Chào các bạn! Vì nhiều lý do từ nay Truyen2U chính thức đổi tên là Truyen247.Pro. Mong các bạn tiếp tục ủng hộ truy cập tên miền mới này nhé! Mãi yêu... ♥

D'aya


============
Hasken rana ya disashe, yammaci ya shigo duniya, daidai lokacin da motar  jamil ta sauka daga kan hanya, ta kurda kan wata rakwababbiyar hanyar kauyen TSAUNIN ICCE da ruwa ya bata sosai. Gefe da gefen hanyar shukoki ne na gero da sauran ababen gona suke bada tallafin cushewar hanyar.
Mutum uku ne a cikin motar, direban dake gaba sai jamil da suhaima da suke zaune a baya. Fuskokin su suna cike da tsananin farin ciki, lokaci zuwa lokaci suna kallon junansu.
A hankali motar ta faka a kofar gidan MAI KAJI. Kauyawa dake gefe da gefe a cikin unguwar suka zurawa farar motar da cabalbali ya bata ta sosai. Da yawa daga yara kanana kaca kaca kamar almajirai sun rugo, wasu na shan rake wasu sun saki baki suna kallon bakin da MANI MAI KAJI yayi.
Kafin Jamil da Suhaima su gama fitowa daga cikin motar, tuni labarin isowar baqi daga birni ya karade cikin gidan malam manu mai kaji. Tani ta fito da gudu daga cikin gidan da daurin kirji tana rike da rariyar tankade, rabin zanin dake jikinta wanda tayi daurin kirji da shi ya karade da garin da take tankadawa.
Tayi kururuwa cike da jin dadi
“Laaaaaha’ila wallahi suhaima ce… suhai.. ce”
Suhaiman bata ji nauyin lalatattun kayan dake jikin Tani ba ta ruga da gudu suka rungume juna suna ihu da kururuwa, a nan suka bar jamil ba tare da ya bisu ba. Ya tsaya yana fama da kayan da yake so ya dauko daga cikin but din motar, direbansu yana kokarin taya shi. Yara suka fara ta su, daukar kayan da suka zo musu dasu, sannan suka shiga. Jamil yayi sallama da direban ya juya ya wuce ya bar jamil da yara suna ta ihu da kururuwa na al’adar kauye.
Suhaima ta fito daga cikin gidan a tsanake da darduma da buta
“Kayi hakuri… Tani ta dauke ni munje muna ta giasawa da mutane” yayi murmushi, akwai tsananin so da kulawa, shauki da bege a fuskarsa.
“My one” ya kirata da sunan da yake kiranta, tana matukar son sunan “Kin fito da wuri ne ai, kamata yayi ki tsaya ki tattauna kafin ki fito, wannan yana daga cikin uzirin da zuciyata tayi miki”
Tayi murmushi, taji dadi matuka da abinda ya sanar da ita, tasan halinsa, yana da matukar uziri, a karkashin dalilin jagorancin da soyayyarta suka yi masa kane kane a zuciya. Yana da kalamai masu dadi da yake sanar da ita, a lokacin damuwa da lokacin farin ciki. Ya iya komai da yasan zai gamsar da ita a lokacin bukatar hakan. Tana jin dadin kallon doguwar fuskarsa mai cike da siririn gashin ha6a da yake gyara shi ya kwanta a lallausar fatarsa.
“Dear!” Kalmar data yi amfani da ita, wadda tasan yana son sunan sosai. “baka rabo da bani soyayya, baka rabuwa da tabbatar min da ni ‘yar gat ace a zuciyar ka”
Ya matso kusa da ita, har numfashinta yana kokarin cin karo da nata. Ya dan durkuso kadan da yake ya fita tsawo. Ta lumshe idanu saboda wani abu a cikin idanunsa da take tsoro, wanda yake sanyaya jikinta taji kamar zata yi bacci.
“My one… you know I really love u ko?” ta gyada kai, bata cire idanun nata ba da suke a rufe. Yayi dariya a hankali da sautin da yasan tana matukar so. “bude idanun ki”
“Yaya kasan mutane fa suna kallon mu ko?”
“Ya kamata suma mu bar musu tarihin hoton mu a matsayin masoyan da suka zo ganin gida, na tabbata za a samu masu koyi da mu bayan tafiyar mu”
Ta zulle ta gefe tana dariya tayi cikin gida, ya bita da kallo yana dariya bayan ya dauki dardumar da ta ajiye masa kusa da butar da ta kawo masa yayi alwala.
**
SUHAIMA da JAMIL Haka suke, a ko’ina basa boye soyayyar su, masoya ne na hakika da suka yi suna a so da matukar kaunar junansu. Tarayyar su tana ba kowa sha’awa yadda duk wani mai goyon bayan dangin soyayya yake marmarin zama ya saurari labarinsu ko kuma ya kalle su. a hankali aurensu ya taso, yanzu haka saura sati uku aure, shine dalilin daya sa suka halarto kauyen su suhaima domin ya gaishe da iyayenta. Kuma su sawa shirin auren da ake albarka.
Wannan tafiya ta tara abubuwa da yawa a dalilinta. Ku bimu a hankali.
**
Bayan sun huta, sun ci abinci, sun natsu, yanzu gasu nan a gaban MALAM MANU MAI KAJI. Yana saurarensu, yana cike da kamala da dattijantaka. Malam manu yana daga cikin attajiran kauyen TSAUNIN ICCE. Shine yayan mahaifin suhaima, wanda yace dole sai anzo ana gaishe shi.
Malam manu ya saurare su. kuma ya shi musu albarka ya tabbatar da auren su yana kan hanya, kuma insha Allah za a yi da kwanciyar hankali.
Dare yayi, suhaima da jamil suka lallaba suka bi tani suna zagayawa gidajen ‘yan uwa domin gaishe su. a tsanake suna biye da ita, duk da suna tare da Tani amma basu bari Tani din ta hana su bayyanawa juna shaukin da suka saba idan suna tare ba. Yaci gaba da tsokanarta cike da soyayya. Tana biye shi itama ta tsokane shi.
Basu dawo ba sai cikin dare, duk da yammaci suka zo amma labarin wasu baki masoya sunzo gidan MALAM MANI MAI KAJI  a cikin zagaye da tsallaken kauyen.
***
Jamil yana zaune a cikin tsukukun dakin da aka ajiye shi, dakin a tsaftace yake, amma gadon na kara ne, baiji komai ba a jikinsa ko a ransa saboda ya tabbatar soyayya ce dalilin daya sa ya samu kansa a wannan gadon, a cikin dakin. Suhaima ta lallabo duk da kunya da kawaicin ta, bata ji zata iya barin jamil dinta shi kadai ba tare da ta zo sunyi hira cike da kaunar juna ba. Tazo ta same shi, yana zaune a cikin dakin, yana chatting. Ta dan Harare shi ta zauna a gefensa, yayi murmushi bai dauke kai daga kallon wayar ba, ta sa hannu ta janye wayar, suna kallon sa, yayi murmushi
“Rigimammiya me kike bukata?”
“Lokacin ka”
“Bakya tunanin za’a ce munyi rashin kunya, kin baro Tani kinzo wurin jamil ko?”
“ai mijina ne”
ya kalle ta ya fashe da dariya
“au! Ni mijin kine?”
taja da baya da sauri tana hararrsa yana dariya, yana nannade hannun riga
“Wallahi karka taba ni…” ya fashe da dariya sosai.. suna cikin dariya, suka ji dididif!! Alamun tafiya da guje guje a cikin gidan… da sauri a tsorace suhaima ta kalli jamil
“yaya!”
“ya aka yi?”
“baka ji karar guje guje ba?”
Kafin ya bata amsa, sun fado cikin dakin, wasu jibga jibgan samarin kauye guda hudu ne suka tsaya tsaye kikam a cikin tsukukun dakin, duk da dakin bashi da fadi sosai amma haka suka shigo cikin dakin suka tsaitsaya suna kallonsu. Kowanne katon kauye a hannunsa akwai icce ko adda. Kallo daya jamil yayi ya tsorata yana kallonsu.
“Wa kuke nema?”
“bashi ya kamata ka tambaya ba malam dan birni” daya daga cikin garadan kauyen ya bashi amsa, yana warin wata irin taba mai kama da warin konanniyar roba.
“su wanene ku dan Allah?” suhaima ta fada a tsorace. Daya daga cikin garadan kauyen ya matso kusa sosai. Ya yi murmushi, hakorinsa daya ya balle,  fuskarsa tafi kama da rago.
“Tun lokacin da kuka zo kauyen nan namu mai albarka muka ga kuna ta nunawa mutane rashin kunya, wai ku masoya ko?”
“Me yasa haka ya zama aibu?” ya bashi amsa duk da a tsorace yake.
“shine ai muka zo mu kwashi rabon mu…”
“ka fada musu abinda muke bukata ba wai ku tsaya kuna kwane kwane ba SHARU” wanda aka kira da sharu ya durkusa ya kalle su.
“munzo ne da zabi uku… ku bamu dukiyar duk da kuka zo da ita..”
“duk abinda muka zo dashi, mun raba a gidan nan.. kudin tafiya ma bamu da su sai direban mu ya dawo gobe”
“to na biyu… idan babu wannan, zamu kashe ka”
suhaima ta dago a tsorace, shima jamil ya firgita matuka, yaja da baya.. “kisa?!!”
“kwarai da gaske… bari ma kaga alama” kafin jamil ya motsa, sharu ya yanke shi a hannu yaji tsananin azabar sukar wukar ta ratsa har kwanyarsa. Suhaima zata yi kururuwa, ya yanke ta da mari FAU!! Tayi shiru ba shiri.
“me..me..menene na ukun to?”
saida sharu ya fashe da dariya sosai, sannan ya kalle su.
“Shine ina so na kwanta da wannan kyakkyawar…” “ka kwanta da ita kamar yaya?”
“in kashe shaawata… in amfana da dandanon yadda yar birni take da zaqi”
“haba bawan Allah…. Me yasa zaku zabi haka a wurin mu? Me muka muku haka a wannan yanayin daga zuwan mu…”
“zaki amince koko mu kashe shi..”
kafin jamil yayi motsi, daya daga cikin su ya zabga masa iccen dake hannunsa, tuni ya sume, suhaima tayi kururuwa. Data ga sharu ya zare wuka zai luma masa.
“Na yarda!!” kuka ya biyo bayan maganar da tayi, a karkashin zuciyar suhaima bata ga tayi laifi ba, ta tabbatar dalilin soyayya zata bada jikinta, dalilin soyayyar jamil zata sadaukar da BUDURCIN Ta, dalilin son su rayu dashi zata yarda wasu kattan banza su kwanta da ita, su keta mata abinda take marari da tarairaya ta kaiwa mijinta gidansa.
Ta runtse idanu. Tana ji hannun sharu, wanda kanta ta yiwa yawa yana keta rigar ta, ta runtse idanu kuka na so ya fito. A hankali hannusa ya kai bra dinta. Bai jira komai ba yaja rigar. Tare da kuka lokaci daya tare da fadawarsa kan jikinta.
*ME ZAI FARU?*

_Xinnee smart_

Bạn đang đọc truyện trên: Truyen247.Pro