Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

BABI NA GOMA SHA UKU











~~BABI NA GOMA SHA UKU~~












Rabon da tayi dariya haka har ta manta, cikinta har wani daurewa yayi ga hawaye na zuba daga idanunta saboda tsabar dariya. Duk yanda taso dannewa ta kasa saida akayi da ita.

"Ammah yanzu har ɗaki kuka bita?" Ahlaam ta tambaya murya na rawa saboda dariya.

"Har ƙasan gadon tsohuwarta kuwa. Har mu za'awa sharrin satar gyada? Gyada fa! Daga ranan aka kiyaye mu a garin nan."

Kai Maimoon da girgiza na sake gimtse dariyarta. Ta ɗaɗe bata haɗu da mutum mai ban dariya kaman Ammah. Tunda tazo gidan kawai taji tsohuwar tayi mata. Gata da faran-faran da son mutane. Sai taji ina ma ace haka suke mu'amala da Inna.

Kaman yanda Adda Salma tace mata, washegari tazo ta dauke da safe wurin sha ɗaya. A hanya Adda Salma ke fada mata dangantakar su da Ammah. Ashe ba dangantakar jini bace kaman yanda tayi zato. Mijin Adda Salma, Habib ne abokin jikan Amma, wato Sayf. Tun suna yare suke tare har izuwa yanzu.

Abun ya ba Maimoon matuƙar mamaki. Ashe dama akwai mutanen da suke daraja abokantaka haka? Wasu kam ƴan uwantaka na jini ma sun kasa riƙewa balle aje wani abuta. Ko dayake da yawa sunfi ba abokai mahimmanci akan ƴan uwansu.

Sun isa wani katafaren gida da ya so tsorata Maimoon. Gidane babba na alfarma, gidan da ya amsa sunan shi gida. Idanu kawai ta zuba tana kallo ikon Allah. Irin gidajen da ake ce ma aljannar duniya. Abunda ya fi burgeta shine inda ko ina yake kore da bishiyoyi da fulawowi.

Ba cikin main building din suka shiga ba. Wani sashe ne daban dake gefe sai dai shi ba gidan sama ne ba kaman wancan.

Wata matashiya suke iske a kofan shiga inda ta sanar dasu Ammah na ciki. Sun same ta zaune cikin falonta da ya ƙayatu da kayan alatu na zamani, tana zaune kan kujera tana kallon tashar Sunnah TV. Tana ganin su murmushi ya bayyana a fuskarta, suka gaisa sosai cikin sakin fuska. Daga gani akwai shaƙuwa sosai tsakanin ta da su Adda Salma, dan su Amira suna shigowa suka haye ta.

Yanda ta tarbi Adda Salma, haka ta tarbi Maimoon. Abun ya bata mamaki kwarai. Ammah doguwace sosai duk da dai ta dan tankware saboda shekaru, jikinta a mulmule yake, sai sheki yake yi kaman ba na tsohuwa ba.

Tunda suka zauna in banda sasu dariya babu abunda Ammah keyi. Bayan an gama gaisawa, Maimoon ta fara mata kitso. Kaman sauran jikinta, shima a gyare yake tsatsap dashi. Daga gani ana ji da wannan tsohuwa.

Basu ɗaɗe ta fara kitson ba wata matshiya da bazata wuce sa'ar Maimoon din ba ta shigo. Doguwace itama, tana ɗan haske kaɗan. Sunanta Ahlaam kaman yanda taji Ammah ta kirata. Kaman yanda Ammah take da sakin fuska, itama haka take. Zama tayi aka dasa hirar da ita.

Ita dai Maimoon iyakarta murmushi, sai kuma in Ammah ta ce mata "ko ba haka ba Munari?" Sai tace mata, "haka ne Ammah."

A cikin hirar ne Ammah ta dauko labarin kuruciyar da inda take basu labarin wata yarinya da ta mush sharri ita a ƙawarta.

"Ammah ai ko mutuwa na jin kunyar idon mahaifiya." Inji Adda Salma.

"Hakane. Amma mu ranar kam bamu ji ba."

"Sai me ya faru?" Ahlaam ta tambayi kakarta.

Ammah zama ta dan gyara, haka ya sa Maimoon ta sakan mata kan da ta zauna da kyau. Bayan ta gyara zama Maimoon ta cigaba da yi mata kitso. Kitson hannu take mata duka baya kaman yanda ta buƙata.

"Har gida Innan su ta kawo ƙarar mu. Mun sha faɗa kam amma ko ma meye mun dai buga. Daga ranan babu yarinyar da ta ƙara neman faɗa wurin mu."

Suna ta hira har Maimoon ta gama ma Ammah kitso. Gashinta da yanzu ya cika da furfura yayi kyau sai sheƙi yake.

"Kai Masha Allah," Ammah tace tana kallon madubin da Ahlaam ta kawo mata. "Gaskiya kitson nan yayi kyau. Inaga ba'a taɓa mun kiston da yayi kyau haka ba. Sannu kinji Munari."

"Yawwa," Maimoon ta amsa da murmushinta.

"Gaskiya kam Ammah ba'a taɓa miki kitso irin haka ba," Ahlaam tace. "Kinga kanki kaman ba na tsohuwa ba."

Daƙuwa Ammah ta mata. "Zuwaira ce tsohuwa."

Dariya kawai Ahlaam tayi, sannan tace. "Da nace bazanyi kitson ba amma na fasa."

Zare dankwalinta tayi, ta zauna inda Ammah ta tashi. Bayan Maimoon ta tambayi wani iri za'a mata sannan ta fara mata kitson. Nan da nan kuwa ta gama mata da yake kan baida cika sosai.

"Yau Hamma Sayf sai ya bani kyauta, nayi kitso." Ahlaam tace tana kallon kanta a waya inda ta bude camera. "Sannu. Nagode sosai Maimoon."

Murmushi Maimoon ta maida mata. Su kam babu ruwan su, sun burgeta sosai. Ko da suka tashi tafiya, Ammah cewa tayi su zauna sai sunci abinci. Nan aka cika gabansu da kayan cima kala daban daban.

Da suka tashi tafiya kuma Ammah ta dauko kuɗi ta ba Maimoon. Tana ganin su ta san sunyi yawa, sunfi ƙarfin kitson da tayi. Kai ta fara girgizawa. "Ammah kuɗin nan sunyi yawa."

"A'a, a'a, kar muyi haka da ke. Duk wanda yazo mun kitso haka nake biya. Na ba wanda basu kai ki kwarewa ba ma balle ke. Ki amsa kawai, bana son musu."

"Toh, Ammah," Maimoon ta amsa a sanyaye. "Nagode."

"Yauwa ƴar albarka. Sai ki ba Ahalan lambar wayar ki ko."

"Ahlaam fa nake ba Ahalan ba," Ahlaam tace tana dan turo baki gaba.

"Ke dan Allah raba ni. Laifin iyayen ku ne ai. A sa muku suna irin na mutane ba za'a sa ba. Sai aje chan a dauko wasu sunayen da mutum ba iya faɗi zaiyi ba balle ya rike."

Dariya dukkan su sukayi. Ko Ikram ma Karima take ce mata

Adda Salma ta fara mikewa, itama ta tashi. "Ammah, mu zamu tafi."

"Toh Salamatu. Mun gode, Allah Ya bar zumunci. Dan Allah kar a dinga ɗaɗewa ba'a leko mu ba."

Murmushi Adda Salma tayi, tana jin kunya. "In sha Allahu."

Har mota Ahlaam ta raka su.

"Mama bata dawo ba ko?" Adda Salma ta tambaya. Kai Ahlaam ta girgiza. "In ta dawo dan Allah ki gaishe ta."

Sallama sukayi, Ikram da Amira sunata daga mata hannu har motar su ta bar gidan. Shiru ne ya ratsa cikin motan.

Idonta na kan titi, tana kallon yanda mutane ke kai kawo. Wani tsoho ta gani ta dako a kai, sai zufe yakeyi, daga gani kasan a gajiye ya kai. Girgiza kai tayi, tana addu'a Allah Ya ba shi duk abunda ya fito nema. Lallai neman halal da wuya.

Dauke idonta tayi daga nan ta maida su kan Adda Salma dake tuki. "Suna da kirki sosai."

Murmushi Adda Salman tayi, idonta a kan titi. "Sosai ma kuwa. Mutane irin Ammah kaɗan suka rage a duniyan nan. Akwai ta da halin girma. She's so nice, bata dau duniya a kan komai ma. Tana ba ko wani dan Adam ta haɗu da shi girman shi. Ga kyauta. Ga mu'amala da mutane da kyau. Ga ruko da addini. Tana burge ni sosai."

Murmushi Maimoon tayi tana jinjina kai.

"Ta dauke ni kaman jikarta, abun na mun dadi sosai. Ban san ko ɗaya daga cikin kakanni na ba. Amma Ammah ta maye mun gurbin su. Tun kafin muyi aure da Baban Ikram muke zumunci. In fact bayan ya kaini na gaida iyayen shi, wurin Ammah ya kaini next."

Lallai duk yanda kayi zaton wani al'amari ya bace akwai wanda suna nan basu kauce hanya ba. Daga abota tsakanin mutane biyu, ji irin zumuncin da aka kulla. Tana fata itama su daure kaman haka da nata ƙawayen. Sun matukar burgeta, mutumin da ya rike zumunci haka tabbas ba zai yarda yan uwanshi ba.



***

Zaune yake kan gado ya faɗa duniyar tunani. Tunanin yanda zai shawo kan matsalar da yake fuskanta yake yi. Ya san yana da babban aiki a gaban shi amma ya ɗauki alƙawari bazai karaya ba. Dan a yanda yake hangowa ya san yana gwagwarmaya ba kaɗan ba a gaban shi.

Yana nan zaune wayar shi tayi ƙara. Ganin sunan Mommy a kan fuskar wayan ya sa yayi saurin amsawa.

"Ashmaan kana ina?"

"Ina daki."

"To same ni a ɗaki na."

Bata jira ya sake cewa komai ba ta kashe wayarta. Dan jim yayi, yana tunanin ko me take so. Tashi yayi ya zura farar jallabiyar shi sannan ya fita dan amsa kiran mahaifiyar shi.

A palo ya samu ƙannen shi duka a zaune. Abun mamaki ɗan bai cika ganin su a wuri ɗaya haka ba. Asalima ko wacce na ɗakinta babu ruwan kowa da kowa.

A tare suka gaishe shi, ya amsa cike da fara'a. "Wace wainar ake tuyawa a nan?"

Dariya sukayi, Jasrah ta ce mai wani series suke kallo. Ayi kallo lafiya ya musu sannan ya ƙarasa ɗakin Mommy.

A kan kujera ya sameta tana waya. Wuri ya samu ya zauna a ƙasa har ta gama. Juyowa tayi kalle shi murmushi a kan fuskarta.

Shima murmushin ya maida mata. "Mommy ina wuni?"

"Lafiya ƙalau Ashmaan, ya aiki?"

"Aiki alhamdulillah."

"Masha Allah, Allah Ya bada sa'a, Ya kade fitina, Ya sa a samu abunda aka je nema."

Cike da farin ciki Ashmaan ya amsa da Ameen. Addu'an Mommy ba ƙaramin faranta mai rai yayi ba. Sai gashi sun ɓige da yin abunda suka ɗaɗe basuyi ba.

Sosai suka ɗaɗe suna hira, Ashmaan kaman ya zuba ruwa a ƙasa ya sha dan farin ciki. Ina ma a ce ko da yaushe hake suke zama? Da yafi kowa gata a duniya. So dayawa yana son zama kusa da mahaifiyar shi haka. Sai dai bambancin ra'ayoyinsu a kan abubuwa da dama ke hana shi.

"Ashmaan,"

Yanayin da ta kira sunanshi da shi ya sa shi gyara zama, ya tattaro dukan nutsuwar shi ya miƙa mata.

"Na'am Mommy."

"Ina so ka saurare ni da kyau da kunnen basira."

Gaɓan shi ne ya faɗi jin furucinta, a zuciya yana addu'ar Allah Ya sa ba wani abun da zai zamo mai matsala ne ba.

"Akwai ƴar gidan ƙawata Hajiya Saudatu...."

Zuciyarshi yaji ta tsinke.

"Na yaba da hankalin yarinyan. Tana da nutsuwa da kamun kai. Ina so kaje ku gana da ita."

Wani abu yaji ya tsaya mai a maƙogwaro. Duk sanyin ɗakin ji yayi zufa na keto mai.

"Toh Mommy, amma..."

"Amma me? Ka ga Ashmaan bance kaje na maka mata ba, cewa nayi kaje ka gani in kun dadaita."

Boyayyar ajiyar zuciya ya saki. Da to ya ƙara amsa mata sannan yayi maza ya bar ɗakin. Chan ƙasan ran shi ya san mace ɗaya ce a duniya zai iya mallakawa zuciyar shi.





Hamma kana da aiki ja a gaban ka kam.



Maymunatu Bukar💕

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro