Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

BABI NA ARBA'IN DA BIYU





~
BABI NA ARBA'IN DA BIYU
~











"Total din ki zai kama dubu takwas kenan," Maimoon ta ce da murmushi a fuskarta dukda matar bata ganin haka.

"Wani banki zan yi transfer?"

Takarda da ke dauke da lambar akant, suna, da kuma sunan banki ta miƙa mata.

"Na tura," matar ta sanar da ita. "Nagode sosai. Tun kafin in shafa ma kamshin ya rike mun kaya. Allah Ya kawo kasuwa mai albarka."

"Ameen, nima nagode." Itama ta yi mata murmushi.

Gyara zaman kwalaben turaren ta yi akan teburin da ta jera su akai. Ko wani kaso akwai takarda dauke da suna da kuma farashin turaren.

An kwashe fiye da rabin kayan da ta zo da su. Bata taba tsammanin haka ba. Mimi da Sadiya kam komai da su ka kawo har ya kare. Abun dai masha Allah gwanin ban sha'awa.

Wurin cike ya ke da mutane kowa ya baza hajar shi ana ta saye da sayarwa. Duk girman wurin amma an cika shi dam! Da ya ke (vendors) sun zo da wuri dan su kafa rumfunansu, har ta na tunani anya za'a cika wurin? Ashe ashe!

Kaman wasa Mimi ta nuna mata za'ayi wani (trade show) BizBazaar a nan cikin wani wurin taro a Garki ko za su hada kudi su siya (stall) daya. Da kaman ba za ta yi ba daga baya kuma ta ce toh su gwada su gani.

Bayan kudin (stall), bata sake siyan komai ba. Dama tana da kayan aiki, su robobi, (stickers) da ledoji. Tun wanda su ka siya da Anwara dawowar su hutu ba su kare ba. Turare kuma wanda ta hada tun lokacin ne ta fito da su. Sun jiku sun kara kamshi.

Jiya basu yi barci ba ana ta shirye-shirye. Sadiya da Mimi sun yi gullisuwa, tuwon madara, iloka da sauran su an kulla a leda, wasu kuma sun zuba a roba kowanne da farashi jiki. Nanah da Waahida suka taya Maimoon sa turare a roba, itama (sizes) daban-daban sai humra shima aka dura wasu a roba wasu a kwalba.

Cikin ikon Allah suna gama jera abubuwa mutane su ka fara taruwa. Abunka da turare ko mutum ba zai siya ba za'a goga mai ya ji kamshi.

Ji ta yi kafafuwanta sun fara gajiya saboda tsayuwa, dan haka ta janyo kujera ta zauna. Niqabinta ta dan daga kadan domin ta sha ruwa, makogwaronta ya bushe.

'Yan kannenta sun tafi zagaye wuri tun dazu basu dawo ba. Ganin kafa ta dauke a wurin su ta fito da wayarta. Ta iske sakonni rututu daga group din da Habiba ta hada. Saboda rashin mutunci sunan group din 'Sayfullah ya yi wuf da Maimoon'. Sau uku tana chanzawa Habiba na maidawa daga karshe dai ta kyaleta dan bata da lokacin ta.

Daga su Habiba sai 'yan uwanta a group din. Maganar anko su ke yi shine su ka tara daruruwan messages haka. Ta fara bin chat din ta na karantawa taga ina ba zata iya ba.

Ko wa ya ce musu zata yi anko ma? Ohon musu. Ita duk harkar takura bata fiye so ba, kowa kawai ya sa kayan da Allah Ya hore mai.

Wai maganan aurenta ake yi. Allah mai iko!

Shekaran da ta gabata da wani ya ce mata za ta yi aure nan kusa da ta ce mai baya da hankali. Amma Allah mai yanda Ya so itace cikin kankanin lokaci ta hadu da wani har suka sasanta aka kai gabar aure.

Ta yi zurfi sosai a tunani bata lura da mutumin da ke tsaye ba saida ya yi gyaran murya. Kiftawa ta yi ta daga kai. Ganin shi ya sa ta zaro ido, sam bata yi zaton dagaske ya ke ba da ya ce zai zo.

Sayfullah ne tsaye ya sha farar shadda sai kyalli ta ke yi, ga hularsa zanna kalar kasa mai duhu zauna das a kansa. Gilashinan nashi na nan makale a fuskarsa kaman kullum.

"Hajiya mai turare tunanin me kike yi haka? In dai ni ne to gani na iso. Nazo in rike jakar kudin yanda za'a ji dadin rabawa da ni."

Murmushi ta yi cikinta ya na wani iri kaman abubuwa na yawo a ciki. Zagayawa ya yi, turarensa ya daki hancinta da ya matso bata san lokacin da ta zuƙa lumfashi mai ba. Tana son kamshin turaren sosai. Wata rana dai zata daure ta tambayesa wani iri ne amma dai a yanzu zata cigaba da jin dadin kamshin.

Sayfullah na daya daga cikin dalilin da ya sa ta yarda su siya (stall) din. Kamar yadda ya yi alƙawari, yana ba ta shawarwarin yadda za ta tafiyar da harkokin kasuwancinta. Kuma hakan ba karamin taimaka mata ya ke yi ba.

Suna cikin hira wata mata 'yar dattijuwa ta tsaya duba turare. Kafin ta mike har ya yi. Cike da sha'awa take kallon yanda ya ke tallata kayan har sai da ya sa matar ta siya turaren wuta kala biyar da humra uku.

"A ina shagon ku yake?" Ta tambaya bayan ta mika mai kudin.

"Eh toh a yanzu dai bamu da shago muna gudanar da komai online ne. Muna delivery ko ina a fadin Najeriya har kasashen waje idan ana bukata. Kuma nan ba da dadewa ba in sha Allah zamu bude shago."

Kai matar ta gyda alamun ta gamsu da bayanan sa. Bayan matar ta tafi ya juyo dauke da murmushi a fuskarsa.

"Hajiya mai turare da fatan na yi convincing din ki ki dauke ni aiki."

Itama da murmushinta ta ce; "Sosai ma kuwa. Amma kai da wa zaku bude shago?"

"Ban gane ni da wa zamu bude shago ba," ya ce harda harara. "Ni da ke mana. In fact ba Abuja kadai ba, nationwide zamu bude."

"Allah Ya taimaka."

"Ameen. Ke dai ki tsaya ki gani."

Kafin ya zauna wasu mata su uku su ka zo, sai ya fasa zaman ya ji me su ke so.

Maimoon ta kankance ido ganin yanda daya a cikin su ta dage tana rangwada sai wani kifta ido ta ke yi kaman sabuwar makauniya. Yanzu za ta kwakwalewa yarinyan mutane ido idan ba ta yi hankali ba.

Ganin abun yana nema ya wuce gona da iri ta mike tsaye su ga tsawonta.

"Ga madam nan ta yi muku ƙarin bayani."

Taso babu niqabi a fuskarta suga yanda ta murtuke ko zasu shiga taitayin su. Ko shafa musu (samples) din bata yi ba. Daga karshe dai ko daya basu siya ba suka bige da tambayan Instagram handle.

Yara sam yanzu ba su da kunya. Harda laifin shi ai shima da ya je yana washe musu hakora.

"Noor saki fuskarki hakanan mana." Sayf ya ce yana dariya.

Bata san lokacin da ta maka mai harara ba. Hakan ya sa ya fashe da dariya. Lallai ma! Wato dariya ta bashi ko? Zai sani!

"Kwantar da hankalinki Rayhanatul Qalb. In ba ke ba sai rijiya."

Hmn! Za'a yi mata dadin baki wai ita ce kamshin zuciya. Dukda dai hakan ya yi tasiri akanta.

"Yauwa, ko ke fa. Ki daina frowning fuskarki, zai sa ki yi wrinkles kuma saura wata hudu biki."

Oh Allah! Ina ma kasa zata bude ta nutse. Ya rantse sai ya sa ta jin kunya yau.

Sayf ya koma ya jingina da kujerar ya na murmushi. She has the most expressive eyes ever! Idanunta ba su taba iya boye abunda ke cikin zuciyarta.

Watanni hudu da suka rage jin su ya ke yi kaman shekaru aru-aru. Shirye-shirye kuwa tuni aka fara tun kafin ma a sa rana. Mami ce mai hada kayan lefe. Shi dai na shi kawai ya mika kudi ya bar mata wuka da nama a hannu. Abu daya kawai ya ke so, shine a sa mata duk wani abu da zata bukata mai kyau da inganci. Mami wani lokacin ta kan nuna mai wasu kayan ta ce ya zaba.

Sai kuma wurin da za su zauna. Har yanzu ba'a samu ba amma anata dubawa.

Tunda ya bata kunya bata sake cewa komai ba. Duk hirararrakin su yawanci shi ke tsawaita maganan. Ita tafi yin shiru ta saurare shi. Dukda shima ba za'a ce mutum ne mai magana sosai ba amma ya fita.

Mutane na ta tsaya a rumfan suna duba turare da yawa kuma suna siya.

Ba da wasa ya ke ba da ya ce sun kusa bude shago. Tana burge shi da sana'an da take yi. Yana son mutum irin haka. Saboda haka zai yi iya bakin kokarin shi wurin karfafa mata, zai bata duk wani (support) da take bukata.

Tare Sayfullah da Maimoon suka saida sauran kayan. Kan kace me komai ya kare. Maimoon ta yi mamaki sosai. Bata taba zaton zata saida komai ba.

"Well done Noor," Sayf ya ce da murmushi a fuskarsa. "I'm so proud of you."

"Nagode," ta amsa tana sadda kai kasa.

Sayfullah ya bude baki zai yi magana Mimi, Sadiya da Wahidaah su ka dawo.

Maimoon ta rike kugu tana kallon su. "Yi hakuri Adda," Sadiya ta ce da sauri. "Mun hadu da kawayen mu ne bamu lura lokaci ya tafi ba ma. Yi hakuri mun bar ki ke kadai, duk da dai Hamma ya zo taya ki hira. Ina wuni Hamm Sayf."

Maganarta ya sa Sayf dariya. "Lafiya lau Sadiya."

Mimi da Wahidaah suma su ka gaida shi ya amsa cikin sakin fuska.

Su Sadiya su ka kwashe kayan suka kai motar Sayf. Dama za su kira a dauke su ne tunda Sayf ya zo shikenan.

A hanya suna ta labari, Sayf ma ya kan sa baki amma Wahidaah ta yi tsit kaman babu ita a motar. Maimoon ta kasa yin shiru, juyawa ta yi ta kalle ta ta ce, "Wahidaah duk gajiyan ce?"

Murmushi ta yi da ya fi kama da yaƙe. "Eh Adda, kaina ke ciwo."

Hakanan ta ji bata yarda da ita ba. "Allah Ya sawake, in munje gida sai a nemo magani."

Daga nan kuma motan ta yi shiru har su ka isa gida. Da sauri daya daga cikin masu gadin ya zo wurin, shi ya fitar da kayan daga cikin mota ya kai su bakin kofa inda su Sadiya su ka karasa shiga da kayan ciki.

Iyayensu maza sun yi tafiya shekaran jiya sun je seminar a Legas. Da kyar aka samu Baffa ya yarda ya bi su. Maman Anwara da Ummi kuma sun raka Jaddati asibiti check up saboda haka Ammi ce kadai a gidan.

Jira ta ke yi ya ce su shiga su gaida Ammi amma sai taga bawan Allah na kokarin shiga mota.

"Ba zaka shiga a gaisa ba?"

Sayf da har ya bude kofa ya juya ya kalleta. "Ba kin ce babu kowa a gidan ba?"

Kai ta girgiza. "Ammi na nan." Ta lura da yanda yanayin shi ya chanza. "Mu je?" Ta yi maganar a sigar tambaya. Wannan karon ba zai tafi ba shiga ya gaidata ba.

Saida ya dauki dan lokaci kafin ya ce, "Lead the way."

Murmushi ta yi mai sannan ta juya ta nufa bangaren Ammi ya na biye da ita a baya. Kamshin turaren wuta ya fara yi mata sallama. Ammi ma ba baya ba wurin son kamshi, ta yi wa Maimoon ciniki ba kadan ba.

A falo ta sameta zaune yafe da babban mayafi. Wahidaah da Maimoon bata san lokacin da ta taho nan ba na zaune a kasa kusa da mahaifiyarta.

Sallama ta yi bayan sun gaisa da Ammin ta na tambayanta ya kasawu Maimoon ta ce mata tare da Sayfullah su ke.

A take wani farin ciki ya mamaye illahirin fuskarta. "Yana ina?"

"Yana waje."

"Wahidaah tashi ki je ki shigo da yayanki, ina zuwa," ta ce kafin ta haye sama.

Kallo daya ta yi mai ta san a takure yake, ya shigo ne ba dan ran shi ya so ba. A kujerar da ke bakin kofa ya yi zaman shi ko cikin falon bai karaso ba.

Ammi da kanta ta kawo mai kayan marmari. Wahidaah na gani ta yi sauri ta karba ta kai mai gaban shi. Godiya ya yi mata dukda bai yi motsin daukan komai ba.

Ammi na zama ya sauko daga kan kujeran ya gaidata kaman yanda ya saba gaida ko wani babba, cike da ladabi. Amma bayan gaisuwan nan bai sake cewa komai ba sai dai ya amsa tambayan Ammi. Kaman ba wurin mahaifiyarsa ya zo ba.

Ammi kuwa ana ganinta ansan ta na cikin farin ciki sosai. Ita tayi ta jan shi da hira.

Mintin shi goma ya ce zai tafi. Har bakin kofa Ammi ta rako su. Maimoon ta zo fita ta mika mata wata leda. Bata ce komai amma Maimoon ta gane me ta ke nufi.

Tana tsaye ya bude mota ya shiga ya zauna kafar shi daya a waje. "Ni zan tafi."

"To. Nagode sosai. Allah Ya saka da alkhairi."

"Wa ye kike wa godiya haka?" Ya harareta. "Ni matsa in rufe kofa."

"Ba ka ce Ameen ba," ta ce tana dariya.

"Ameen Noor."

Ledan da Ammi ta bata ta mika mai. "Gashi in ji Ammi."

Karba ya yi ya ajiye a gefe. "Ki ce mata nagode."

"Ka dai kirata ka ce mata ka gode ni nawa delivery ne kawai."

Bai ce komai ba.

"Zaka kirata ko?" Ta tsare shi da idanu har saida ya yi ajiyar zuciya ya daga kai. "Zan kira."

"Promise?" Kai ya sake gyadawa. Hakan ya yi mata dadi. Murmushi mai fadi ta yi sannan su ka sake yin sallama.

Dakinta ta nufa ta watsa ruwa ta chanza kaya. Tana cikin danna waya taga alert ya shigo. Ta yi zaton na daya daga cikin matan da suka siya kaya dazu ne sai yanzu banki su ka ga daman tura mata message.

Saidai da ta bude ta ga sunan Sayfullah baroro. Da sauri ta kira shi.

"Raihantul Qalb?"

"Yanzu banki su ka yi mun wani odd message da sunan ka."

Dariya ya yi sosai. "Sannu Noor, wato odd message. Kudin turare ne."

"Turare? Wani turare kuma?"

"Turaren Mami da Nusayba."

Ai bata san lokacin da ta kira sunanshi ba. "Sayfullah!"

"Na'am, Raihantul Qalb."

"Ka turo in yi maka refunding. Me ya sa zaka turo kudi bayan gift na bada ka kai musu?"

"Haka ake bada gift? Aiko za ki karya jarin ki."

"Ni dai ka turo," ta ce tana turo baki gaba.

"Bazan turo ba. Shi yasa ban ce zan siya ba dan nasan ba za ki karba ba. Discussion closed."

Tasan ta yanda zata kama shi. "Ka kira Ammin ka yi mata godiyan da ka ce zaka yi?" Jin ya yi shiru ta san bai kira ba. "Habibi you promised fah?"

"Na sani Noor, zan kirata."

Daga nan kuma su ka fara hira abun su kaman ba dazu suka rabu ba.

Da daddare Maimoon na shirin kwanciya Wahidaah ta shigo. Da murmshi Maimoon ta ce mata ta shigo. A bakin gado ta zauna.

"Kin sha maganin kuwa?"

Kai kawai ta gyda mata.

"Wahidaah lafiya? Ko har yanzu kan ne."

Kai ta girgiza. "Mun gode Adda."

Ta saka Maimoon a duhu. "Kun gode? Ke da wa? Kuma godiyan me kuke yi."

"Ya Sayf ya kira Ammi. Ya zo wurinta kuma ya kirata duka a kwana daya. Ban taba ganinta haka ba, tana cikin farin ciki sosai. Saboda haka mun gode, ni da 'yan uwana."

"Wahidaah..."

"Ya Sayf...ban san ya zan fada miki ba amma he has always been aloof damu amma yau ya zo shi kadai har ya dade kuma ya kirata....abun is hard to believe. Kuma duka saboda ke ne Adda. Mun gode."

Wahidaah na da kananun shekaru amma yanda ta ke magana ya nuna tsananin hankalin da ke tattare da ita.

"Ki daina mun godiya Wahidaah. Ban yi komai."

"Ba ki san yanda Ammi ta dade ta na jiran wannan ranan ba shi ya sa ki ke gani ba ki yi komai ba."









I wrote this with my eyes closing saboda barci. Try to vote and comment please 🙏🏽


~Maymunatu Bukar 💕

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro