Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

Chapter 25



Da sauri aneesa ta dafe kumatunta cikin mamaki take kallon khushi muryarta na rawa tace da gaske marina kikayi khushi?wani takaicine ya sake kamata cikin fushi tace may be,bata jira me anee zata sake fada ba ta dauki travelling bag dinta ta nufi hanyar fita,da sauri aneesa ta sha gabanta cikin kuka tace i am so sorry khushi don Allah karki tafi ki barni wlhy rayuwata ta saba dake bazan iya rayuwa babu keba please ta karasa maganar tana zubewa a kasa bayan ta hade hannunta guri daya,tsaki khushi tayi cikin zafin nama tace kin dade kina yaudarata aneesa wannan karon bazaki sake yaudarataba gara ma ki dena min magiya saboda bazan sake yarda dakeba,bazan sake daukan maganarkiba saboda tunda kike fadamin magana baki taba fadamin magana mai amfaniba sai wacce zan shiga halaka,cikin kuka aneesa ta mike tsaye tace i know but just give me a last chance please,ki bani dama ta karshe nayi miki alkawarin bazan sake fada miki maganar da zai saki kuka ba i promise,shiru khushi tayi tana kallonta ba tare da ta yarda da maganar da take fada mata ba ta sake juyawa zata fita,rike mata hannu tayi cikin magiya tace please khushi just give me a chance ki bani damar karshe don Allah....gyara tsayuwarta tayi sannan tace well zan tsaya in saurari maganarki amma kisani yanzu ina cikin hankali na saboda haka magana me kyau hankali na zai iya dauka kawai,ajiyar zuciya aneesa tayi tace hakane but at least ya kamata ki ajiye jakar nan dake hannunki kici abinci ko kadan ne,shiru khushi tayi bayan ta ajiye jakar dake hannunta sannan ta karasa gaban dinning table din don tana jin yunwa sosai ita kanta rabonta da cin abinci tun jiya,ganin khushi ta zauna yasa aneesa yin wani murmushin mugunta a hankali tace zaki gane kuskurenki khushi,bayan ta zauna taci abinci sosai tasha lemon da anee ta zuba mata a cup ji tayi gaba daya jikinta yayi weak,da kyar ta kwanta akan gadon ba tare data iya cire takalmin da yake kafafuwanta ba,ganin halin da khushi ta fara shiga yasa aneesa yin dariyar mugunta a hankali tace khushi my love.............

"Sai faman zagaye yakeyi a dakin amma ya kasa samun mafita,mum ce ta shigo dakin jikinta sanyaye tace Alhaji ya kamata ace ka samu guri ka zauna tun dazu kake abu daya a tsaye baka tunanin kaje ka fadi hawan jininka ya tashi?furzar da zazzafar iska yayi daga bakinsa yace ya kikeso inyine?wannan wacce irin masiface haka na rasa yarinyata guda daya wacce nafi kowa so a duniya sannan yanzu da wanne bakin zanyiwa mukhtar bayani na fada masa cewar aneesa ta gudu da meenal?kwata kwata number din aneesa baya shiga bansan wanne hali take cikiba na farin cikine ko na bakin ciki bansaniba taci abinci ko bataci abinciba taya kike tunanin hankalina zai iya kwanciya?haba Alhaji karka zama me son kanka dayawa mana itama meenal fa matsayin yarka take amma naga kamar baka damu da itaba mum ta fadi maganar cikin damuwa,da sauri alhaji ya dakatar da mum cikin fushi yace shut up!banason zancen banza da wofi sau nawa zan fada miki karki sake kwatanta soyayyar aneesa da ta kowa,shiru mum tayi ganin yanda Alhaji ya fusata kamar ze kai mata duka cikin sanyin jiki tace kayi hakuri nima ba wai nace hakaba don ranka ya baci yanzu dai addu'a zamuci gaba dayi kawai Allah ya bayyanasu kuma Allah ya fitar damu cikin wannan masifar da muke ciki.....cikin fushi yace amin sannan ya fice daga dakin mum ta bishi da kallo tana girgiza kai cike da damuwa ita kanta tasan aneesa ce bata da gaskiya amma soyayya ta rufewa alhaji ido ya kasa ganin lefinta

"A tsorace khushi ta farka daga nannauyan baccin da takeyi idonta ya sauka akan agogon dake dakin karfe 6 na yamma,jin yanayin jikinta yasata saurin kallon jikinta cikin tsoro ta bude blanket din dake jikinta ganinta naked ya sata runtse idonta sannan ta kalli aneesa itama haka take,cikin tsananin tashin hankali ta fasa ihu,a firgice aneesa ta bude idonta ganin yanda khushi ke ihu yasa aneesa rufe mata baki,ture hannunta tayi ta dauki towel ta shiga Bathroom,da kyar tayi wankan jin yanda kanta ke mugun sarawa kamar ze fashe...muryar anee sanyaye tace khushi,da sauri ta dakatar da ita zuciyarta na zafi kamar zata fito tace don't you dare call my name again abinda kadai nakeso ki sani shine i hate you and i will never trust you again ta karasa magana tana kuka,wannan karon jikin aneesa yayi sanyi sosai a hankali tears suka zubo daga idonta tana shirin yin magana khushi ta dakatar da ita sannan tayi wani murmushi me cike da takaici tace don't worry just save your words i dont want to listen anything from you,wayarta ta dauka tasa a jaka sannan ta janyo travelling bag dinta ta fita daga dakin ba tare da tasan inda zataje ba,har ta karasa fita daga dakin aneesa na tsaye kamar matacciya cikin tashin hankali,a farfajiyar hotel din ta tsaya cak hawaye ya fara wanke mata fuska,wannan wanne irin rayuwane?tabbas duk wanda ya bar gida toh gida ya barshi sannan bariki ba riba sai faduwa kasa warwas lol only few can relate,gaba daya ta rasa inda zataje wannan wacce irin masiface ta sameta a kasar daba ta iyayentaba ita yanzu ina zataje?duk irin horn din da ake mata besa tajiba har sai da motar tazo ta bigeta ta fadi kasa warwas wannan shi ake kira bariki a U.S.A ba riba lol...tuni mutane suka cika gurin da abin ya faru ambulance tazo ta dauketa aka wuce da ita asibiti,ganin yanda hayaniya ke tashi yasa aneesa fitowa don tambayar meyake faruwa?sedai bata samu damar ganin komaiba don tuni aka wuce da khushi asibiti karasawa tayi gurin wani bature da yake tsaye bayan ta mika masa hannu sunyi shaking hands take tambayarsa me yake faruwa,anan ne yake fada mata abinda ya faru cikin rudewa ta tashin hankali ta shiga taxi ta fada mishi asibitin da ze kaita duk da itama bata saniba amma ta haddace sunan asibitin da aka fada mata,bayan ta biya me taxi din kudinsa ta karasa shiga asibitin da gudu sedai duk yanda taso ba,a barta ta shiga dakin da khushi take ba saboda binciken da manyan likitoci keyi akanta,sai da aka dauki 3 hours ana abu daya kafin a samo kan khushi duk da haka ba,a bari kowa ya shiga inda khushi takeba,sai karfe 2 na dare tukunna khushi ta farka kallon dakin kawai takeyi,sai a lokacin aneesa ta samu damar shiga dakin ta zauna duk da ta fuskanci wani yanayi a kallon da khushi keyi mata kamar bata taba ganintaba hatta sunanta data kira saidata dauki tsawon lokaci kafin ta waiwayo,bayan dr yazo da safe ne yake fadawa aneesa cewar khushi ta samu buguwa sosai a kwakwalwarta tayi loosing memory dinta,cikin tsoro da tashin hankali ta mike kamar zararriya tana kallon Dr dinda yakeyi mata bayani loosing memory?what are you saying?bata jira ya sake cewa komaiba ta koma dakin cikin rikicewa take jijjiga khushi amma kallon bakuwar fuska takeyi mata cike da tuhuma......

"Sai da suka kwana 2 a asibiti ganin babu alamar lafiya yasa aneesa dole kiransu mum ta sanar dasu inda suke sannan da halin da suke ciki,cikin kwana 3 su dad suka sauka a U.S.A tare sukaci gaba da jinyar khushi bayan dad yayiwa su abba bayanin cewar sunje america ne gaba dayansu saboda siyayyar kayan auren khushi inda ya nemi alfarmar a kara musu sati 1,babban tashin hankalinsa shine loosing memory dinda khushi tayi wanda bata iya gane kowa a cikinsu hatta sunanta bata iya tunawa,sedai likitoci sunyi musu bayanin cewar zata iya dawowa hankalinta nan da kwanaki kadan,sai da aka dauki 5 days kafin a sallamesu daga asibitin bayan kwana 2 suka koma nigeria hakan yayi daidai da bikin khushi saura kwana 3.....bayan sun sauka daga jirgine suna kokarin shiga mota wasu yan sanda guda 2 suka sha gaban aneesa tare da nuna musu identity card dinsu,cikin mamaki su mum ke kallonsu inda daya daga cikin yan sandan yace you are under arrest sakamakon tuhumarki da akeyi da kokarin aikata kisan kai tare da lefin kidnapping,a zafafe dad ya kaiwa dan sandan mari sedai kafin hannunsa ya kai yayi saurin kaucewa yace ranka ya dade ba,a fada da hukuma ka adana duk wani hukunci da zaka yanke idan yarinyarka taje court,basu jira ya sake magana ba suka ja hannun aneesa suka shigar da ita mota suka tafi da ita

Thank you for reading my story!!!

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro