Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

BABI NA ARBA'IN DA BIYAR






~
BABI NA ARBA'IN DA BIYAR
~








A kwana a tashi babu wuya, kaman jiya ne aka sa rana amma lokacin har ya zo.

Manyan kawaye Habiba da Safara'u tun ana saura sati daya biki su ka iso garin. Tare da su aka karasa sauran shirye-shirye da ya rage.

Adda Salma, Anwara da Kydah ne (chief organizers), ita amarya kawai sai yanda aka yi da ita. Ta ce ma ba sai sun tambayeta ba duk abunda su ka ga ya dace su yi kawai. Adda ta ce hakan ba zai yiyu ba ai ba su bane amaren dolen ta rika sa baki kafin a yi (deciding) akan abu.

Ango Sayfullah farin ciki a wurinsa baya misaltuwa. Babban burinsa na mallakan Noor a matsayin abokiyar rayuwa ya kusa cika.

Da yawa kafin ya yanke hukunci ya kan nemi shawararta. Ganin haka itama ya sa ta yi koyi dashi. Daidai da dankunne da zata saka saida ya taya ta zaba.

Wata rana suna waya Sayfullah ya ce shi zai biya kudin komai daga kudin kaya zuwa dinki, kwalliya, lalle da sauran su. Maimoon kuma ta nuna maganan haka ma bai taso ba tunda Baffa ya bata kudi fiye da yanda zai isheta ma.

Ƙiyawar da ta yi ya ba Sayf haushi har ya so ya janyo sabani a tsakanin su. Daga karshe dai shi ya bada kudin lalle da kwalliya dukda ba haka ya so ba amma Noor din ta sa ta kafe ta ƙi yarda ya biya komai.

Cikin satin da ya gabata aka kawo kayan lefe. Babu abun cewa sai Masha Allah domin Sayfullah ya nuna bajintarsa. Komai an saka mata shi a wadace. Abun sai son barka.

Yau tunda suka tashi da asuba ba su koma ba ana ta hidima. Tun shekaran jiya su ka taho gidan Kydah tunda a nan za'a yi taron zai fi sauki.

Dukda yau ne (Henna party) din ita amarya tun jiya aka yi mata nata a tsanake. Ja kawai ta yi baki saboda yana ɗaye mata fata.

Kowa na kai kawo banda amarya da ke nannaɗe cikin bargo. Barci ta ke ji amma hayaniyan su ya hanata. Abu dai sai da yamma amma sun wani tashi da sassafe.

Daga sama ta ji an ɗaka mata duka a kan cinya. "Maimoon ki tashi ki shiga wanka."

Fitowa ta yi daga cikin bargon. "Kai Adda!"

"Tashi kowa ya yi wanka banda ke. Zanje kasuwa kafin in dawo kin yi wanka."

A lokacin ne wani barci mai daɗi ya ke nema ya yi gaba da ita. Dole ta mike dan idan Adda ta dawo ta sameta bata yi wankan ba zata sha faɗa. Ita kadai ce a dakin sai 'yan biyun Kydah da ke barci a gefenta.

Bayi ta shiga ta hada ruwan wanka ta zuba turaren da Hajiya Layla ta hada mata na musamman. Tuni bayin ya dauki ni'imtaccen kamshi.

Tsayawa ta yi tana kallon kanta a madubi. Babu karya ta sha gyara kam. Sadiya ta ce har wani 'glowing' ta ke yi. Ba ta dade a bayin ba ta fito daure da babban zani.

"Yauwa Maimoon, kin fito. Bari a kawo miki abinci ki ci mai kwalliya ta kusa zuwa." Kydah ta ce tana daukar Huda da Inas.

Har ta kai kofa ta juyo. "Yauwa Ya Sayf ya kira ki. Na dauka na ce mai kina wanka dan kar ya yi ta kira."

"To," Maimoon ta gyada kai.

An samu cigaba sosai har Kydah na amsa kiran Sayf. Da kaman ba su san juna ba amma saboda shirye-shiryen biki sun fara sakin jiki da juna. Wani lokacin da gangan Maimoon ke sa Kydah ta kira yayanta ta tambaye shi wani abun ko kuma ta tabbatar da wani abun musamman lokacin da ake gyara a gidan da zasu zauna.

Nanah ce ta kawo mata abinci. "Ina Habiba?"

"Tana chan tare da masu (decoration), in kirata ne?"

Kai ta girgiza. Bata shafa mai ba, riga kawai ta saka sannan ta zauna cin abinci.

Bayan sallan azahar mai kwalliya ta iso. Wata kawar Anwara ce ta hada su da ita. Wanke fuska ta je ta kara yi kafin ta zauna akan kujerar da suka zo da ita.

"Kin dai yi arwala ko?" Anwara ta tambaya. Kofin kankare ne a hannunta tana tauna kaman ta samu nama.

"Sai hakorin ki ya yi ciwo Anwara." Kydah ta ce mata. "Kina tauna kankara kaman sweet."

Anwara ba ta ce komai ba ta cigaba da tauna kankaranta har wani lumshe ido ta ke yi.

Duka su ka yi dariya Kydah ta girgiza kai ta ce. "Allah Ya shirya ki."

"Nima haka na rika shan kankara da ina da cikin (first born) dina," mai kwalliyar ta ce tana murmushi. "Amma ki yi kokarin saka abu a cikin ki ba ki yi ta shan kankara ba, kaman yanda 'yar uwar ki ta ce zai iya janyo miki ciwon hakori ko na maƙogaro."

"In sha Allah, nagode."

"Ba komai. Allah Ya raba lafiya."

"Ameen," Anwara ta amsa.

"Mara kunya," wata cousin din su ta ce tana dariya. "Mu ya kamata mu amsa ba ke ba. Oh, yaran yanzu babu kunya."

Mai kwalliya ta nemi da a bata waje zata fara aiki. Ba musu dukkan su su ka fita ya rage Habiba da Anwara ne kadai a dakin. Tun zuwan su Maimoon ta lura ta su ta zo daya.

Ba'a je ko ina da fara kwalliya ba Maimoon ta raina kanta, har ta gaji da zaman kuma babu alamun an kusa gamawa dan ko rabi ba'a yi ba.

A shafa wancan a goga wancan haka har aka yi awa daya ana abu daya. Lallai masu kwalliya ko da yaushe suna kokari ita kam wuyanta har ya kage.

Da aka zo saka (lashes) Maimoon ta ce sam bata yarda ba. Babu yanda mai kwalliyan bata yi ba ta ce a'a.

"Kina da idanu masu kyau,  (lashes) din zai kara fito da su."

Duk magiyar su haka su ka hakura. Bada ita ba za'a yi ƙarin gashi ba. Da yawa mutane ba su san saka lashes da saka attach a kai duk laifi daya bane.

Bayan an gama kwalliya aka hau gyaran gashi, shima nan an ci lokaci ba kadan ba.

Habiba da Anwara su ka taya ta ta saka riga. Leshi ne (baby pink) aka yi mata dinkin (simple bridal gown) da bai ja kasa ba kuma babu hayaniya an yi mai beadwork mai kyau.

"Tubarakallah Masha Allah! Wow! Adda Moon kin ganki kuwa."

Mai kwalliyan ta daura mata dankwali sannan ta yafa mata gyalen yanda ya kamata. Daga nan kuma ta dauki hoto duk da Maimoon din ta ce bata so ta yi posting.

Kowa ya shirya cikin ankon material (lilac) wanda duk yawanci doguwar riga su ka dinka.

Gidan ya cika da hayaniya dan tuni mutane su ka fara zuwa. Taron mata ne kadai kuma matasa banda iyaye.

Daga dakin su na jiyo muryar Adda Salma tana aikin MC. Kafin a fita da amarya saida su ka yi hoto da 'yan uwanta makusanta. Mimi harda nema ta saka ta kuka.

A tsakiya su ka saka ta aka fita da ita waje. Wurin ya yi kyau masu (decoration) sun yi kokari sosai. A gefe a ka yi wurin yin lalle shima jajayen carpet ne aka shirya a wurin sai 'yan kananan benchi da mutum zai daura hannu a kai.

Masu lallen sun iso har sun fara aikin su.




"Masha Allah ga amaryan mu nan ta fito. Tubarakallah Masha Allah." Muryar Adda Salma ta karade wurin.

Ba tare da bata lokaci ba aka fara gudanar da taron. An yi wa Maimoon kara sosai harda wanda ba ta yi zaton za su zo ba duk sun zo. Rukayya kawar ta da suka hadu a makaranta itama ta zo tun daga Zazzau. Ahlaam kanwar Sayf ma ta zo.

An ci, an sha, an yi raha an kuma dauki hoto sosai domin tarihi. Mai hoton ma da suka dauko mace ce.

Taro ya tafi sumul babu wani gargada kaman yanda su ka yi fata. Ba'a watse ba sai gab da Maghriba. Bayan nan kuma Sadiya, Nanah da Waahidah su ka bude wani sabon shafin. Su ka dage suna rawa abunsu.

Daga karshe Maimoon guduwa ciki ta yi ta bar su. So ta ke yi kawai ta cire kayan ta sha iska sun isheta kuma.

Bayan ta yi wanka ta tafi kicin neman abunda zata saka a ciki. A nan ta samu Kydah ta hado ta da snacks.

"Dama na san za ki nema shi ya sa na boye miki. Ni kam da bikina babu wanda ya yi hausar nan haka na gama hadiye miyau wurin event daga karshe ban ci komai ba."

Maimoon ta yi dariya. "Nagode Maman 'yan biyu."

Daki ta koma ta iske babu kowa. Hakan ya mata dadi dama so ta ke yi ta yi waya cikin kwanciyan hankali dan ba dama su ga tana waya sun rika tsokananta kenan.

Kaman yanda ya saba katse kiranta ya yi sannan ya kira da kansa.

"Raihanatul Qalb, irin wannan kyau haka! Tubarakallah Masha Allah."

Dariya ta yi ta san aikin daya daga cikin kannensa ne a cikin su za'a samu ta tura mai hoton. Tasan ba zai wuce Ahlaam ba dan taga alama itama irin su Sadiya ce akwai rawar kai.

"Kin yi kyau sosai."

Yanda ya furta maganan a hankali kaman ya na rada ya sata jin kunya sosai. "Nagode."

"Ina nan na kasa barci."

Kara kudundune kanta ta yi cikin bargo. "Saboda me?"

"Saboda na kosa gari ya waye. Kaman in janyo lokaci haka na ke ji. I can't wait for you to be mine."

Abubuwan da suka saba yawo a cikinta dinnan? Sun dawo! Kuma sun karu sosai.

"I feel the same way."

Saboda tsabar kunya bata tsaya jin abunda zai ce ba ta kashe wayar. Bai sake kiranta ba sai text da ya tura mata.

Gobe kaman haka kin tsufa da zama Mrs. Sayfullah. Allah Ya tashe mu lafiya Noor.

Da murmushi makale a fuskarta barci ya yi awon gaba da ita.






***






Da misalin karfe sha daya na safe darururuwan mutane su ka shaida daurin auren Dr.Sayfullah Abdur-Rahman Hambali da Maimoon Muhammad Lamido.

Baba Nasir ne waliyin amarya Baba Ahmad mijin Mami waliyin ango.

Farin ciki wurin ango Sayfullah baya misaltuwa. Harda kwallarsa da aka sanar da an daura. Nan da nan ya turawa matarsa kyakkyawan text.

Murmushin da ke fuskarsa bai gushe ba yayin da ya ke musabaha da mutane.

Habib ya sa hannunsa a kafadar sa. "Congratulations. Allah Ya baku zaman lafiya mai daurewa.

"Ameen Ameen. Nagode Habib."

Baya da abunda zai ce mai bayan wannan. Habib ya mai abubuwan da ba zai taba iya biyansa ba. Tabbas Habib mutum ne mai kirki da rike amana kuma yana alfahari da ya kasance amininsa wanda baya da tamkar shi duk duniya. Sun taso tare tun suna kanana har zuwa yau dangantakan su bata chanza ba sai ma karuwa da ta yi.

"Ango juyo a yi hoto." Hussain ya ce yana daga wayarsa.

Hannun Habib na kan kafadar Sayf aka dauki hoton. 'Yan biyu su ka saka ango a tsakiya suma aka dauka hoton.

Bayan an gama daukan hotuna aka nufi hall din da za'a yi (reception).

Alhamdulillah Sayf ya yi ta nanatawa a zuciya. Yau burinsa ya cika Maimoon ta zama matarsa ta sunnah kuma uwar 'ya'yan shi in Allah Ya yarda.






***




Mrs Sayfullah an daura. Allah Ya bamu zaman lafiya da hakurin zama da juna. Allah Ya albarkaci rayuwar auren mu.

"An daura!"

Nan da nan aka fara guda. Hawaye ne suka zubo mata a fuska. Duka yaushe ta ke tunani ba za ta taba samun wanda zai so ta ba, duka yaushe ta gama tunanin ita kam bata da rabo a duniya wata kila sai a lahira, yau ita ce aka daurawa aure.

Ba'a hana ta kuka ba dan an san kukan dadi ne. Da safe su ka dawo gida. Bayi ta shiga ta yi arwala dole ta mikawa Allah (SWT) godiyarta da ya nuna mata wannan rana mai cike da farin ciki.

Cikin kankanin lokaci Allah Ya sauya yanayin su daga kunci da rashin walwala zuwa farin ciki da annashuwa.

Ta dade a kan abun sallah tana addu'a. Bayan nan aka gyara mata fuska, yau ba zata yi kwalliya ba. Laffaya fari Adda Salma ta tayata nadawa.

Fuskarta a rufe Aunty Maryam ta kama mata hannu aka shiga cikin gida da ita. Bangaren Ammi aka fara kaita. Cike ya ke da mutane, 'yan uwan Ammi duk sun zo.

A daki Ammi na ganin su ta mike ta rungumo Maimoon jikinta. Itama hawaye ta ke yi tana tuna lokacin da ta tafi ta bar Sayfullah ya na da shekara uku yau ya girma ya yi aure.

Auren Sayfullah da Maimoon wata dama ce Allah Ya bata ta gyara tsakaninta da danta. Ba zata yi wasa da damarta ba. Ta yi kuskure babba kullum tana nadamar abunda ta yi. Ta bari fushi da kuma tsoro sun rabata da danta. Amma in sha Allah komai zai daidaita.

Zaunar da Maimoon ta yi a gefenta. "Allah Ya yi muku albarka diyata." Abun hannu guda shida na gwal ta fiddo ta saka ma Maimoon a hannu.

Daga nan aka kaita wurin Ummi. Daga Ummi har Maimoon an rasa wanda za'a ba hakuri a cikin su duk kuka su ke yi.

Farin ciki wurin Ummi ba'a magana. Addu'ar da ta dade ta na yi yau Allah Ya karba sai kuma fatan Allah Ya ba su zaman lafiya mai daurewa. Duk cikin yaranta Maimoon ta fi kowa shiga damuwa, tana fata Allah ya dawwamar da ita cikin farin ciki a gidan aurenta.

Da kyar aka samu su ka saisaita kan su. Sai dai Ummi da ta bude baki za ta yi magana sai kuka.

Duk mutanen dakin sun tausaya musu ana kuma jinjina irin son da ke tsakin su.

Kawayen amarya su ka rakata daki ta chanza kaya aka kara gyara mata fuska saboda idanun nan sun kara girma saboda kuka.

"Ki adana hawayen sai an tashi tafiya da ke," Habiba ta tsokaneta. "Sai wani kuka kike wa mutane, to ki zauna a gida an fasa auren."

Maimoon ta maka mata harara da sauran hawaye a idanun aiko Habiba ta fashe da dariya.

"Rabu da ita Maimu," Safara'u ta ce. "Lokacinta na nan zuwa."

Habiba ta yi shakiyin murmushi. "Ni ai bazan yi kuka ba, in kuka bata mun lokaci ma sai dai kawai ku ji na kai kaina."

Kowa ya sa dariya aminan na burge su.

Cikin atamfa amarya Maimoon ta shirya dinkin riga da sket da ya zauna das a jikinta.

"Kin yi kyau Adda Maimoon," Kydah ta ce da murmushi a fuskarta.

"Yau ni ce addar Ya Kydah."

Dariya ta yi. "Ahh ai kin samu (promotion), kin zama matar Yaya dole a kira ki Adda."

Tun a daki aka fara daukan hoto kafin a fita waje. Maimoon har saida ta gaji da murmushi ta koma tana yaken dole. Ta gaji, daga a ja tan sai a ja ta chan.

A falon Ammi ma sun sha hotuna sosai. 'Yan uwan Ammi kwan su da kwarkwartan su sunzo bikin babban dan su Sayfullah.

"Allah Ya baku zaman lafiya. Allah kuma ya baki ikon shawo kan Sayfullah ya daina fushi da Indo." Hajja Mero—mahaifiyar Ammi, ce ta yi wannan maganan.

Maimoon na zaune kusa da ita dan haka ita kadai ta ji abunda Hajja ta ce.

"Na san kin san ya halin da su ya ke. Ina rokon ki da ki yi iya bakin kokarin ki wurin gyara tsakanin su, abunda dukkan mu muka kasa na tsawon shekaru."

"In sha Allah Hajja." Maimoon ta furta a sanyaye.

"Hajja kuskus din me ku ke yi da amaryar ki?" Wata abokiyar wasan (cousin) Ammi ta tambaya tana murmushi.

"Yanda zamu kwakwale idon maigidan mu ke shawara."

Duka aka sa dariya. Maganan Hajja bai daina yawo a kan Maimoon ba har ta bar sashen.

Oh Allah! Ya Allah Ka bani iko!

Bayan azahar da misalin karfe biyu dangin ango a karkashin jagorancin Hajiya Fatima Mami su ka zo tafiya da amarya. Kaduna za'a kaita gidan Alhaji Abdur-Rahman inda za'ayi budan kai daga nan kuma amarya da ango za su dawo gidan su su kadai.

Kukan da Maimoon ta yi dazu farilla ne akan wanda ta ke yi yanzu. Duk an tausaya mata. Wayyo aure yakin mata.

Da aka kaita wurin iyayenta maza Baffa kasa cewa komai ya yi saboda hawaye da suka taru a idonsa. Baba Nasir da Baba Abdullahi ne su ka yi mata nasiha mai ratsa jiki.

An kaita wurin Jaddati itama ta yi nata nasihan. Mimi da Sadiya na ta kokarin danne kukan su amma da suka ga dagaske Addar ta su tafiya za ta yi sai su ka sa kuka suma.

Da kyar aka banbare su daga jikinta. Habiba, Safara'u da Adda Salma za su bi su sai Ahlaam. Kawarta Rukayya nada wani bikin tunda safe ta tafi.

Har su ka isa (train station) bata daina kuka ba. "Ki yi hakuri Maimunatu kin ji." Mami ta ce.

Bayan tafiyan tawagar 'yan kai amarya tawagar ango da abokansa su ka iso yi wa iyayen amarya godiya. Wurin Jaddati aka fara yi musu iso.

"Yanzu aka tafi da amaryar ta ka tana ta yi wa mutane kuka."

Sayf ya yi murmushi. Jaddati na tuna mai da Ammah.

Sameer ne dan jagora. Daga nan su ka isa da su wurin Ummi. Ummi fullancin ya motsa tana jin kunya suruki. Maman Anwara ce ta rika amsa gaisuwan su.

Sayfullah ya ji gabansa ya fadi da suka iso bangaren Ammi. Tun a farfajiyar gidan ya hadu da wasu daga cikin danginta. Yawanci duk bai san su sai sun yi gaba Sameer ke rada mai ya dangantakan su ya ke.

Tuni Sameer ya sanar da mahaifiyarsu sun kusa zuwa ta saka an share falon an goge sannan an kuma kunnan turaren wuta.

A gaban kujerar da Ammi ke zaune duka suka samu wuri suka zauna. Ammi ta miko mai hannu a hankali ya daura hannun shi akan nata ta damke shi sosai tana murmushi.

"Ammi gyara ayi muku hoto." Sameer ya ce yana ciro wayarsa daga aljihu.

"To," ta amsa murmushin fuskarta na fadada. Hannunta na cikin na Sayf ya tayata mikewa tsaye. Sai ta zama 'yar karama kusa da shi.

"Sameer kawo kaima ka shiga," Cewar Habib.

Su biyu suka saka Ammi a tsakiya. Ganin haka Hajja Mero ta aika a kira 'yan matan. Allah Ya so basu yi nisa ba ,Kydah da Waahidah su ka shigo falon da sauri. Kydah ta tsaya gefen Sayf, Waahidah kuma gefen Sameer.

Kowa wurin ya lura da yanda Ammi ke kokarin shanye hawayenta. Hajja Mero kuwa saida su ka zubo ganin tsantar farin cikin da ke fuskar 'yar ta. Yau gata tsaye da duka 'ya'yanta, abunda ta dade tana fata.

Har aka gama hoton hannun Ammi na cikin na Sayf.

















Mrs Sayfullah😻!





~Maymunatu Bukar💕

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro