun sai ka yi tunani a kai. Ba sai mun yi wani tunani ba, abunda ya kamata mu yi a fili yake."

"Mahnoor..."

Ta waiga ta kalle shi. "Kisan kai fa kenan. Ta ya zaka yi tunanin zan yarda a kashe mun yaro? Never!"

"Mahnoor idan wani abu ya same ki...."

"Kar ka mun haka Sayfullah." Ta sa kuka. "Ta ya zan cigaba da rayuwa idan na yarda aka kashe mun baby? Ba zan iya rayuwa da burden dinnan ba bayan akwai wasu hanyoyin. Dan Allah Sayfullah, na hada ka da Allah kar ka ce in yarda a kashe mun baby.
Please..."

Sayf ya runtse ido zuciyar shi na mai ciwo mara misaltuwa. Ya Allah! "Naji Noor, na yarda. Amma ki sani idan aka zo matakin da saina zaba, I'm choosing you."



***


Maimoon ta koma gidan su inda aka sata kan (complete bed rest) bata tashi sai ya zama dole, sallah ma a zaune take yi. Sosai iyayenta, kannenta da sauran 'yan uwanta ke kula da ita. Ba a barinta ita kadai bare ma ta samu damar yin tunanin da zai tayar mata da hankali. Mimi da Sadiya a nan suke kwana. Hakan yasa suka tuna rayuwar da suka yi a baya da ta wuce kaman ba a yi ba.

Kullum Ammi sai ta aiko mata da abinci da kayan kwalama sannan ta zo ta dubata. Mami ma ba a barta a baya ba, da anyi kwana biyu za ta zo dauke da kuloli. Ammah ma da taji labari ta dage sai an kawo ta ta duba Maimoon. Ta zo tayi kwana daya inda ta sauka a gidan Mami. Mami ta so riketa tace sam ita dubiya kawai tazo.

Sayfullah kusan ko da yaushe yana nan a ranakun da bai samu zuwa ba kuma suna makale a waya tare. Yana duk abunda yasan zai faranta mata rai kuma yana gujin abunda zai tayar mata da hankali.

Dr. Zainab na kula da Maimoon sosai. Matar nada kirki sosai, gida take zuwa ta dubata, saidai in tana bukatan wani na'ura ne zasu je asibiti.

Kuma Alhamdulillah komai na tafiya yanda ake so.


***

Baffa ya wayi gari da kiran da ya tayar mai da hankali. Ummi ma hankalinta ya tashi dukda bata san mai ya faru ba. Ta jira Baffa ya gama wayar sannan ta tambaye shi lafiya.

Girgiza kai yayi. "Ashmaan ne ya kirani. Gidan Bello yayi gobara jiya cikin dare ko tsinke ba a fitar ba."

"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un! Da fatan dai babu wanda yaji ciwo?"

Baffa yayi ajiyar zuciya. "Radhiya da Fauziya Allah Yayi musu rasuwa."

"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!" Ummi ta dafe kirji.

Hankalin su ya tashi sosai. Maimoon, Mimi da Sadiya mutuwar ta dake su. A ranan Ummi da Baffa suka shirya suka tafi Kaduna.

Ba karamar wuta bace duba da yanayin yanda gidan ya kone sosai. Har aka wayi gari akwai wasu wuraren dake ci da wuta. Ganin gidan ya girgiza Ummi.

A gidan makwabtan su dake tsallake ake zaman makokin. Ummi ta shiga ciki bayan tayi wa Bello gaisuwa. Bawan Allah gaba daya baya cikin hayyacin shi.

Jasrah na ganin Ummi ta rugo da gudu ta rungumeta sai tasa kuka kuma. Itama Ummin hawaye take yi. Hajiya Suwaiba na zaune sanye da hijabi idanuwanta a kumbure ga hawaye na zuba a hankali. Ummi ta tausaya mata saboda itama tasan radadin rashin 'da. Inaga ace yara biyu a lokaci daya ga kuma ta hanyar da aka rasa su.

Tunda abun ya faru Hajiya Suwaiba bata ga fuskar da ta sani ba saboda haka ganin Ummi ya sata fashewa da kuka. Duk abunda tayiwa Rabi a rayuwa amma gata tazo yi mata jaje da gaisuwa. Kaicho! Tana kallo gida da dukiyar da take takama da su take amfani wurin cin zarafin mutane su ka kone kurmus kaman fallen takarda kuma babu abunda ta iya yi. Saboda wanda Ya bata su Ya karba. Tare da yaranta guda biyu. Tun dazu take tuna yanda aka fito da gawarwakin yaranta ko gane su bata iya yi ba, gaba daya sun kone kurmus.

"Suwaiba ya muka ji da karin hakuri. Allah Ubangiji Ya yi musu rahama. Allah Ya baki hakuri da juriyan rashin su, Allah Ya baku ikon cin wannan jarabawar."

"Ameen Rabi," Hajiya Suwaiba tace kuka na kubce mata. "Ameen. Nagode, nagode sosai."

A waje wurin su Baffa ma kusan hakane. Bello na tunanin Muhammadu da ya wulakanta ya tozarta ya ajiye duk abunda ya ke yi ya taho amma dan uwan shi da suka fito ciki daya babu shi babu alaman shi.

Ashmaan tunda abun ya faru ko hawaye daya bai digo daga idanun shi ba amma ganin Baffa ya sa zuciyar shi karyewa. Baffa bai hana shi kuka ba sai bashi baki da yayi tayi.

"'Yan uwanka basu samu zuwa ba saboda Maimoon babu lafiya. Sunce basu same ka a waya ba."

"Allah sarki Allah Ya bata lafiya," wayar shi cikin tashin hankali jiya wani ya zareta daga aljihun shi.

Baffa ya kira su da wayar shi ya ba Ashmaan su ka yi mai gaisuwa da jaje.

Kwanan su Baffa biyu a garin Kaduna. Gidan Baffa dake garin wanda suka fara zama a baya su Mommy suka koma. Baffa ya ida gina gidan da kudin da 'yan uwan shi ke sa mai a account na matsayin albashi. Dama niyar shi ya saka 'yan haya. Kafin ya baro garin saida ya tabbatar an saka duk wani abu da za a bukata a gidan, sannan ya bada aka yi siyo musu kaya (ready made) tunda ko kyalle basu tsira da shi ba.

Ranan Alhaji Bello da Hajiya Suwaiba sun yi kuka da idanunsu, tsantsar nadama ta lullube su. Dama baka taba gane mai kaunar ka tsakani da Allah sai ka shiga mawuyacin hali. Wanda kake tsammanin zasu taimaka maka su suke fara janye jikin su.

Wani irin wulakanci ne basu yi wa bayin Allah nan ba amma yau su suka fitar dasu daga cikin kangin da suka tsinci kan su.

Tabbas mutane masu irin zuciyar Muhammad da Rabi kadan ne a duniya.

Wannan abu da ya faru da su ya tabbatar musu cewa wadata ta Allah ce. Shi ke badawa duk sanda Ya so kuma shi ke karba a duk sanda Ya so. Ba wayo ko dubarar ka yasa ka samu dukiya ko yaran da kake dasu ba. Allah ne Ya so Ya baka kuma zai iya karba a duk lokacin da Ya so.

Kafin ya tafi Baffa ya damkawa Ashmaan kudi su yi harkokin yau da kullum. Ya rasa da kalaman da zaiyi amfani wurin godewa Baffa.

Baffa ya girgiza kai yace, "Ashmaan ka yi mun fiye da haka."

Bayan komawarsu Abuja Baffa ya samu 'yan uwan shi ya nemi shawarar abunda ya kamata yayi domin taimakawa Bello.

"Na dandana shigen rayuwar, bana fata kowa yayi ta."

Nasir da Abdullahi sun yaba halin dattako irin na Baffa. Mutum na gari mai saka sharri da alkhairi. Sun yanke shawarar saka hannu jari a kamfanin Bello saidai duk wani kadara da aka samu ta gurbataciyar hanya banda su. Sannan kuma Ashmaan an bashi aiki a Lamido Homes.

Da Bello ya ji wannan abu yayi kuka, kuka mai cike da nadama da da nasani kukan da bai taba yin irin shi ba tunda ya ke. A motar haya shi da Suwaiba suka shirya suka je Abuja yi musu godiya.

Hajiya Suwaiba duniya tayi mata karatun ta natsu. Ta kara girgiza ganin irin daular da suke rayuwa a ciki.

Tabbas duniyan nan juyi-juyi ce, yau kaine gobe ba kaine ba.


***



Cikin aminci Maimoon ta cigaba da rainon cikinta. Cikin na da wata bakwai da rabi aka samu matsalar da dole sai anyi mata CS take yanke.

Sayfullah ya tsinci kan shi cikin fargaba da tashin hankali. A masallacin da ke asibitin yayi salla ya kaiwa Allah kukan shi.

Karfe tara na dare a ranan juma'a aka ciro kyakkyawar diyar Sayfullah da Maimoon. Uwa da 'yar duka suna cikin koshin lafiya.

Sayfullah ya fara shiga dakin haihuwar. Kai tsaye wurin Noor dinsa ya isa. A hankali ya rungumeta yana jin kaunar ta na karuwa a zuciyar shi. A hankali ya janye ya kalleta suka sakarwa juna murmushi. Ya duka ya sumabaci goshinta.

"Allah Yayi miki albarka Raihanatul Qalb."

Nurse din ta miko musu diyar su nannade a shawl. Sayf ya rukota a hankali yana kallon fuskarta idon shi cike da hawayen farin ciki.

Da Maimoon zata iya tsaida lokaci da tayi. Tasbihi kawai take yi a zuciya. Allah abun godiya. Ta kasa dauke idonta daga kan mijinta da 'yar ta.

"She's beautiful," Sayf yace yana kallon Maimoon. "Just like you."

Dr. Zainab ta shigo tace Maimoon na bukatar hutu dan haka Sayfullah ya fita dauke da 'yar shi.

Mami ta fara karbanta tana hamdala. Asibitin babu kowa sai su, duk wani makusanci nasu banda iyaye maza na wurin. Haka aka rika daukan babyn.

Kwanan su uku aka sallameta. A gidan Mami zata yi zaman jegon kaman yanda suka yi shawara.

Bayan sati biyu yarinya taci sunan Mami Fatima amma za a kirata Batool. Mami taji dadin karamcin da Sayf yayi mata aiko ta nuna bajintarta sosai.

Baby Batool tayi goshi Masha Allah. Kakaninta kaman masu gasa musamman Ammi da Baba Abdur-Rahman.

Batool 'yar gata ce, yar gaban goshin kowa musamman babanta. Washegarin suna Sayfullah yazo da dare. Falon sama ya hau tare suka ci abincin dare Batool a hannushi yaki ya ajiyeta.

"Oh Allah, to ka ajiyeta ka ci abincin mana."

"Babu ruwanki," yace ba tare da ya dago ya kalleta ba.

Maimoon ta girgiza kai tana murmushi. Tana samun kulawa wurin Mami, iya kular da za'a yi mata kenan a gidansu. Kafin ta nemi abu an kawo mata harda wanda bata da bukata. Wata dattijuwa ke yi mata wankan jego Batool kuwa Mami ke wanketa safe da yamma ta gasa mata cibiya.

"Kai!" Sayf yace da karfi. "Noor meye wannan?"

Gabanta ya fadi ta koma kusa da shi. "Mai ya faru?"

"Hujin kunne na gani. Yanzu saboda Allah karamar yarinyar nan za'a bulawa kunne wannan ai mugunta ne. Shi yasa naji tana kuka dazu kenan. Waye yayi mata hujin inje in ji dalili. Ke kina me kika bari aka yiwa 'ya ta wannan ketar."

"Gani sai kaji dalili," Muryar Mami ta daki kunnuwansu. "Ni nayi mata, ni ce muguwar kenan Sayfullah."

Sayf ya zaro ido. "Mami ni ban ce ba..."

"Eh mana mara kunya...."

Kunya ta lullube shi ya mika Batool wurin mamanta ya fita da sauri Maimoon na tayi mai dariya.

A haka har tayi arba'in. A lokacin ne kuma Sayfullah ya kekeshe ido yace a bashi matar shi. Bai ma sanar da Mami ba dan ya san hanawa zata yi dan haka Baba Ahmed ya samu. Bayan sun je yawon arba'in—har Katsina kuwa—a maimakon ya maidata gidan Mami yayi gida abun shi.

Ya ko sha mita wurin Mami amma ko a jikin shi.

Sayfullah da Maimoon sun koma gida inda su ka cigaba da rainon diyar su tare. Sannan kuma aka bude sabon shafin soyayya.

Basu da abin cewa sai Alhamdulillah!









BAYAN WASU SHEKARU




Shekaru da dama sun shude, abubuwa da dama sun faru wasu na farin ciki wasu akasin shi. Habiba sarkin boko tayi aure tana zaune a Kaduna. Sai hadin da yazo wa kowa a bazata amma anyi farin ciki sosai, Waahidah da Hassan.

Maimoon ta kammala digiri dinta sannan kasuwancinta sai bunkasa yake yi. Yanzu haka tana da manyan shaguna a garin Abuja da wasu jahohi a Najeriya sannan duk inda aka bincika ko bata da shago to akwai (distributor).

Zaman aure dama zo mu zauna zo mu saba ne. Babu auren da yake cikakke (perfect) amma hakan baya nufin ma'auratan basa cikin farin ciki. Duk yanda rayuwa tazo musu muddun suna da juna babu abunda zai same su.

Batool nada shekara hudu ta haifo danta sunkucece da ya ci sunan Baffa. Muhammad yanzu yana da wata takwas. Baffa yace ya yafe ba sai an boye sunan ba.

Maimoon na zaune tana shirin wani seminar da aka gayyace ta jiyo sallamar Mimi.

Bata yi tsammanin zuwanta ba taji dadin ganinta sosai. Dama ta gaji da kakalo turanci.

"Ina Sadiya?" Maimoon ta tambaya bayan ta kawo maga ruwa.

"Bata san nan zan zo ba."

Kai ta gyada suka yi hirar su har Maimoon taje ta dauko abayoyi Mimi ta taya ta zaban wanda zata sa ranan seminar din. Mimi ta zaban mata wata silver mara hayaniya sannan ta zaban mata (purple) niqab da zai shiga da rigar.

Bayan sun gama wannan Mimi ta dubi yayarta. "Adda ina so muyi magana dake amma dan Allah kafin in fada miki ina so ki zama open minded."

"Mimi kina bani tsoro. Menene?"

Mimi tayi ajiyar zuciya. "Ban san ta ya zan fada miki ba," tace tana cizon lebe. Sauke ajiyar zuciya ta sake yi. "Hamma Ashmaan yana so ya turo amma ban san ta yanda zan fara samun su Ummi ba ban san ya zasu dauki abun ba."

"Hamma Ashmaan?" Maimoon tace tana kallonta cike da mamaki. "Tun yaushe?"

"Nima ban sani ba Adda. Mun dai fara magana tun bayan rasuwar su Fauziya daga nan kuma...Adda kiyi hakuri. Wallahi na kasa zuwa in fada miki saboda ina tsoro."

An dade! Tace a zuciya sannan tayi murmushi ta kamo hannun Mimi. "Me yasa kike tsoro Mimi. Kar ki sake mun haka. Idan baki fada mun ba wa zaki fadawa?"

Mimi ta sadda kanta kasa. "Ina fargaban ya zaki dauki abun."

"Kina son shi?" Ta gyada kai. "Yana son ki?" Nan ma ta sake gyada kai. "Shikenan magana ta kare ai Mimi. Kada ki damu zan samu Ummi da kaina."

Tabbas taji dadin wannan al'amari. Kanwarta tayi dace domin Hamma Ashmaan mutumin kirki ne. Sannan tasan wannan karon ba za a samu wata matsala ba dan Alhaji Bello da Hajiya Suwaiba duniya ta koya musu darasi.

Bayan Baffa yasa hannu jari a kamfanin Daddy abubuwa sun cigaban musu amma fa ba kaman da. Yanzu za a iya cewa dai suna da rufin asirin su daidai gwargwado.

"Nagode Adda. Ba kiji haushi ba?"

"Haushin me?" Tayi dariya. "Ki cire wannan a ranki, ki dauka bai taba faruwa ba." Ta kan manta da wani abu ya taba shiga tsakaninta da shi a baya saboda Sayfullah tuni ya mamaye lungu da sako na zuciyarta.

***

"Baba nayi kyau?" Batool ta tambaya tana juyi gaban babanta. Mamanta tayi mata wanka tana cikin yi wa Muhammad ta gudo bayan ta dauko kayan barci daban daban ta saka.

"Wow! Sosai princess!"

Batool tayi tsalle ta dane cinyar babanta. "Baba bani labarin yanda ka hadu da Mamaa."

Sayf ya zaro ido. "Mamina wannan tambayar daga ina?" Batool ta dage kafada.

Kafin ya bata amsa Maimoon ta fito dauke da Muhammad. Shekaru sun shude amma kullum Raihanatul Qalb din shi kara kyau take yi.

"Fatima Batool. Oya wuce muje ki kwanta."

"Ni Baba zai kaini daki." Batool tace tana makale wuyar Sayf.

Tare suka kaita dakinta sannan suka nufi nasu dakin. Maimoon ta kwantar da Muhammad a cikin gadon shi na jarirai. Tuni Sayf ya gama shirin barci yana zaune kan gado ya mike kafa.

Bayan ta gama sa kaya ta feshe jikinta da turare. Daga nan ta haye gado. "Baka ba Batool amsa ba. Dama kullum Ammah sai tayi maka chanchakwato baka bata ladar hadamu da tayi ba."

"Ai ba ita ta hada mu ba akwai dai sa hannunta. Amman ko da bata aike ni wurin ki ba zamu hadu infact kafin Ammah ta aike ni already na san ki."

"Ka san ni?" Maimoon ta ce cike da mamaki. "Ni din? Ina ka san ni?"

Sayfullah yayi dariya yana janyota jikin shi. "Matso kusa in baki labarin yanda naga idanuwan da suka juya mun duniya gaba ɗaya....."




KARSHE.

















ALHAMDULILLAH! Allah na gode maka da Ka kawo mu karshen littafin nan.

It has been a minute yeah?🤭

Na gode, na gode! Na gode da kasancewar ku tare dani tun daga farko. Allah Ya bar mun ku💕

Do leave a review. Thank you.




Ma'asalam
Maymunatu Bukar💕

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro